Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 7 of 139

Wanka tayi ta shiya a gurguje cikin shigar manyan mata da boko ya gama ratsa su.
Fuskanta babu wani kwaliyan zama a tare da ita sai dan maikon mai data shafa sai man lebe data murza don yanayin garin.
Gurin takalma ta nufa ta saka wanda yai shige da kayan jikinta da sauri ta fito daga dakin duk da sauri takeyi amma idan ka ganta sai ka dauka takon isa da iza takeyi saboda wayewa.
Makullin mota ta dauka don bata bukatan driver a inda zata tafi yau don gidan safiya take son kaiwa ziyara da sa,a.
Tana bude falo sukayi kicibis da bakin ta dake hawo steps din da zai sada mutum da kofan shiga gidan.
Tsayawa sukayi suna kallon kallo a tsakanin su kafin hjy iyami ta fara fadin kune tafe banda labarin hakan.
Sai lokacin Alh isma,il yayi dan murmushi yana kawar da abin kunyan dayaso yi lokaci guda don ganin hjy dayayi a yau bayan tsawon shekarun daya dauka basu hadu ba.
Shima ya wayence da fadin af na manta da gidan bakar baturiya zamu ziyarta dole saida notice.
Kai ta girgiza tare da kallon wanda suke tare tana fadin sannu da zuwa kaidai shi wanan har kullun baya tsufa halin shi na kurciya yana nan a yadda yake da zolaya.
Ke kuma zolayan ne bakya so ba bissimillah ku mana ku shigo kasa na tsaya mun bar bako a waje.
Bako ko baki don nima bokon ne tunda ban taba zuwa gidan ba ai kinga na zama bako.
Hjy iyami tace kaidai ka sani tana ja dan gefe guda tare da nuna masu hanyar shiga don bata yarda su sakata gaba ba kasancewar su maza.
Falon suke bi da kallon yadda ake tsara komai zakace a kasan turai gidan yake don tun a waje suke bin ginan gidan da kallon sha,awa.
Zama sukayi saman kujerun alfarman dake falon kafin aka fara gaisawa tare da tambayan iyali.
Alh isma,il yana tambayan samarin hajiya daya sani take fadin kai ai yanzu sun zama magidanta in ka debe shi na biyun da har yanzu baiyi aure ba yana chaina yana aiki dasu a yanzu.
Kai masha Allahu Alh yace sai kuma yayi mata gausuwan rashin mijin ta don tun lokacin basu hadu ba dashi yace koda suka zo gaisuwa mata sunyi yawa basu shigo ba.
A lokacin yanayin hjy yadan canza take fadin hakane saidai bamu dade ba muka koma don yara dake karatu a can.
Bayan sun dan sha abin shanda aka cika masu gaba dashi yake fadin hjy dama kamar yadda nace dake magana ce tafe damu sai fuska da fuska zamuyi maganan .
Hjy tace kwarai hakan kace yanzu ku nake saurare ai dayan mutumin ne ya karbe zancen da fadin hjy nasan baki sanni ba ni.
To ni sunana Aliyu zaki kubau dan majalissan dake wakiltan nahiyar uku dake makwabtaka damu.
Munzo nan ne da wani bukata ko shawara na duba a gareki wansn ba wani zance bane sai sunan ki da muke son mu bayar don zaman ki macen data cancanci wani mukami da muke son a samu a tamu nahiyar a cikjn gwaunatin nan.
Ni kuma Alh har yaushe na dawo kasan nan da zan iya shiga wanan harkan na siyasan kasan nan yanzu.
Bayan haka kuma ni yanzu duk wani mukami na gwaunati ko wani aiki ban ra, layin shi saboda hutu nake so a yanzu a cikin iyalina.
Me nake nema a yanzu wanda Allah bai ban ba sai hamdala da shukura ga ubangijina ga yara sun kawo karfi suma Allah yana duba mana duk a yanzu.
Mun san da hakan hjy sanin hakan ma yasa mukaga cancantan ki ga wanan matsayin don kece zaki tsaya muna badon kudi ba sai don tausayawa jama,an mu.
Kada kace haka Alhaji don shi mukami da kake gani ba haka yake ba na rike na kuma san meke cikin sa sarau.
Balle mukamin irin gwaunatin kasan nan sai a hankali don mutane ba gaskiya suke so ba a yanzu niko kasan a bisa tubalin mijina nake komai shine gaskiya.
Don haka tun zancen baiyi nisa ba ina rokon ku da ku janye wanan magana a duba wata da ake ganin ta cancanci hakan a bata don Allah.
May na fadama Alh isma,il ya fada yana kallon abokin nasa cikin dan murmushi nasan wanan matar ba zata canza ba ai a yadda na santa tun farko.
Kaji ke nan ina nan a yadda nake har yanzu hjy iyami ta fada sai dayan mutumin yace hjy zamu baki lokaci kiyi shawara yadda ya dace don bamu son wanan daman ya kubbuce muna a yanzu.
Don dama ne da hujja da muke dashi akan ki na mace mai ilimi da matsayi irin wanda ake nema a wanan nahiyar tamu a yanzu.
Shiya sanni yasan ko wacece ni banda ra,ayin irin wanan mukamin ko a majalissan dunkin duniya danayi aiki dasu acan da ka fadi sunana sun san dani a wurin.
Hjy ki dai kara shawara a duba abin kamar yadda nake fada maki a yanzu don wani abin ansan badon kudi mutum ke rike sa ba sai don al,umman nahiyan ka.
Zatayi shara yanzu dai mun fada maki bukatan mu don Allah muna son kiyi duba ga wanan abin kafin mu sake dawowa muji shawarab da kika yanke akai.
Hakana dai sukai sallama ba tare da sunga alaman yarda daga gurin hjy iyami ba shi dayan mutumin daya kira kanshi da Ali zaki kubau yana cike da mamakin hjy iyami din don bai dauka akwai irin matan nan a jaharsu ba haka.
Unguwar da hjy bata fita ba ke nan a ranan don bayan tafiyan bakin ta sai taji kasalan fita ya kamata lokaci guda don tunanen maganan bakin nata da sukazo mata dashi.
Tsuki taja tana gyara kafan ta saman kujera data dagwara don taji dadin zama da kyau tana fadin ina zaman zamana kuja min sabon zagi da tonon asiri da tsufana.
Nikan dariya nayiwa hjy ina fadin hjy ina tsufan yake a nan saidai inda babu tsofin ko za a kiraki da tsohuwa ko dadtijuwa din.
Don babu mai ganin ta a yanzu yace itace mahaifiyar wa yan nan yaran nata a yanzu.
Sai data dan dade zaune ta tuna da zancen unguwar da zata tafi do yau taso ta ba su safiya mamaki ta ziyarci gidajen su su sanda suma yan uwane kamar kowa.
Don kawai sun fito ba ciki daya da yan uwan su ba bai kamata ana ware su haka ba a cikin dangi don tasha alwashin ida nufin marigayin mijin ta duk akan yan uwanta idan tana raye a duniyan nan .
Saidai muce Allah ubangiji ya ida nufi na alheri hjy da haka mata suke duka wurin raya zumucin da zumunci a yanzu bai tabarbare ba a duniyan nan.
Shigowan yaran ta dake gida suna hutu ne ya dawo da hankalinta garesu gurinta suka nufo kamar yara kanana muhsin ya zauna a gefen ta tare da rankwafo kanshi saman wuyan ta yana fadin wallahi mami na gaji sosai.
Kafin dayan ya zauna a makari kujera dayan gefeb yana fadin hajjaju zaman garin nan fa ya fara isata wallahi.
Gashi ko a nan zaku zauna don ba zan yarda wani cikin ku ya kara niss dani ba kamar yadda kewan dan uwanku ke wahal dani a yanzu.
Wai mami idan an tashi magana sai ki kawo zancen yaya jackson shifa ina jima yanzu ya manta da Nageria a ranshi.
Dan duka takai mai ga kai tana fadin daga min ya daga da sauri yana fafin wassh Allah na yana shafan wurinda ta dukeshi din.
Tana fadin har daku cikin batawa dan uwanku sunan shi na musulunci da kiranshi wai wani jackson cen ba dadin ji.
Allah hajjaju idan ba kince haka ba a turai babu mai gane shi ake afadi don jackson din ko jack ya rufe sunan nasa a yanzu.
Bai rufe ba ta fada a hayayyake shima idan yazo zan mashi magana kan hakan idan baso yake yaje lahira ana tayar dashi da wanan sunan kafiran ba.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.