Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 8 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

5️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

YAN UWA MASOYA ANNABI ALLAH YA KARAWA ANNABI DARAJA YABA MU IMANIN A MAI ANFANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , ,

DON SAMUN LITTAFI BA TARE DA DAUKAN HAKKI DA NAUYI A KANKI BA SAI KI TURA DARI UKU A BANK DINA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA TA WANAN LAYIN 08036959257 KO 09036

Tun bayan fitan Abban mu ban koma daki ba wankin dana tara na farayi muna kafin yan kitso su fara shigo min su hanani aikin komai.
Ina shanya kayan ne nake jiyo zagin da Asabe ke durawa wanda ba sosai nake jiyo su ba daga inda nake har na samu na gama ruwa na diba naje nayi wanka.
Ban kai ga karasawa aikai sallama ko ban leka ba nasan masi kitsonane suka fara shigowa lokacin .
Makwabciyar mu hassana ce da yaranta yan mata biyu da zan wa kitso suka shigo fitowa nayi na dauko tabarman da innan mu ta bani don yan kitso din na shifinda tare da gaida ita.
Dakin inna na shiga tana zaune tana gyaran sarkan kanwarmu daya katse nake fadin inna ko zan dora abinci ne kafin in zauna.
Jekiyi tsabgan gaban ki gunda ga mata sun fara shigowa barni in gama in dafa muna fate da guntun tsakin daya saura muna shekaran jiya.
Ko zai kaimu har dare tunda ba abinda zamu dafa da daren inna Allah zai bamu da yardan ubangiji tunda ga yan kitso nan sun fara shigo min yanzu sai a sayo ko taliyan hausa a dafa da daren.
To kije ku zauna kada matar mutane ta dade a zaune inna ta fada na juya na fita raina babu dadi a lokacin don a yanzu kan ina iya fahintar halin da mahaifiyar namu ke ciki na mijinta da sauran mutanen gidan mu din.
Daga kofan innan mu kadan nake zama muyi kitso don Asabe tace bata yarda ana sake masu gashin mata barkatai a gida ba kada azo a barbada masu tsiya a gida.
Ina kitson ina tunanen halin da innar namu take ciki na bakin cikin rayuwa duk saboda kasancewan mu mata a gareta don kila badon mun fito a yaya mata ba da bata fuskanci duk wanan nakin cikin haka ba.
Muryan lantanane ya dawo dani ga dogon tunanen dana lula ina rike da kan yar karamar yarinyar dana farawa kitson lokacin.
Wai har an zauna wanan bakar sana,an da babu karuwa a kullun a cika muna gida da yan gulma da sunan kitso nikan malam ya dawo ya tare min wurina don wanan abin ya isheni hakana.
Kai ke nan duk abinda kakeyi idon mace na kanka a zubama ido a fita dakai waje ana baradawa a cikin gari.
Dagani har matan da nakewa kitso ba wanda ya tanka a cikin mu don idan da sabo sun saba da wanan halin na habaici idan sun zo kitson don kiri kiri ake nuna min hassada ga yin kitson kuma.
Maimakon ta shiga dakin datayi niyar shiga da farko sai kuma ta juya ta koma lungun Asabe ta dade kafin ta fito.
Lokacin har na gamawa yaran duka biyu na farayiwa uwar saura kadan mu karasa kitson namu tana yan wake waken ta na hausa mai kama da habaici.
Naji matar da nakewa kitson tace uhumm wanan matar baban naki da jan magana take naga dai kullun nazo kitso gidan nan sai ta samu abindata fada a kanmu.
Ina jin dadin yadda baki kulata kike aikin gaban ki ba tare dakin damu da ita ba don irin su saboda bakin ciki suke haka don tayi sanadin da zata saka a hanaki kitson ga baki daya tunda sun san kina samu a nan.
Ba komai ai wata ran sai labari na fada mun gama ta dauko dari biyar sabuwa ta mika min na girgiza kai tare da fadin a, a wallahi ki ban dari ko dari da hamsin .
Haba Abu kullun na turo yara a kyauta kike min kitson nan ki karba baban sune ya bamu mu kawo maki da nake fada mai alherin da kikewa yaran shi kullun.
Dole na karbi kudin badon naso ba damun wanan kudin ya zama kamar buduwar hanyar alherina ranan don duk wa yanda sukazo kitso mun samu alheri sosai a wurin su.
Bansan yaya Asabe sukayi da mahaifin mu ba ya dai bani hakkuri kan in hakkura da karatun nan kawai a yanxu.
Ranan nayi kuka sosai kamar ba gobe tun innan mu na ban hakkuri har ta gaji ta kyaleni ta saka min ido.
Saratu ne abinka da dan uwa data dawo innan muke fada mata wuni nayi ina kuka a daki yau don Abba yace ba zancen komawa makaranta a wurina.
Tashi tayi ta sameni a dakin tana ban hakkuri tare da ban shawaran da muke ganin zai fitar dani daga kuncin da Asabe ds lantana ke shirin jefani s ciki.
Fitowa nayi don taya innan aiki gitkin dare haka ma su sararu da sauran yan uwan mu suna debo ruwa daga rijiyan uguwar mu suna cika duk kayan dake gidan na ruwa.
Har sun kusa cika na kofan lantana don sheri kawai lantana tace wai habiba ta saka hannu a ruwan don haka bata so sai dai su zubar su debo mata wani.
Wanan ya kawo rikici a gidan mu sosai ranan don har inna takai ga tanka masu Abba kuma ya dawo ya hau innan mu da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Wai inna ke goya muna baya muna iya shegen da mukaga dama a gidan ai lantana ma kamar uwa take a gurin su tunda tana auren shi.
Saratu dai taki komawa diban ruwa kuma ta hana yan uwa zuwa su debo suka kada guga a riya karshe dai ruwan da ba,a deboba ke nan har Abba ya dawo hake wanan fadan .
Kwala min kira yayi wai na kwashe ruwan randan innan mu guda in zubawa lantana a nata randan in yaso mu mu zauna ba ruwan tunda saratu ta zama abinda ta zama a yanzu duk gaba daya zai hadamu yai muna aure lokaci guda tunda ba finta nayi da wani girma ba.
Inna kan bata da aiki sai kuka don hakane kowa ke kokarin takata yadda yaso a gidan don rashin maganan da bata yi idan suna mata abinda sukaga dama, mu a namu ganin ke nan.

Hjy iyami abin duniya y isheta ga matsin da gwaunati da yan siyasa ke mata dole ta zauna da yaranta da yan uwanta kan maganan.
Inda suka bata shawaran karban mukamin don taimakawa rayuwan tallakawa da sauran al,umman nahiyar su din.
Haka yasa ta shedawa Alh Aliyu zaki kubau amincewan ta wanda ba karamin farin ciki yayi da jin hakan ba daga bakinta ,.
Duk da yana hangen da wuya su iya tafiya a yadda suke so da ita don ra,ayin daya hango a tare da matar duk da ba laifi ko yaya ne ai wayau maza yafi na mata ya fada.
Tawaga guda sukayo zuwa gidan sun dade suna tataunawa da ita kafin suyi mata godiya su tafi.
Hakan yasa taji duk ta gaji ga ranan don yan aikin ta kawai bazasu iya mata abinda take so ba daidai a hakane safiya suka zo gidan suka same ta cikin gajiya.
Bayan sun gaisane tare da mata murnan abin arzikin dake shirin faruwa da ita take fadin anya safiya zan iya wanan abin yanzu.
Yau kawai duk nabi na gaji dan dawainiyar dana wuni inayi da jama,a agidan nan .
Shiyasa nake son a samo min yarinya yar maidaidaciya da take da rikon Amana in zauna da ita don wa yan nan kinga su ba zama sukeyi ba ko ba school sai sun kirkuro fita sam basu zama a tare dani.
Na rasa inda zan samu irin yarinyar da nake bukata na kusa wace zata dinga min hidima ko yaushe.
Dan shiru safiya tayi kafin tace za a duba a gani indaya dace sai a samo maki yarinyar kamar yadda kika bukata.
Zanje kauye in duba maki mai dama mu gani idan zata iya idan kuma ta gaza sai a mayar da ita a sake duba wata.
Dakin mun hakan dana gode kuwa safiya shiyasa nake kara jin dadin ki wallahi na dade ina tunanen ta ina zan fara duba yarinyar data dace yadda nake so nan gari.
Da wanan maganan suka rabu ranan inda safiyan ta koma gida da tunanen inda zata duba yarinyar data dace takawowa hjy a yanzu gashi tayi alkawarin hakan gare.
Kafin gari ya waye ta yanke shawara a ranta zata duba ta gefen mahaifiyarsu ta gani idan hakan zai samu garesu.
Don koma meye zata iyayiwa hjy iyami indai zata iya baifi karfinta ba don ko meye hjy ta cancin hakan garesu .
Don ta nuna a duniya su yan uwan mijintane a yanzu don ko wani wuri zata tafi na alfarma suna daga cikin masu mata rakiya.
Wanan abin yana ba mutane da dama haushi har suka fara fadin asiri sukai mata suka shiga zuciyan hjyn a lokaci guda.
Daga hjy harsu suna jin ire iren wanan magana saidai ba abin mamaki bane hakan da mutane suke fadi don yanzu mutane basu dogara ga Allah sun manta da ba duga aka zama daya ba.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.