Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 65 of 139
Kujeran da nake zaune sama anty fadila ta kala kafin tace dani waini na tambaye ki mana zainab wai tunda maigidan nan ya dawo ya nemi ki a shimfidan shi kuwa ?
Kai na dago da sauri ina kallon ta don ban fahinci inda zancen nata ya dosa ba yasa nace a cikkn mamaki shifida kuma anty ?
Kamar ya shimgidan shi don ban fahinci mekike nufi ba wallahi kayya ta fada cikin daure fuska a gareni.
Tana fadin waike zainab wace irin yarinya ce haka mara wayau da hankali ke an fada maki haka zaman aure yake wai ?
Iyakar mace taci tasha ta saka mai kyau ajikinta ta kwanta shine zaman aure tsakanin mata da miji kawai a rayuwan su.
Idan shi bai neme ki ba bana fada maki hanyar da zaki bi ki ja mijin ki a jikin ki ba zainab kada fa tunanen da nakeyi ya zamo gaskiya a gareku gidan nan.
Me kike tunane anty na tambaya cikin marairaice murya don a zatona wani abin kuma ta hango a tare dani sai naji tace dani barshi kawai hasashen hakan kawai nakeyi akan ku bai zama lalai haka din bane.
Amma dai gaskiya zuciyana ya fara zargin wani abu a gidan nan yanzu, saidai abinda nake so dake shine koda shi bai nemeki ba zainab kiyi hakkuri ki daure ki kai kanki a gare shi mugani .
Da sauri nace ban fahince ki bafa anty ina mai kallon fuskanta don karin bayani a gareni ki dai gwada abinda na fada maki din ta fada tana mikewa daga wurin da take zaune din zuwa kitchen din gidan.
Nan ta barni zaune ina tunanen maganan ta ta yaya zan kai kaina da kaina wurin ya jafar din yadda take nufi din.
Sam hakan ba zai taba yuyuwa ba kenan nidin fitsarariya kenan take nufi ko ms sam hakan ba zai yuyu dani ba wallahi sai dai duk abinda zai faru ya faru na fada a raina ina masifa da ita cikin zuciyana.
Ni a wurins tun daga ranan da nashigo gidan shi har rana mai kama data yau nan taba tunanen wanan abinda take nufi ba a yanzu a tsakanina da yaya jafar din don haka sai maganan nata baiyi tasiri ba a zuciyana ko kadan.
Itama daga wanan ranan bata kara yimin irin wanan maganan ba ta kawo ido kawai ta saka min naci gaba da yan harkokina na yau da kullun duk da bawani abu bane illa zaman falo saiko dan fita haraban gidan da yamma wani lokaci musha iska a waje shine kawai abinda nakeyi a gidan.
Don shi kanshi ya jafar din bayama zama a gida ko garin kwana biyu zakaji baya kasan ya dan fita zuwa wano kasa na kwana biyu kafin ya dawo.
ZAINAB IDRIS mAKAWA
ZAINAB IDRIS MAKAWAZAINAB IDRIS MAKAAW
ZAINAB IDRIS MAKAWAA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5ï¸Â⃣4ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN,
KADA KI MATA DA LITTAFIN KUDINE KIBAN HAKKINA KO KI BIYA RANAN DA NADAMA BAIDA AMFANI GA BAWA.
DON KIRA ZAKI KIRA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 08036959257 KO TURA KUDI BAKIN ZAKI TURA GA WANAN ACCOUNT DIN KAMAR HAKA 2254380105 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA AMIN, , ,
Shi hakki gaskiyane yar uwa zaki ban a ranan da nadaman hakan baida amfani a garemu baki daya don haka karatun wanan novel bai zama dole a gareki ba yar uwa ki barshi shine sauki a gareki da zaki gane gaskiyan hakan a gareki da fatan masu imani zasu fahince ni.
Ya mamud yana zaune sai faman tunanen zancen shi da dan uwanshi yake a zuciyan shi tun ranan da sukai wanan maganan ya kasa sukuni a zuciyar shi.
Don ya rasa dalilin dan uwan nasa na fadan wanan maganan haka dole akwai wani dalili nasa da yake boye mai a zuciyar shi.
Don haka ya zama dole yasa ido kan kanin nasa har ya fahinci halinda da dan uwan nasa yake boye mai.
Ta yaya zai iya fahintar hakan bayan ba agari daya ko kasa daya suke rayuwa dashi ba a yanzu koma dai meye zai gane a sannun wanan alkawari yai wa zuciyat shi.
Don haka ya yanke shawaran da zuciyar shi zai fara tunkarana ko zai iya fahintar wani hali daga gurin dan uwan nasa saidai kaico ta yaya zai iya fahintar hakan dadin mace mai mutunci ke nan da ace matarshi mai kaunar yan uwanshine da ita zaiyi amfani har ya gano abinda yake so a wurina din.
Ko yanzun ma bai baci mai ba don zaiyi amfani da daman shi na namiji ya tursasata zuwa gidan don kawai su sada zumunci a garemu ta hakan har dan shakuwa zai shiga tsakanin mu ai.
Da dare suna zaune cikin ikon Allah itace ta dauko zancen jafar din da kanta take cewa dashi yanzu dai kanin ka shi ya fita zancen kowa a garin nan tunda yazo sau daya nasa shi a idona yana ganin bai neman komai a wurin kowa yanzu.
Shi jafar din ya dago yana tambayan ta da mamaki tare da fadin ina mamakin wanan halin naki Nuriya ?
Jafar naga ko yau muna tare dashi a gidan nan shekaran jiyama mun dade dashi muna hira a waje saida mami ta dawo muka bar wurin.
Kece dai bai samun fuskan da zai sake dake a wurin ki don hakane shima yanzu bai damu da ya shigo inda kike ba don yana jin rashin mutuncin da kikewa mahaifiyar shi ko yaushe.
Ni din ai duk wani laifi a kaina yake karewa dama a gidan nan fon hakane na kama kaina da kowa don na fahinci ba kauna akeyi ba.
Babu wanda bai kaunan ki gidan nan saidai halinkine basa kauna a yanzu don ba kowa zai zauna anaciwa uwarshi mutunci ba yana kallo a zauna lafiya da maishi.
Ko haka kokaga sunayi wa naki iyayyen su don kawai ina auren ki shine laifi a garsu baki daya ya kamata ki natsu ki gane hakan zai iya jawa yayan kima bakin jini a gurin su.
Bai damu da bacin ranta ba yaci gaba da fadin kin rasa gane cewa shi arziki na Allah ne ba fina jafar yayi ba daya bashi arziki ya barni duk da ina gaban shi .
Yanzu haka da taimakon jafar din nake samun ci gaba a rayuwana ko yaushe ba tare da mami tasan da hakan ba din shi ke tallsfa min ba tare dana roke shi ba.
Kai kaga zaka iya hakan don ni ban gaji komawa baya ba a gidan mu don haka kaje kaita jiran ya taimaka maka din.
Fita batun ta yayi yaci gaba da abinda yakeyi a falon ba tare daya kulata ba harta kare fadan ta ta shige daki ta barshi falo zaune.
Kai ya girgiza a cikin takaici yana fadin kina da matsala wallahi ni dai baki isa ki rabani da yan uwana ba wallahi ya fada cikin jan tsuki.
Kwana biyu dayin wanan maganan ta fito don zuwa unguwa ne motar ta haka kawai ya tsaya tayi tayarwa yaki tashi ranta ya gama baci sosai tana ciki tana kokarin ganin motar ta baci taga fitowan shi daga cikin gidan nasu yana waya.
Kaita kawar gefe kamar bata ganshi ba sai kokarin tayar da motanta takeyi kawai motar taki tashi kuma.
Har ya dan wuce ta ya nufi inda motocin shi suke ya dawo inda take ya tsaya tare da kashe wayan da yakeyi yana fadin madam lafiya kuwa ?
Wani nauyi da kunya ne ya kamata lokaci guda bai tsaya jiran me zata fada ba yace motar taki ta tashine ya tambaya yana kallon ta.
Wallahi lafiya na ajeta yanzu kuma na tayar taki tashi ta bashi amsa yace fito mu gani da hannu ya kira yaran shi mutum biyu sukazo wurin banda taju dake can ya kura masu ido yana bin Nuriya da kallon tsana.
Donshi ya ki jinin yaga wata mace ta rabi jafsr din a rayuwan shi koda kuwa yan uwan shine idan ba Aisha daya san kanwar shice ita har yakan dan sakar mata fuska wani lokaci.
Da sauri sukazo wurin ya nuna masu motar su duba matsalan ta a daidai lokacin Nuriya din ta koma gefe shi ta tsaya itama.
Ganin suna bata mai lokaci yaja tsuki yana fadin idan ta fara baki matsala a kawo maki wata ki daina hawan wanan din don kada ta tsaya maki wani wuri da babu kowa a kusa.
Sai taga ya shiga kiran layi ba tare da ya tsaya ba yake fadin a kawowa matar brother din shi mota yanzu mai lafiya na mata zata fita unguwane yanzu.
Bin bayan shi tayi da kallo tare da mamakin abinda taji yana fada a bakin shi tace a ranta lalai mijinta yayi gaskiya daya fada mata halin dan uwan nasa gashi tun ba,aje ko ina ba Allah ya nuna mata hakan .
Wanan dalilin yasa suka yanke shawara da mijin ta su sameshi har gidan shi suyi mai godiya wanda hakan ya zama dalilin zuwanta gidan namu a wani rana.
Na gaji da zaman daki da takura kaina yasa na fito falo na samu halimatu zaune tana kallo na zauna ina fadin halimatu wanan kallon yai maki yawa baki damu da duba littatafan ki ba na karatu.
Wanan film din nake son kallo yayan mu yanzu ai na fito dan na kalleshi inga yadda za a ci gaba ta fada hankalinta yana kan tv dake aiki.
Wuri na samu na zauna kafin in kalleta ince da ita amma dai kin san sanyin AC din nan yayi yawa halimatu anya halimatu kin dauki rayuwa da sauki kuwa ?
Ina jiye maki ranan da zamu koma gida a gaban iyayyen mu ranan da zaman gidan nan ya kare muna dagani har ke don baki dauki duniya da sauki ba ke nake gani.
Da sauri ta dago kai ta kara kallona tana fadin gida kuma anty me zamuje yi gida har mu zauna kuma ?
Halimatu kanki daya kuwa na tambayeta a cikin bacin rai sosai don dai nasan yanzu halima ta dan san duniya tana da shekara goma ko sha daya ai wurin haihuwa.
Tundani inada shekara sha shidda da dan kai da haihuwa yanzu na sha bakwai nake nema in rufe a duniya saidai tashin mu da wayau mu ba iri daya bane da nasu yanzu.
Sallama akayi bakin kofan duk da garin ya hade da hadari ruwa na iya saukowa ko wani lokaci .
Bakon abune garemu muji sallaman bako a gida don haka gaba dayan mu hankalin mu ya koma ga kofan don ganin mai shigowa din.
Ya mamud ne tare da Nuriya da yaran su biyu ke tafe ban san lokacin dana mike tsaye ina sake fara,a a fuskana ba kafin in tuna da waye Nuriya a gurina na mayar da fara,a na dan daure fuska ba yabo ba fallasa garesu.
Sannuki da zuwa na samu kaina da fadi tare da dan matsawa a inda nake tsaye a cikin farin cikin ganin su a wanan lokacin.
Zainab kuna lafiya ya jafar ya fada a daidai lokacin daya karaso cikin falon gaba daya ya fada ya samu wuri ya kai zaune da gudu yaran suka shige min jiki don murnan ganina da sukayi kafin yarinyar tace anty kin barmu yanzu bamu da mai koya muna assignment a gida kullun sai aunty ta dokemu a school.
Kan yarinyar na shafo naji dan namijin na fadin ke ba mommy tace mu barce mata anty ba mu kirata da zainab .
Ba uwarba har uban yaji kunyar maganan sai naji yace kuce mata anty matar unclen j daga yau kunji ko ?
Kasa nakai gurfane a gefen kujeran daya zauna din ina fadin yaya ina wuni ya gida ya aiki dasu mami da anty Aisha ?
Ya amsa dan maganan shi a cikkn sauri sauri da lafiya kalau zainab ya kuke na komai dai lafiya ko ?
Na amsa kai kasa da lafiya kalau yaya na juya gurin matar nasa ina gaida ita ba tare dana mike ba sai bina takeyi da kallo ta amsa min da kyat tana wani shan kamshi a fuskan ta.
Ko jafar na gida ta fada a cikin wani yanayi na nuna gajiya a tare da ita tana bin ko ina na gidan da kallo da sai kamshin ke tashi wanan aikin anty fadilane hakan.
Kafin in bata amsa Anty fadilane a bayan mu take fadin au baki mukayi gidan ashe sannun ku da zuwa a cikin fara,an ta ta karaso inda muke a falon a daidai lokacin na mike daga gurfanen da nake din tana gaisawa dasu.
Don ita koda yaushe fuskanta a cikin fara,a yake irin mutanen nan ne da baka saurin gane fushinsu tare dasu.
Nuriya ta amsa tare da kara maimaita min tambayan ta da jafar nace yana gida wurin shi muka zo ta fada tana kawar da kai gefe daya daga kallon mu.
Bari matarsa ta duba maku shi don dazun nan naga shigan shi gida anty fadila ta fada tare da kallon inda nake tayi min nuni da ido.
Cikin sanyin gwiwa naja kafana da har lokacin ina rike da hannun yarinyar jikan mami da suke kira da husna zuwa part dinshi din.
Kwakwasa biyu nayi a kofan kafin naji an bude kamar dai kofan da remote yake amfanine don sai kaji an bude ka dade tsaye ba wanda zai bude ya fito kamar dai wance karon da nazo.
Don haka sai na murda na shiga da sallamana a bakina can na hangoshi yana kwance saman gadon shi da laptop dinshi a gaba ya daga kafa daya yana aiki.
Ga cup a gefen shi da wani ruwa mai ruwa zuma a cikin kofin da alama dai yana aiki yake shan juice din.
Kai ya dago yana kallon mu har na karaso bakin gadon ina fadin sannu da aiki yaya su ya jafar ne dama suka zo suna falo.
Yarinyar dake rike a hannuna ya tsurawa ido kafin yace Husna tare da daddyn ku kukazo ne yana mikawa ya yarinyar hannu tazo wurin shi.
Bin dakin nayi da kallo ko ina na dakin a gyare yake fes sai walkiya yakeyi don gyara ga komai na dakin farine tundaga kan gado wardrobe da mirrow zuwa labullayan dakin duk farare kalane.
Juyawa nayi dan fita daga dakin yake fadin ki tsaya ki hada min wanan takardun jin haka yasa na tsaya har saida ya sauka daga saman gadon na nufi gadon don tattara mai takardun nasa.
Ba wasu takardu bane masu yawa zube saman gadon don haka sai bai daukeni lokaci mai tsawo ba wurin hadawa na aje mai kusa da jakkan dana gani nasa saman gadon .
Gyara gadon karayi dan dan takuran dayayi don hawan saman gadon dayi a lokacin nafito tare da ja masa kofan dakin.
A zaune na samesu a falon yana hira dasu a cikin sakin fuska ga abin sha da motsa baki an cika masu gaba dashi wanda nasa hakan aikin anty fadilace .
Har lokacin Husna tana makale dashi ajikin shi yana dan mika mata biscuit tana ci a hankali haka yasa na gane yana da son yara ashe shima.
A daidai lokacin dana karaso ya mamud ke fadin kawai nazo na samu madam tana murna da motar daka bata .
Na dade ina gurin canza mata mota tun lokacin da motar ta fara bata matsala saidai hakan bai samu ba sai gashi ka rigani bayarwa ashe zaiyi godiya yace
Kai haba dai madam ai tafi nan garemu wanan yaran haka data haifa muna kyawawa haka dasu ai taci a biyata da abinda yafi wanan ma yanzu.
Ai, ashe dama dan yaran ka ka bani wanan kyautan to nagode Allah yanu muna naku yaran watarana kuma ta fada tare da dago ido tayi min wani kallo da bansan ma,anan shi ba.
Wanan kamar gobe ai ya mamud ya fada yana mika hannun shi cikin snacks din dake gaban su ajiye dakina na juya na nufa dan in duba abinda zan iya ba yaran a lokacin.
A cikin dakin na samu halimatu a kwance tana karasa kallon da takeyi a falon suka shigo gidan a lokacin ban tsaya ta kanta ba na bude wardrobe dina na fara bi da idanu don na rasa me zan basu a lokacin.
Idona ne ya sauka wurin sunkin sabulan kasan waje dake a wani gefe sai turaren da bab san ranan shafasu ba a jikina don ko yaushe cikin kawo min turare aka a gidan tun kan wani ya kare.
Suna debo na saka a leda nafito kitchen na nufa wurun kayan kwalaman da ake ajewa na zuba a ledan saida ledan ya cika na fito daidai lokacin da har anty Nuriya ta mike tsaye a lokaci suna shirin tafiya.
Da sauri na karaso ina fadin cikin yar murya karama har zaku tafi ke nan anty dan har yanzu ina da dan tsorin su da shakkun su a raina don haka bana iya sake jiki dasu.
Eh dama ba zama zamuyi ba don akwai hadari a garin saida muka fito mukaga hakan ta fada tana fara takawa don fara fita daga falon.
Da sauri na mikawa yaron namiji ledan dake hannu ina fadi karbi wanan ka rika maku nagode yaron ya fada don tun lokacin dana koya masu yin godiya a makaranta idan wani ya basu kyautan wani abu na koya masu yin godiya ga mutum.
Ya mamud ne ya tsaya yana fadin zainab mun gode mu zamu tafi sai a kara hakkuri a zauna lafiya da kowa da sanu zaki saba da bahagon halin wanan mijin naki ya dan karasa maganan sa a cikin barkwanci.
Nagode yaya na fada a cikin ladabi gareshi yaci gaba da fadin ina fada maki kullun zainab ki daukeni kamar dan uwan ki na jini har in jafar yayi maki wani abu zainab don Allah ki kirani ki fada min.
Har wurin motan su muka rakasu saida kyar Husna ta yarda ta shiga mota wai zata zauna a wurin uncle ita ina jin ya mamud yana lalashinta da tabari zai kawo ta sufita yawo tare da uncle da anty sai ta washe baki tana dariya dan yarda da hakan daya fadamata din.
Bayan tafiyan sune na sauke zuciya tare da juyawa don nakoma ciki tsaye yake ya dora hannayen shi duka biyu saman weist din shi.
Tare da kura min idanuwan shi a kaina sai hakan yasani na tsargu dashi dan irin idanuwan daya watso min din lokaci guda .
Na fara tafiya naji yana fadin da alama kina son ganin baki a gidan nan ko don naga kamar zuwan su ya sakaki nishadi yanzu haka ?
Tambayan nasa ya ban mamaki saidai babu hali bada amsa a gareshi don gargadin kowa a gareni shine nayi mai ladabi da biyayya a kullun.
Don hakane na kakaro murmushin dole a fuskana da ban tashi yiba na soma tafiya don na kagu na bar gurin a lokacin.
Saidai kuma zuwan su baida ma,ana gareki saboda kin nuna masu irin zaman da kikeyi dani a gidan nan .
Da kina da wayau da kin nuna masu nidin mijin kine ai ta hanyar zama a kusa dani ko kiyi dan wani abinda zai nuna mudin mata da mijine ai.
Da sauri na dago kai ina masa kallon ido da ido na dan lokaci kafin na mayar da kaina kasa na dukar da sauri dan ba zan juri mai irin wanan kallon ba.
Da fatan kin fahinci abinda nake nufi da hakan koda kuwa mamine ta shigo gidan nan ya zama dole ki nuna nidin mijine a gareki yanzu ina fatan kin fahinci mai nake nufi da hakan ?
Kai kawai na gyada mai ba don na gama fahintar mai yake nufi da hakan ba a lokacin sai washe garine nake fadawa fadila yadda mukayi dashi .
Nisawa tayi tare da kallona a cikin mamaki take fadin akwai magana ke nan zainab mijinki bai shirya amsan ki a matsayin mata a yanzu .
Na rasa me hakan da yakeyi yake nufi don yana da wata manufa ta daban ke nan akan ki koda ya aure ki.
Kallonta nayi cike da fargaba a tare dani tace kwarai burin ko wasu ma,aurata shine su raya kansu da madara ko zumar kauna .
Amma shi mijinki nasa daban ne akan auren ku zainab dole akwai inda ya dosa dake a rayuwan shi don babu zancen kankanta a tare dake yanzu.
Kedin kinkai matsayin da duk wata mace cikakkakiya ake tunanen takai kamar yadda yace hakan ba laifi mu kuma sai muyi amfani da wanan daman wurin jefa mashi kaunarki a zuciya mu gani bashi din ya fadi hakan ba bude kunnuwan ki ki saurareni da kyau yanzu.
Mutukar baki ko mamin naku sukazo gidan nan ke kuma sai kiyi amfani da naki daman na ya mace ki dinga shammatar shi dole shi har idan lafiyayin namiji yake dole ya fada tarkon da zamu haka masa din.
Amma fa zainab hakan ba zai samu ba sai idan kin kara jajircewa sosai kin kawar da wanan kunyan naki da kike dashi irin na matan hausawa.
Zaki iya hakan koba zaki iya ba don in sani kada in bata lokacina don naga kema kina da kafiya akan wani hali naki na daban.
A hankali na gyada mata kai tare da furtawa a hankali cikin kyarmar murya da zan iya anty insha Allahu.
Nan dai tayi ta koyar dani hanyoyi dabab daban da zan tunkari matsalan dake gabana din ina mata godiya wanda ni kaina nasan gaskiya ta fada min ga wanan bahagon auren da Allah ya kaddareni da yinsa a yanzu da kurciyana.
Ban yarda da shawaran fadila ba kadai don jajircewa nayi sosai ina raba dare wurin mika kukana ga ubangjji mahaliccina sai gashi ina ganin sauki ga al,amarin nawa cikin dan kankanin lokaci.
Eh dole ince hakan do kuwa yanzu ankai shi da kansa zai shigo har dakina mu gaisa da safe haka kuma idan zamu kwanta barci duk na fahinci hakan a yanzu.
Duk da dai ba wani sakin fuska amma zai shigo mu gaisa ya tambayeni idan banda wani matsala a tare dani ko kuma idan ya dawo wani lokaci ko dakinsa baya shiga zai shigo har dakina yayi min ya gida tare da tambayan badai matsala ko ?
Idan muna dashi zan fada mai ko idan muna son wani abu zan dan sake infada mai komai sai yin hakan da yakeyi ya dan jawo muna kusanci a tsakanin mu.
Inda nakan shiga part dinshi da safe in gaidashi kafin shi ya shigo nawa part din da sunan gaisawa dani.
Bangaren taju kuma yanzu ba kasafai nake ma ganin sa cikin gidan ba sai can ba a rasa ba zamu dan hadu dashi sama sama muke gaisawa dashi din ba tare da wani sakin fuska ba ga kowan mu.
Kwaliya kuma irin na daukan hankalin maza kamar yadda fadila tace na jajirce gutin yinsu iya gwargodon hali ina bakin kokarina saidai kallo daya zai min ya kawar da kanshi gareni.
Sai wanan abin kuma ya fara damuna a zuciyana mutum kamar dutse shi baya ko sanin na ina mai wani kwaliya a hakan.
Kamar yadda yace indinga nunawa udan baki sun shigo hakan na daure tun ina jin kunya har na fara daina kunyanshi ina nuna muna normal dashi ai a zaman mu .
Don a gaban baki mu har wasa da dab dariya zamuyi kamar ma,aurantan gaskiya ne ni da shi ai sai idan sun tafine mukoma kamar yadda muke baran baran.ws🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.