Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 76 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWAA hankali na fara takowa daga inda nake tsaye zuwa dining din a cikin tafiya mai kama dana hawainiya da nakan yi idan ina tafiya don sayin halina bai tsaya iya halina ba kwai har yanayin magana na da tafiyana a cikin sanyi nakeyin sa wanda sai mutum ya dauka sallone ya mayar dani hakan.
Ba iyanan abin ya tsaya min ba don har yanayin kukana idan ina yi a kusa da mutum sai zuciyar mutum ya shiga wani hali a lokacin don tausayi.
Gabana na faduwa na karaso inda yake zaune a gurin daning din a cikin tafiyana mai kama dana hawainiya da zaka dauka sallone ya mayar min da tafiya hakana.
Har na karaso inda yake zaune yana mamakin sauyina a cikin lokaci guda na yadda na sauya ma sanin da yayi min da farko na mika hannu a hankali na fara bude warmer din dake gabana har lokacin yana zaune ya rike haban shi da hannayen shi duka biyu ta hanyan yin tagumi dasu yana kallona.
Wani irin ferfesu na gani a ciki tare da wasu irin ganyayyaki da wani icce da ban san ko na meye ba na nufi dayan kulan zan bude naji ya dakatar dani yana fadin zuba min wanan din.
Da mamaki na juyo na dan kalleshi har lokacin yana zaune a yadda yake saidai wanan karon bani yake kallo ba.
Plate na jawo na soma zuba abinda ke cikin warmer din a hankali saida yagaji ya bude baki da kyat yana fadin ya isa hakana mana a cikin dakewa.
Mayar da marfin nayi na rufe naja kujera daga gefe daya na zauna ya dauki spoon ya fara kurban ruwan a hankali ta hanyar ja a cikin sallo.
Duk ina zaune gefen shi ina kallon shi ba tare dana motsa a inda nake zaune ba shi kuma ya mayar da hankali yana kurban abinsa hankali kwance.
Sai mamakin haka nakeyi a zuciyana a daidai lokacin ne wayan shi yai kara kamar ba zai daga ba ya dauka daga inda yake zaune.
Turanci mai kama da yaresu na chaina yakeyi naji yace outside da dan karfi kafin ya kara magana aka shigo gidan a daidai lokacin.
Mutum hudune dukkan su uku suna da kama da yan kasan sai na hudun nasu ne launin shi ya dan bambamta da sauran.
Tunda na daga ido na kallesu naji sam basu kwanta min a rai ba don yanayin shigan su ma yana nuna basu da tarbiya ko kadan.
Ina zaune a yadda nake a wurin ban ko motsa ba balle alaman tashi don shigowan su din sai dai a cikin daurewa nake zaune don yadda suka sameni a lokacin jikina babu hijjab a tare dani.
Duk wani iskancin da suka shigo dashi lokaci daya suka shanyeshi a fuskan su sai sukayi wani irin sayin a wurin.
Barin ma shi philis daya fi kowa iya iskancin don baida kunya ko kadan shi a gaban kowa yana iya nuna halinsa.
Addua nake a bakina kamar yadda malam yace inyiwa wanda duk ban yarda dashi da zarab zamuyi arba da maishi.
Yar uwa addua kan gaskiya ne don shi philis din da numfashinsa ya kusa daukewa yake tambayan zuciyar shi wanan wace irin kyaune da ita haka kamar ba black girl ba ?
Tun kan su zauna dayan ke kallona yake fadin wanan queen din fa kanwar kane Jackson ko yar uwarka koko ka fara harka da matane kuma ?
Sai dai wanan din ai tayi kankanta da yawa gaskiya sai dai idan sister din kace ko ?
Wani kallo ya watsawa philip din lokaci guda yana fadin wanan ba business din ku bane kun shigo muna gida haka babu notices bayan kun san family dina na gidan nan.
Mu kuma ba haka addinin mu ya koyar damu shiga gidan da yan uwa suke tare da yardewan mutanen gidan.
Dukkan su dariya sukayi idon su na a kaina kara daure fuskana nayi garesu don kar suga damana a lokacin .
Mikewa nayi a lokacin Allah ya taimakeni ina saye da wani bakin dogon riga nawa na larabawan jordan mai shara sharan hanaye sai dan dinkin maternity daga zuwa wuyan rigan don yana da fadi bai matse min ba a jikina.
Cikin wani irin murya da ba yaya din ba harsu din sun mutu a saurare duk da basu jin yaren da mukeyi nida shi nake fadin.
Ka karasa ci ne a kwashe kayan yanzu aifa tuni yanayina ya tafi da imanin su lokaci guda har wasun su na rayawa a ransu wanan ai mutum zai iya gwadata ya gani a cikin mata.
Ki barshi julie zata fito ta kwashe ki koma ciki kawai yanzu ya fada fuskan shi a daure saida abin yaso ya bani dariya sai na fuske na fara tafiya don barin wurin.
Shima yaya mikewa yayi yana kallon agogon hannun shi yana fadin kuna nan ke nan don ni fita zanyi yanzu.
Duk wani kallo suka bishi dashi lokaci guda suna mamakinshi don yin hakan da yai masu kafin su mike subi bayan shi zuwa waje don shi har yakai kofa a lokacin.
A wajen gidan suka sameshi ya dafa kan mota ya dan bada nauyin shi ga motar suka sameshi a wurin suna fadin.
Kamar bakai murna da zuwan mu ba yau gidan naka bayan babban tukwicin da mukazo ma dashi har gida bayan ka kori tj a gidan ka musan yanzu kana cikin matsuwa a dan kwana biyun nan da kayi ba harka a tare dakai.
Sai lokacin ya dago daga yadda yake yana sauke idon shi akan saurayin da suka kawo mashi har gida wanda suke kira da sunyi mai sabon kamu har gida.
Don yaron dan kasan Egypt ne sabon dan hannune shi farkon shiga harkan shi ke nan a yanzu don haka sukaga ya dace da jacksom din .
Wani irin kallo yakewa saurin da yake tsaye yana dan wani kame jikin shi kamar wata mace sabon shigan karuwanci a fagen maza.
Tsab ya gama kallon saurayin kafin yayi murmushi yana fadin a cikin wani yare kasan nafi son baki kamana don nafi ganewa hakan.
Dariya suka saka tare da fadin ka dai gwada wanan din ka gani zakaji dadin zama dashi sosai don yaron zai iya dakai a yadda yaken nan sosai.
Dan murmushi ya kakaro a karo na farko a fuskan shi tun zuwan su gidan ya bude baki da kyat yana fadin ya gode da kulawan su gareshi.
Ya riko hannun yaron zuwa gareshi tare da jawoshi jikin shi a daidai lokacin ya jamal ya shigo gidan idon shi kan abinda yake faruwa.
Bai tsaya kulasu ba ya wuce abinsu cikin jin haushin su gabadaya don ya gane mai ake kullawa a wurin .
Saboda yasan taju yabar gidan tun washe garin daya dawo gidan a buge yaji suna fada sosai da taju din har yakai yai mashi korar kare ta yadda ba zai iya dawowa ba gidan lokacin.
Bin ya jamal din sukayi da kallo kafin yace kai wanan lafiyayyen guy din fa haka ko kayi sabon kamune ko bamu sani ba ?
Wani kallo ya sakewa mai maganan kafin yaji dayan na fadin amma wanan ai suna da kama sak da jackson wata kila dan uwansa ne na jini ai.
Sai gudan yace amma guy din ya hadu ya shima dan hannu ne in tayashi don nidai guy din yayi min wallahi.
What ya fada da karfi tare da fadin blood brother dinane fa kake fadan wanan maganan a kansa.
To meye a ciki don na nemi dan uwan ka a harka bro ina duk karuwan kan mune hakan da inje waje ina neman wasu .
Zuwa lokacin ran yaya jafar din ya kai kololuwar baci don ji yake kamar ya shake abokin nasa a wurin saboda takaici.
Kadai rigani magana ne don ni gaba daya ya tafi da imanina a wurin nan don guy din ya hadu sosai.
Dayan ya karbe da fadin saidai baku ganin cewa duka yan uwan nasa suna da jin kai sosai don gaba dayan su babu wanda ya gaida mu.
Don ko kallo bamu ishesu ba dukko yadda muke da daraja a gari nan ake girmamamu sai gashi su ko kallo bamu ishesu ba ai.
Cikin wani tsawa ya dakatar dasu yana fadin zan halaka mutum a wurin nan idan baku rufe min baki ba yanzu da kazamin maganan nan naku.
Kallon yanayin shi sukeyi don sun fahinci ranshi ya gama baci a lokacin ga baki daya kafin suji yana fadin.
Ai wanan wullakanci ne da cin zarafi ku rasa wanda zaku danganta da wanan abin sai dan uwana na jini.
To bari kuji shi wanan harkan da kuke ganin munayi kowan ku nan yasan da addinin shi bai yarda da hakan ba.
Idan baku sani ba yau ku sani a kullun ina mai nadaman shiga wanan harkan naku da kuka koya min wanda addinina da al,adana duka ya haramta wanan abin ga wanin mu.
Yau gaskiya nayi nadaman sanin ku a rayuwana tunda har zaku iya kallon kanina ku nuna mashi sha,awan ku a fili babu dayan ku nan da ban ganin girma da daran dan uwanshi koda yan aikin gidan ku ne.
Daga haka ya juya rai bace ya bude motarshi ya shiga yana kokarin barin su wurin ranshi a bace.
Ganin hakan yasa suka san ranshi ya gama baci sosai alokacin da maganan su don sanin halin shi da sukayine zai iya sharesu har abada ga baki daya daga wanan lokacin.
Ganin ya shiga mota yana kokarin tayarwa ya wuce suna bashi hakkuri ta hanyar daya dace yasa ya jamal din sauke numfashi yana barin wurin da yake tsaye yana sauraren su a cikin takaici ya shige gidan.
Babu kowa a falon kai tsaye ya wuce zuwa part din shi yana mai jin zafin hakan daya faru a zuciyar shi.
Yana jin da zai iya a ranan zai bar gidan dan uwan nasa ya koma Nigeria saidai hakan ba zai yiyu ba don dole ya tsaya kodon hjy dake asibiti da kuma mu da muke zaune a gidan cikin rashin sani.
Don haka yaba kanshi hakkuri yana mai fadi a ranshi cewa fushi yanzu ba nasa bane idan shi yai fushi da dan uwan nasa mu yaya zamu kasance kuma ?
Bamu hadu dashi ba bama wada yasan da dawowan shi gidan a lokacin sai bayan sallah magariba da muka fito falo muka ganshi ya fito falon ya samemu muka gaisa dashi a wurin.
Mamane ke tambayan shi kona biyun nan wai meke damun shi ita fa batagane yadda ya canza ba akwana biyun nan idan anyi magana yace ba komai alhalin ba haka tasan shi ba a baya.
Mama banu komai wallahi ni dai kawai yanayin garin nan ne bai mun ba mun saba a gida muna ganin yan uwa da abokai ko ina.
Ta katse shi da fadin kai banda abinka baka ganin yaran nan matane basa fita ko ina amma a haka sun sake jikin su suna sha,anin su a gidan nan cikin rashin damuwa.
Balle kai na miji kamarka kana nuna haka a yanzu mu mata muce me ta fada a cikin raha.
Daga inda nake na saci kallon shi na fahinci akwai wani abinda ya bata masa rai a lokacin saidai banyi magana ba fun zaman shi a wurin suna ta hiran su da mama kan ciwon hjy da ake samun saukia yanzu kan jikin nata .
Don ko yanzu za a iya sallaman ta ta dawo gida saidai dan binciken da suka tsaya yi a kanta ya hana a sallamota daga asibitin yanzu.
Mikewa nayi don tunanen daya addabi zuciyana a lokacin na dan kallesu ina fadin mama ni zan shiga daga ciki .
Ke ko tun yanzu muna nan muna rage dare don ni wanan shiga kwanan da wuri haka ya fara isata wallahi aiba jamal shi kadai zaman garin nan ya isa ba a yanzu harni nan zama wuri dayan nan ya isheni wallahi.
Gashi mijin ki dawowan shi ba maza ba a gidan nan niko yanayin aikin nasane yake haka har dare ko wani lokaci dan gara yau ma ya dawo gidan nan yau da wuri.
Dan murmushi nayi ina gyara zamana ba tare da yin magana ba a lokacin sai naji ya jamal na fadin kila ta gajine da zama ai.
Ina fa gajiya ai bata dade da fitowa ba kazo kila dai don ta ganka zaune wurin nan ne take son ta tashi.
A,a mama ya jamal ai tun ina gidan mami mun saba dashi yana daga cikin masu tausaya mi a lokacin dashi dasu ya mamud .
Mu din ne bama tausaya maku ashe ta fada tana kallona a cikin zolaye nace da sauri a,a mama ba haka nake nufi ba wallahi kowama yana sona sosai wallahi.
Ai baki sani ba zainab wallahi ban gama danin halinki ba sai a dan zaman nan namu nan yanzu na kara tantace koke waye.
Gaskiya jafar yayi dacen mata idan kun dore a haka don ba ko wace sarakuwane tasan darajan iyayyen mijinta kamar yadda kike nunawa din.
Dadin wanan yabon da mama tayi min a yanzu naji na dukar da kaina ina dan murmushi kasa kasa naji tace kai gaka ba wani sakin fuska kakewa dan uwanka ba kwanan nan aida gobe sai mu rokeshi mu dan fita yawon mike kafa .
Tunda hjy dai taji sauki ba kamar yadda mukszo kasan nan da ita ba a cikin tashin hankali lokacin.
Taji sauki yanzu kan sai dai kuma yanzu data dawo zata fara fitina da mutane kamar yadda ta saba yi a kullun .
Dakuwa mama ta mika mai daga inda take zaune tana fadin ja,iri ai kuma naga hankalin ku ya tashi ai data kwanta ciwo.
Yana dariya ya mike tsaye yana fadin mama ni zan shige akwai dan wani aiki da zanyi matar yaya saida safe ke nan ya fada yana kallona.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.