Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 53 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

4️⃣4️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

YAR UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO YAUSHE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMAN UBANGIJIN MU AMIN YA ALLAH, , , ,
YAR UWA KADA KI MANTA LITTAFIN NAN NA KUDI DON ALLAH KADA MU SHIGA HAKKIN JUNA DARI UKU NE KACAL ZAKI BADA , , ,

Kofa aka turo tare sa sallama a lokaci daya wanda hakan yasa ta mayar da hankalinta ga wanda ke shigowa dan karamin falon a lokacin wanda ba kowa ke zuwa falon ba sai lokaci lokacin don takardun aikin ta masu mahianci da take adanawa a falon nata.
Mami lafiya naga kira yafi a kirga a wayana ban san da shigansu ba sai yanzu na duba mami ta dago kai a cikin wani irin yanayi mai ban tausayi ta kalli dan farin nata dake tsaye daga kofa a cikin damuwa ga yadda ya samu uwar nasu alokacin.
Kara rikicewa yayi lokaci guda kai tsaye ya karasa shiga dan falon tare da samun wuri ya kai zaune a gefen ta.
Mami wani abu ne kuma ya faru ko kuma jikin ne don office din ki na fara zuwa yauma akace min baki samu fitowa ba.
A hankali takai hannu ta zare glass din dake idon ta yanayin da fararen kwayan idonta da suke ciki na bacin rai ya baiyana a sarari har dan na iya ganin yanayin nata.
Jikin shi yai sanyi sosai lokaci guda yasan ba karamin abune ke jefa mahaifiyar tasu ga tashin hankali irin haka ba ga sanin da yai mata na jajirttatan mace a duniya.
Dan gyara zama yayi ya fuskance ta sosai da kyau don jin me zata fada mai a lokacin kafin ta dago kai tace dashi.
Mamud for long ka san da Jafar yana shaye shaye dama ?
Maganan tazo mai a bazata saida yadan razana don yasan ta kwabewa kanin nasa ke nan yau tsakanin shi da mahaifiyar su din tunda har ta sanda hakan gareshi.
Mami yasha wan, , , , hannu ta sake daga mai tare da dago kai ta kalleshi tana fadin ai tambayan ka nayi kawai ka ban amsa in sani.
Ajiyan zuciya ya dam sauke kafin yace gaskiya mami ba zance na san lokacin ba saidai tun kan dai ya tafi Hong Kong nasan da yana dan taba abubuwa kadan ina kuma kokarin tsawata mai ko a lokacin.
Sheshekan kukan data sake ne a lokaci daya ya kara tayar mai da hankalin shi sosai har ya mike ya isa gareta da sauri yana fadin.
Haba mami kuka kuma at dis stage da jafar yake a kanshi aini ina ganin wanan bai kai abin kuka ba tukun illa a tsaye a fahinci waye jafar a yanzu ?
Da sauri ta dakatar da kukan da takeyi din don jin abinda dan nata ya sake fada mata kan dan nata da take gani shine hasken rayuwan da kowa nasu nan gaba.
Wanan dalilin yasa take kokari ganin ginashi a kasan nan tun tana raye don ko bayan ta ya kasance suna da bangon dafawa kamar jigon su.
Shine hikima da kokarin mami na nacewa da auren shi da yar gidan mamman bello mai ritaya tsoho wanda ke daya daga cikin dattijan kasan nan dake fada aji a arewa.
Sai dai shi dan baisan manufarta kan hakan ba duk da ya hango hasken a zancen ta tun farko saidai shi sam baida ra,ayin hakan a rayuwan shi.
Yasa ya kaucewa wanan hadin da mami din ke sonyi mai da ko wace yarinya da bashi yaji zai iya zama da itaba a rayuwan shi don kawai wani siri nasa na daban can da bai damu da kowama ya sani ba a yanzu .
Muddin dai din ya samu daidai da yadda yake son macen ta kasance a rayuwan shi nan din gaba.
Mamud me kake son fada min a yanzu mami ta fada a cikin wani sabon tashin hankali a fuskan ta kuma wanda yafi na farko hadewa.
Mami ba wani abu bane dubaga yadda jafar ke samun cigaba yanzu a kullun idan anyi duba ga yadda rayuwa yanzu ya koma ga mutane.
Mumunan faduwan gaba ya kara zowa mami din hankali tashe ta furta hakane mamud nayi babban sakaci da damana na uwa a gareku da bana bibiyan bayan al,amuran ku akoda yaushe.

Haka kawai daga kwancen yaji ranshi na raya mai yakira layin wayana a lokacin don jin yadda na samu gida da yan uwana.
Kiran farko har zai katse yaji an dauki wayan ana fadin bata nan tana waje muryan karamar yarinya da bata kai mace sosai ba ke fadi a wayana.
Ke wacece ke maganan ua fada yana dan murmushin da bai tashi yinshi a lokacin na sai yajo tace ni, nice halima kanwar ta.
Au halima ya fada kamar ya santa a fili dama , kina lafiya ?, ta amsa da lafita kalau , ina yayan naki ta tafi ya tambaya .
Bata fitaba tana nan tana gyarawa innan mu wurine yanzu aka gama fada da inna da lantana saboda wurin girji dan murmushi ya sauke don jin abinda yarinyar ta fada.
Kafin yace fada kuma tace eh kullun lantana sai taja innan mu fada tace a raba wuri yana sauraren ta a daidai lokacin yaji wani murya na salati ana fadin yanzu wayan yayan tamu kike jagula halima?
Ba jagula nake ba an kirata ne na daga ta fada daga a dan shagwabe amma ke din nan yana ji zasu kaure da fadan su da suka saba yi ko yaushe.
Samun kamshi yayi da rashin kashe wayan yana saurare duk abinda ke faruwa har dawowana dakin da mukai magana akan abindaya faru yana jin komai bai kashe ko ya damu da kudinshi da a Ke jayewa ba a lokacin.
Basu fada min komai ba tunda na dawo dakin sai da nayi shirin kwanciya barci ne waya ya dauki sabon ringiing a dan daburce na daga wayan, murya kasa kasa ina amsa mai sallaman shi .
Don nagane shi duk da ban tubuta mai komai a wurin sunan shi ba har yanzu muryan shice take fadin ke idan ba,a kiraki ba ba zaki taba kiran mutum ba ko ?
Ganin har innan mu na dakin zaune yasa na dan saci kallon inda take a dan kashe murya nake fadin kayi hakkuri na mantane ban kira ba.
What ya fada da dan karfi har saida na dan razana da hakan na samu da kyat cikin rashin damuwa na sake fadin na mantane bankira ba.
Ji nayi ya sake wani wawan tsuki a wayan tare da fadin ke kina da hankali kuwa ?
Sai kuma ba bata lokaci yaci gaba da fadi kai tsaye ba tare daya saurari mai zan fadaba wanda dai bai wuce kalman hakkuri ba gareshi a lokacin
Ke ki saurareni da kyau kiji may zan fada maki don gobe zamu fara deal din mu na abindana fada maki zai faru tsakanina dake na taimakon junan mu a tare.
Don haka goben nan akwai wanda zaizo garin ku da safe daga kaduna zasu diba fili a saya a ginawa mahaifiyar ki wurin da zata zauna tare dasu halimatu fada ya kare daga yau a zauna lafiya.
A cikin mamaki na dago kai na kalli inda inna take zaune tare da sauran yan dakin namu dake zaune a lokacin kafin in mayar da hankali a wurin wayan ina kallo a cikon mamakin ji abinda ya fada din.
A Ina ma yasan wata halima can na fada a raina muryan shi naji yana fadin akan karamin abu za a dinga batawa inna rai yadda naji tana fadi dazun.
A ina yaji wanan zancen na fada a fili ba tare da nasan zan furtan hakan ba yace wacce abin ya dama ta fada min tunda ke ba zaki kira ki fada min ba asan abinda za a kan wana case din.
Koda na dago kaina gaba daya dakin idanunsu a kaina yake lokacin suna sauraren meke faruwa duk da bajin maganan sukeyi ba a lokacin.
Har ya gama maganan shi na kashe wayan ina kallo da mamaki sa,adatuce ta fara fadin me yaji yayan mu ?
Zancen fadan inna da lantana na dazun yake min fada ban sanardashi ba sai ji yayi ke nan yasa wani ya samai ido a kaina a garin nan kome ?
Da hannu sa,adatu ta nuna min tsakiyan kan halima take zaune a kusa da ita tana lasan miya a kwanon data karasa cin abinci a lokacin.
Itace dazun ta dauki wayan ki da aka kiraki ta fada mai komai yaji inna takai mata magara daga inda take zaune tana fadin waya aike ki mai shegen bakin tsiya da yawan magana.
Inna tambayana yayi ina yayar mu nace tana waje wurin da lantana ke fada dake shine na fada mai komai daya faru inna ta karasa a cikin sanyin murya.
Yanzu me kikayi ke nan yarnan zaki jawa mutane zancen gori da zunden mu a cikin garin da gidan nan kaf yanzu idan wanan zancen yazo kunnen jama,a ai sai a saka mu a baki.
Da kyat na hade wani yawu mai daci da dumi daya taru min a baki tun barin wayan na kasa magana in furta komai sai binsu da kallo da nakeyi dakin duk lokacin da wani yai magana a cikin su.
Bayan dogon nazarin danayi na yan mintina da har ya hana inji karshe fadan inna da halima ashe har dukan ta tayi a wurin ban farga ba.
Ba komai na tuna ba sai abinda ya fada da bakin shi ki huta kowa naki ya huta ta karkashin ki ayi alfahari dake a cikin yan uwan ki wata rana idan kin daure zama dani yadda nake.
Indai hakane na zan gwada in tabbatar da hakan daya fada min din idan har gaskiya yake har cikin ranshi abinda ya fada din a lokacin.
To ya zama dole kodan farin cikin mahaifiyata da yan uwana in amince da tasa bukatan mutukar hakan ba zai sabawa addinina ba ko ya taba min mutuncina .
Duk da nasan yin hakan wani gangancine nake kokarin aikatawa a rayuwana a matsayina na ba yar kowaba a duniyan nan nasa na tarawa kaina babban ganganci a rayuwana.
Haka kawai na dauki waya da sauri na rubuta idan hakan zai zama farin cikin mahaifiyata da yan uwana a shirye nake da inyima biyayya idan hakan bai kauce wa addinin mu ba.
Ina gamawa na sake karantawa batare da nazarin komai ba na tura mai sakon kai tsaye ina mai runtse idanuwana a hankali.
Muryan inna ne ke fadin wani abin yace ta fada mai ne ko me yafaru ya furta hakan.
Ba komai bane inna na bata amsa don hankalinta ya dan kwanta ina kokarin kawar da damuwan dake fuskana a lokacin.
Ba zan so mu jefa ki a cikin wani halin rayuwa harda zaki takura ba saboda wanda daga baya za a dawo abin yazo ya damu mutane kuma.
A,a inna don Allah ki cire damuwa a ranki kan wanan zancen don shi haka rayuwan shi yake da taimakon na kasa dashi ko yaushe.
Allah ya kyauta inna ta fada tare da kaiwa halimatu wani sabon rankwashe akai ta sakr sake wani ihu mai karfi tana fadin inna bansan hakan zai maku zafi bane ai.
A daidai lokacin dana tura mai da sakon yana kokarin fita falon mami don ya dubata a daidai tsakiyan falon sakon yashigo mai a wayan shi.
Wani irin shu,umin murmushi ya sauke a fuskan shi wanda baisan lokacinda ya sakeshi a fili ba don saurin kamawa da tarkon shi danayi a lokaci guda.
Caraf idon shi suka sarke dana mami dake zaune ta hakince tana ba mai aikinta umurni a lokacin.
Ya karaso zuwa saman kujera ya zauna a kusa da ita ba tare data samu mai magana ba don ta lula acikin tunane halin da dan nata ya shiga ba tare da saninta ba.
Idan ko har akan wanan yar matsiyatan abu kamar wasa ga zance naso ya juye ya zama mata babban magana a rayuwa yanzu kuma.
Har yau kan ita mami a daure yake don ta rasa gano me yagano a jikin wanan yar har ya mace haka a cikin sonta .
Yarinyar da ba a bakin komai aka dauke ta ba don yar aikine ba wata mai galihu can ba ko asali har yake neman jefa kanshi ga halaka haka ?
Saidai maganan babban danta mamud ya kara jefata a cikin zargin dan nata a yanzu don tsoron ta Allah kada abinda dan uwan nasa ya fada ya kasance gaskiyane hakan .
Ita dai a iya sanin ta da dan nata tun yana karami komai zayi a duniya zaiyi shine a cikin hikima da fasaha irin na masu hazaka da kwakwalwa.
Sai gashi yanzu ta kasa gaskanta zarginta na canza halayen dan nata ga baki daya ga yadda suka san abinsu da farko.
Fuskan shi a wayan shi yana duba tun bayan zaman shi wurin hankalin shi ya koma kan wayan mami tana magana da mai aikin da bazaice ga fuskanta ba tunda yakai zaune a wurin.
Juyowa mami tayi tana masa duba irin na tuhuma lokaci guda don yadda ta ganshi din yazo ya zauna mata ba wani jin darr din ta ko kadan akan laifin da take ganin ya aikata dole yaji nauyin hakan a lokacin.
Jikin shine ya bashi a lokacin da ana kallon shi yasa ya dago kai dan jin hakan da yaji a jikishi.
Caraf idanuwan shi suka hade dana mami din lokaci guda sai yaji ya dan tsargu da hakan shima don irin kallon da uwar tasu take mai a lokacin don haka ya dukar da kanshi babu shirin haka saboda nauyin ta dayaji.
Jafar may ye matsalakane yane yanzu mami ta fada tana mayar da hankalinta gareshi baki daya don ji amsan da zai bata a lokacin.
Amma sai ta lura kuma har ya mayar da hankalin shi ga wayan ba tare da yasan tanayi ba a wurin da kai nake magana ta fada da da karfi tare da nuna bacin rai a fuskan ta.
Firgigit yayi tare da sake dagowa yana kallonta yana fadi mami ban jiki bane na dauka da wanan kike ai har yanzu ya dan fada a tsarge.
Jafar wai yake damun rayuwan kane a yanzu koka sake shan wani abinne kuma saboda wanan banzan yarinyar daka kwallafa rayuwan ka gareta don jaraba.
Nafa gaji da wanan kwanaye kwanayen da kakein a gidan nan aure dai ne nace bada yawun bakina ba sai kasan yadda zakayi da yar mutane tun yanzu.
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya dago kanshi da yake a sunkuye ya dubeta tare da sake wani guntun murmushi a fuskan shi yana fadin.
Mami kina ganin akwai wata wace har zata iya sauya min rayuwana a yadda nake har yaushe na hadu da wanan yarinyar taki da zata sakani wani abinda ba halina ba yanzu.
Ran mami ya baci ainun da abinda ya fada a ranta tace mamud yayi gaskiya al,amarin yaron nan yayi girma ban sanda hakan ba kenan.
Jafar yanzu duk yarda da amana dana baku ashe akwai wani rayuwa da zaka fada wanda ban san dashi ba a tare da kai har ka boye min kanayi. .

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.