Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 118 of 139

ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAN UWA MUSULMAI DA FATAN MUN WUNI LAFIYA ALLAH YASA AMIN .
UBANGIJI ALLAH YA KARAWA ANNABI DARAJA DA DAUKAKA A DUNIYA ALLAHUMA AMIN.

YAR UWA LITTAFIN KUDINE WANAN DON ALLAH KI BIYA KAFIN KI KARANTA DON GUDUN FADAWA HAKKIN WANI NAGODE ALLAH YA BAMU IKON KIYAYYEWA AMIN.

Na fatar da komai na jakkan hannuna ina nema brosh dina sabo gurin hakane na manta da kayan saman gado ciki har da wayana.
Wandatun zuwa kaduna gidan su Nafisa ban taba fitar dashi wani ya gani ba sai wanan ranan dana fitar din garin sauri in shiga bayi kuma na manta dasu saman gadon.
Nafisa ta shigo dakin dauke da abin karyawan data hada muna don yau umma ta tashi bata ji dadin jikin ta hawan jinin ta ya tashi mata.
Shine dalilin zuwan nafisa kitchen tunda safe ta shirya muna abin karyawa don yayanta dake zaune a yola can kauyen su tun bayan rasuwan mahaifin su da abubuwa suka sake ya koma can yana dan buga buga irin na tallaka yana samo masu abinda zasuci a gidan.
Ganin wayana saman gado ta dauka tana mamakin irin girman sa bayan ta gama dubawane ta ga dacewan ta saka min shi a caji.
Ta dauka ta saka bata gane kan wayan ba don haka ta kunna ta gani ko ya kawo ya dauki cajin a daidai wanan lokacin kuma kiran sa,adatu dake faman gwada layina a koda yaushe kiranta ya shigo a lokacin.
Ina ban daki naji kukan wayana ai a zabure na dago da sauri na watsa ruwa na fito daga ban dakin ina mamaki.
Itama Nafisan ta tsorata da hakan don bata taba zaton kira zai shigo min a wanan lokacin ba haka.
Kallon juna mukayi lokacin dana fito bayin da mamaki karara a fuskana a cikin daburcewa take fadin waina saka maki cajine kada ya dauke sai kuma ga kira ya shigo lokaci guda.
Ai da kin sani baki kunna ba da zaki saka min canjin na fada ina karasowa inda wayan ke ringing don ganin wanda ke kirana a lokacin.
Sunan Sa,adatu nagani a wayan naki dauka har kiran ya katse ina kokarin kashewa ne kira ya jafar ya shigo na kashe wayan.
Shikan a nasa bangaren kiran ya nuna mai a kaduna nake don haka ya sake wani irin murmushi a fuskan shi lokaci guda .
Saidai tambayan kanshi yayi kaduna ina nake zaune ke nan ya tambayi kan shi lokaci guda don a iya sanin sa bai taba jin nace ina da wasu a garin kaduna ba ai.
Nan gidan anty Sa,ansu ya fado mashi a rai don idan ba zai manta ba ai na taba fada mai itace ta kawoni gidan mami aiki daga Anchau.
Kai ina ya fada anya a sanin da yaiwa gwaggo sa, a zata iya ajeni a gidan ta ba tare data tuntubi gida ba.
Don shi bala,in ganin mutuncin anty sa, a yake gani ko yaushe don tun suna kanana ya fahinci hakan matar tana son su tsakani da Allah sabanin sauran yan uwan su da akan samu tsegumi a tsakanin su kullun.
Wani tunane yayi ya danna kiran ya mamud yake tambayan shi ko yana da numban gwaggo sa, asu dake kaduna.
Ya mamud yake fadin wallahi baida layin ta sai dai idan zai nema mashine ya turo mai yace hakan yayi kyau ya kashe waya don baison wani dogon magana a yanzu.
Ya mamud ya kira wani dan uwan su a kaduna shine ya turo masu layin gwaggo sa,a din a lokacin sai dai abinka da yan uwan zamani shi maishi yana tunanen wani alheri zasuyiwa anty sa,a din a lokacin.
Can gidan mu kuma ihu sa,adatu tayi tana fadi wallahi inna layin yayan mu ya shiga saidai bata dauka ba har ya katse.
Inna tace ta sake gwadawa amma wayan yana a kashe baya shiga kuma yanzu don dole suka aje wayan suna tunanen ina na shiga haka na boye ne.
Yayin da anty Fadila ita kuma ta tsure sosai ga abinda ya fada mata din ta kwana tana tunane tana fadin ashe mutanen nan sun san me nakeyi a gidan su amma basu taba nuna min hakan ba.
Ko wanan ne dalilin da yasa yanzu bana gane komai a wurin zainab din ga baki daya ta sauya min ba kamar da da take fada min komai ba.
Wai to ta yaya har haka ya farune bayi sakacin da suka fahinci ko ni eaye mai kuma nazo yi a gida a matsayin yar aiki yanzu ?
Ban nunaww Nafisa komai a fili sai dai a zuciyana gaskiya ban so hakan ba don sanin waye ya jafar game da computer da nayi zai iya tracing dina a haka har ya gano inda nake.
Ina zaune a dakin bayan fitan nafisa sai ga umma da bata jin dadi ta shigo dakin daganin yanayin ta kasan a cikin karfin hali ta kawo kanta dakin na nafisa.
Ina ganin ta na dan daga ina sannu umma ya karfin jikin ko zamu tafi asibitin ne dai na fada a cikin kulawa gareta.
Murmushi umna ta dan sake tana kawai zaune gefen gado inda nake muna mata sannu kafin tace dani ai ko haka nagode yar nan.
Yanzu yayan ku ya shigo min da magani masu kyau da tsada wai zainab ce ta bada kudi ya sayo min su na gode Allah ya karawa arziki albarka .
Nace amin a kasan makoshina take fadin ai na dade ban sha irin su ba don rashin kudi gashi yanzu har Allah ya taimakeni na samu na mike ciwon bai kaini kwance ba.
Nake fadin ayyah sannu umma Allah dai ya baki lafiya tace amin kamin dan shiru ya biyo dakin can ta dago kai tana fadin.
Zainab dama gurin ki nazo yanzu kawarki ta sameni a daki tana fada mi karanbanin da tayi maki ai.
Kallom inda nafisan take tsaye a cikin damuwa nayi kafin nace umma me kuma ta fada maki tayi min ina kallon Nafisa din ido cikim ido.
Nafisan ke fadin wallahi banji dadin hakan bane besty shiyasa naje na fadawa umma ta baki hakkuri.
Kai haba besty kika tayar da umma kan wanan maganan shiriritan tana fama da kanta haka don Allah ki daina hakan mana.
Bashi ba zainab wallahi Allah yaga niyata dama naso nace dake ki kira mahaifiyar ki don ta san kina nan wuri mu ko hankalita zai kwanta ga hakan.
Da sauri na dago kai na kalli gefen da umma din take zaune tace eh zainab mahaifiya ba wasa bace.
Yanzu Allah kadai yasan irin yadda take ji a ranta na rashin ganin ki din nan kwana biyu da ba,a yi ba ga kuma mahaifin ku nasan ba zai kyaleta ba kan hakan don su maza a kullun mune da laifi akan yayan mu ai.
Duk da bansan me ya hadaki da mijin ki ba zainab alama dai kuma ya nuna min krce da gaskiya don haka ki natsu kiyi tunanen irin halin da mahaifiyar ki da yan uwan ki zasu shiga na rashin sanin inda kike a yanzu.
Hawayene ya fara zuba min a idanuwana lokaci guda don jin me umma din ta fada nima kaina da wanan tunanen nake kwana nake tashi a kullun tunda na barsu din.
Nasan inna zata shiga wani hali kan hakan haka kuma Abba zai dauki laifi ya dorawa inna duka ita daya alhali bata san da wanan zancen ba.
Da kyar na iya budan bakina don hawayen dayai min yawa nace Umma idan ba haka nayi ba ba zasu daukan man mataki ga halinda nake ciki ba ko kadan umma.
Tace na sani zainab nasan halin maza sai su cutama su koma baya suna kyautatawa iyayyen ka ko wani na tare dakai na kut da kut don kawai su batar da laifin su gareshi.
Don haka ba tare da dogon bincike ba zainab kiyi hakkuri ki ban lamban mahaifiyar ki nida kaina zan kira i mata bayanin kina hannuna don haka ta kwwntar da hankalinta ta.
Jin hakan na dago kaina da idanuwa da suke tab da hawaye na kalli umma din mace kamila natsatsa ta kada min kai alaman inyi hakkuri don Allah in karbi tayin ta din nace shike nan umma.
Kallon inda wayan nawa nayi kafin in kai gareshi har nafisa ta matso tana daukan wayan ta miko min na karba layin umma din na nema na mikawa nafisa wayan don ba zan iya karanto mata ba a lokacin.
Kira daya sai gashi inna ta dauki wayan kamar tana jirace da kiran dama ta dauka da sallama umma ta karba kamar sun san juna dama sai bayan gama gausuwan ne umma ke fadin nasan dai baki san wace ke magana ba inna ta amsa da eh ko altine ce ta damau, ?
Umma tace lala ba ita bace bakuwace na kiraki ne a kan yarki dake hannu na a yanzu da sauri umma tace gunki take boyar Allah ?
Tace eh nan tazo wurina sanadiyar diyata da sukai karatu tare shekarun baya daya wuce na kirane don hankalinki ya kwanta tana nan tare damu zaune.
Cikin sanyin murya irin na inna take fadin hankali kan ya tashi matuka don kowa na ganin nasan inda take zaune boyewa kawai nayi.
Musanman mahaifin du da yake ganin da sanina ta bar gida nasan komai kan matakin data dauka din saboda Allah hjy za ace .
Yau shekaru shidda da yan kai da auren yarinyar nan haka take zaune a gidan mutumin nan ashe kamar photo ?
Ba wani abinda ya taba shiga tsakanin su na aure har wanan lokacin kokai nan da girman ka ai ba zaka yarda da hakan ba ko ?
Subbahanallahi innalillahibwa inna alaihin raji,un umma ke fadi a bakin ta tana fadin ai kinga kuwa bata fada muna komai ba wallahi tunda tazo garin nan nima ban matsa mata kan sai ta fada min ba din.
Jam ko a shari,ance kan ai ba aure matukar ba an gyara ba gaskiya don hakkurin diya mace a wanan kalilan ne duk da a zahiri mun fisu hakkurin hakan.
Nan dai inna ta koro mata da zancen komai kamar dama jira take ta samu wani wanda zata amayewa damuntane kan hakan.
Da gani kuma ranta abace yake matuka sun kwasa da Abban mu a kaina dama kuma hakan nake gudu na gudu daga gaban su don kaucewa fitina ashe ban fita ba.
Karshe dai umma ta mika min wayan don inna taji muryana ko zataji sanyi a ranta na karbi wayan a hannun umma muka fara gaisawa da inna din a sanyayye.
Tace in kwantar da hankalina tunda gidan mutunci nake yanzu kuma hankalinsu su ya kwanta tunda sun san inda nake ai.
Har zuwa lokacin da za,a zauna da mijina idan ya bada hujjan shi na dalilin hakan a tsakani mu don malam yace zasu zauna dashi .
Kamar inna na gani a lokacin na gyada kai ina fadin ni inna bana son a wani zauna kawai malam ya raba aure na dashi kwata kwata na tsane shi inna.
Da sauri umma ta karbi wayan tana fadin ki kyaleta don Allah zaki kwantar da hankali ki nuna kema har yanzu baki san inda takw ba .
Inna tayi mata godiya tana karawa suka kashe wayan umma ta kalloni tana fadin yar nan haka kikai fama a gidan wanan mutumin ?
Na dukar da kaina kasa take fadin dole dayan biyu ko kece kikai masa wani abu ko kuma baida lafiya a jikin sa idan bashi ba ta yaya namiji zai zauna da mace kamar ki yana kallonta haka.
A raina nace umma kudai baku san komai ba ke nan a daije ga hakan ga hujjan dana kawo maku din.
Gaba daya ya rikice da neman na don sunyi waya da anty sa,a da yaya mamud ya samo layinta ya kawo mai ya nuna ko mun iso wurin ta don munce zamu zo idan mun shigo kaduna ?
Take fadin ayyah ashe mun shigone wallahi bata ji ba ko ga wani cewa munzo nigeria ai suka dai gaisa ya kashe wayan bayan ya fahinci ba can nake ba.
Mamaki ya kara kamashi lokaci guda ya gyara zama ta hanyar mimike kafafun shi ya dora hannun shi saman goshin shi yana murza a hankali.
Ya mamud dake gefen shi zaune ne ke fadin bata je can ba ke nan ko ya bude idanuwan shi da sukai masa ja jajajir ya sauke ga dan uwan nasa yana fadin wai bata can .
Amma dai tabbas nasan tana cikin garin kaduna tunda wayana ya nuna min hakan nasan tana garin comfarm.
Jafar duk laifin kane tun farko har hakan ya faru ya mamud yana kallon dan uwan nasa tare da gyara zaman shi yaci gaba da fadin.
A iya sani da kai ban taba zaton wanan halaiyar a gareka ba sai gashi daga sama mun tsunceka a cikin wanan harkan why jafar why zaka zabi wanan mumunan akidar ?
Hummh ya fada a yadda yaken zaune bai cire hannun shi a saman goshin ba yadda yaken da farko sai can ya cire ya kalli dan uwan nasa da idanuwan shi da suka kada suka kara rinewa ya sauke kan mamud din.
Mamud nima bansan dalilin fadawa wanan harkan ba gaskiya na dai tashi na tsunci kaina a cikin sa dumu dumu nima ba zance ma ga dalilin hakan ba yanzu.
Nayi iya kokarina don kaucewa hakan sai dai Allah bai karba min ba har hakan yakai ga yanzu da kowa yake kokarin sani .
Don nasan dole zainab zata fadawa iyayayyen ta wanan maganan tunda yanzu rabuwa take son yi dani ta ko wani hanya ?
Kai sam zainab ba atayi hakan ba da zatati aida ta fada muna muna tun zuwan mu chaina Jamal daine ya fara fada muna hakan koshi sai da mami ta matsa mai ne ya fada min ni kadai ba tare da mami a wurin ba.
Jamal ke nan dan uwana ya gaji ya fada ma balle zainab da aure ne ya hadani da ita don me kake tunanen ba zata fadawa iyayyen ta halaiyana ba ita ?
Kai ya mamud din ya girgiza yace kai ai ka godewa Allah daya taimakeka ya hadaka da mace kamar zainab don da ace watace ko irin su Nuriya da tuni ta dade da tona min asiri duk da bamu kasan nan kuwa.
A wanan lokacin ya mamud ya farga da wani yanayi da dan uwan nasa ya fara shiga a lokacin don bai farga da wuri ba da hakan.
Sunan shi ya fara kira a hankali kafin wani tari ya fara sarkeshi yana dafe kirjin shi da yake jin yai masa nauyi da tauri lokaci daya.
Da sauri ya mamud din ya mike zuwa wurin jafar din tare da riko dan uwan nasa yana kiran sunan shi hankali tashe da kyat ya samu ya dago kai ya amsa mashi.
Tun yaushe ne baka da lafiya haka ya tambaye shi dan murmushi ya sake a fuskan shi na karfin hali kafin ya kalli mamud din yana fadin kada ka damu da wanan.
Da zainab tana nan itace idan ya taso min takan ban wani magani data amsa min a can.
Wani iri mamud din yaji a ranshi da dan uwan nasa yai wanan maganan ya mike tsaye yana fadin abinda nake fadawa mami ke nan game da yarinyar nan tabi bayan ta asan abinda ake ciki tana fadin wai dama can bata dace dakai ba.
Gara ku rabu ta nema maka wata can daban daidai da kai mami ta manta cewa kowa na fada mata zainab alherice a gareka amma ta kasa fahintar hakan don kawai tana ganin girma da kimar iyayye ta baikai bane ta aure ka kome oho ?
Yau ma akan case din ku saida suka kwasa da jamal don kawai ya fada mata gaskiya kan hakan ta haushi da fada sai da ya fita ya kyaleta.
Dan murmushi ya sake kafin ya kai kallon shi ga wayan dake kiran layin shi har kiran ya katse bai daga ba ya mamud dai ido ya zuba mai a lokacin.
Kafin yace dashi shi zai koma office anjima idan ya tashi zai lekoshi yaji ya ake ciki sai jafar din yace dashi ba sai ka dawo ba ka huta kawai.
Yana fadan hakan ya mayar da idanun shi ya lumshe yana jin takon tafiyan dan uwan nasa har ya fita daga gidan.
Kiran wayan ne ya kara shigo mashi ya bude ido yana kallon bakom lamban dake kiran shi din kafin ya daga da sallama a cikin harshen turanci.
Sai yaji anyi mai sallama a musulunce ji muryan maishi ba yaro bane dadditijo ne kuma mai kamala shima ya amsa mai a mutunce.
Malam yace nasan ba lalai bane ka sanni amma zaka iya jin sunana a bakin matar ka zainab ?
Jin ya ambaci zainab din yasa ya gyara zaman shi da kyau yana saurare dattijon a lokacin malam yaci gaba da fadin.
Kan zancen matar ja nake son ka samu lokaci kazo mu zauna a kai kafin mutane su farga da halin da ake ciki tsakani ku.
Cikin karfin hali jafar din yace saidai malam ban fahinci ko dawa nake magana ba a yanzu a takaice kai waye gun matata ?
Dan murmushi malam yayi kafin yace da jafar din nasan haka nine kakar matarka zainab mijin maizube data zauna a wurin ku a farkon auren ku nan Abuja.
Ga mamakin malam din sai yaji ya gyara murya a cikin ladabi yana fadin a malam ne na gane yanzu ya kwana biyu ya jama, a ?
Malam ya amsa da fadin alhamdullahi tare da katse zancen da fadin idan ka samu lokaci ka shigo akwai zancen da nake son muyi ni da kai idan kazo.
Yayi wa jafar din sallama ba tare da bashi daman fadin komai gareshi ba kuma shima sallaman ya mayar mai suka kashe wayan .
Wayan yabi da kallo yana tunane me malam keson su tatauna a tsakanin su shi da shi ko zainab din dai ta fada masu komai ne yake son ganin shi ke nan ?
Ko kuma duk wanan neman da ake mata dama tana gidan malam ne iyayyen ta basu dan da hakan ba ?

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.