Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 47 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4ï¸Â⃣0ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GA YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI YA KARA MUNA IMANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , ,
Yadda na zauna na makure kamar ban falon a lokacin don yadda nasha jinin jikina tun bayan shigowan shi falon.
A hankali ya dago kai ya dan kalli gefen danake kafin ya bude baki a hankali yace ya kike cikin nuna basarwa yai maganan ta hanyar daukan remote yana kunna tv dake kashe baya aikin.
Ban iya bashi amsa ba don tambayan daya jefo min yai min nauyi a lokacin sosai.
Saida ya kunna tv yakai tashan da yake so ya sake juyowa inda nake zaune a takure yana fadin ya naji kinyi shiru koda wani matsalane kuma ?
Hjy ce tayi karfin halin bashi amsa tare da fadin ba dole ba matsala dai yafi wanan ka kawomu nan ka aje kamar wasu marasa galihu haka.
Balle wanan yar bata tare da wani matsala tunda tana tare dani a yanzu ai murmushi zancen ta yayi yana gyara zama yace.
Nagode hjy nagode da nuna kaunar ki garemu da ba don ke ba da komai baizo a sauwake haka ba yanzu.
Sai da hjy na rasa meke damun mami har yanzu mami taki ta amince min aka ra,ayina, a rude na dan dago kai na dubeshi don jin abinda yake fadi a lokacin.
Hjy naji tana fadin ka barta da kanta zata gane gaskiya ta biyo hanya don kanta amma gaba dayan ku saikun daure sai dai kafin hakan nafi tausayin wanan yar da ake nunawa hakan a yanzu.
Na sake wani irin ajiyan zuciya da bansan fitowan shiba lokaci guda ina mayar da kaina saman kujeran da nake zaune.
Daga hjy har shi lokaci guda suka juyo suna kallona sai shine ke fadin me ya faru zainab yanzu kuma ?
Jin an ambaci sunana yasani dan dago kai daga yadda nake a zaune ina a hankali nace ba komai idanuwana suna kokari sako da hawaye lokaci guda.
Idan da son samu ne ka bari muje in gana da iyayyen yarinyar nan ko hankalinta zai kwanta don yanzu gaba daya hankalinta ba akwance yake ba da kowa a nan.
Idan hakan zai kwantar mata da hankali sai a shirya tafiyan ku hjy indai haka ba zai shafi karatun ta ba da zasu fara jerabawan su nan da mako mai zuwa insha Allah.
Ba matsalan komai ai itama da alama bata wasa da karatun ta don duk wanan halin da take ciki bai hanata karatun nake gani ko yaushe tana rike da littafin karatun naku.
Muryan shi na sake jin yana fadin zan koma hjy zuwa gobe an gama maku shirin tafiya in Allah ya yarda sai zuwa gobe da dareb zan shigo insha Allah.
Kaji namijin gaske haka nake son mutum da saukin hali ko yaushe ba irin uwarka da ta kasa gane hakan ba har yanzu.
Oh hjy kina akawa mamina ido da yawa har na fara jin kosawan hakan a yanzu acikin alaman mamaki hjy ta katseshi da fadin Allah ko ?
To da kaida uwar taku duk saina juya maku baya muga ta tsiya a yanzu kuma .
Yana dariya ya mike tsaye tare da fadin ko zaki daina sai bayan kin gama min aikina sai ki juya muna bayan ba matsala a lokacin .
Amma a yanzu sarkin yaki idan kika ce kin juya min baya ai ban san ta inda zan fara kamawa ba a nan.
Tashi ki takawa mijin ki mana kina zaune wuri daya haka hjy ta fada tana jifana da harara a take annurina ya kara gushewa lokaci guda na hade fuskana ga baki daya.
Bazaki tashi bane a hakan har zaki kai ga yadda ake so kina wanan sanyin jikin haka da wanan yawan matan dake dakon shi kamar dan sarkin das.
Simi simi na tashi tare da daukan hijjab dina na saka akaina na fice a falon cikin sanyin jiki nabi bayan sa kamar yadda hjy ta umurceni dayi din.
Ban san da tsayin shi gaf da kofan ba, saida na iso gurin ne nakusa cin karo dashi a guri yana tsaye ya dafe kofan falon da hannu daya dayan yana waya dashi.
Da sauri na dan ja baya tare da fadin yi hakkuri bansan kana nan ba a tsaye maimakon ya amsa min sai idanuwan shi manyattatu daya watsa min lokaci daya kafin ya saki wani shu,umin murmushin da bai kai ciki ba yana fadin.
Kai na kawar gefe daya ina bata rai tare da turo baki gaba saboda neman hanyan da zan samu kawai nake in fita daga kangin shi ga baki daya.
Madadin inga fuskanshi ya sauya ga abinda nayi mai rashi ya baci sai kawai naga yana min murmushi kamar ba jafar din dake da aji da class mai yawa haka ba yanzu a gabana.
Hakan dana gani yasa a cikin dakewa nayi kokarin juyawa ina fadin dama hjy ce tace wai na biyoka nayima saida safe wai ina fadi har na juya na fara tafiya do barin wurin.
Muryan shi na tsin kayo yana fadin ashe da badan ita ba baki san ki zo ki sallami mijin ki ba haka zamuyi dake idan mun tare a gidan mu.
Ko irin tarbiyan da kika koya ke nan a yanzu baki san ki girmama na gaban ki ba kuma baki san tarbiyan ki na daga cikin abinda nakeso ba fiye da komai.
Kalaman da yake fadi suka saka jikina sanyi a lokaci guda har ba kasa aiwatar da dan shirin dana kulla a zuciyana kan nayi mai rasgin mutunci ko zai rabu dani gaba daya a rayuwana.
Sai gashi ya buge ga yabona wanda naji dadin hakan a raina don kowa ba son a yabeshi a rayuwan shi.
Sai dai duk da hakan na dan turza dan zuciyana ta ban kwarin gwiwan fada mai magana nace ya Jafar.
Don Allah kaji tsoron Allah ka rabu da rayuwana a yadda ka ganni kowa yasan ni ba yar kowa bace ban taba tunanen irin kalaman da mami suke jifana dashi ba a yanzu.
Sai gashi a sanadin wani bukatan ka a kaina yakai mami tana aibantani tana aibantamin iyayyena da basuci ba basu sha ba a ka wanan magana.
Kasa nakai gwiwa bibiyu a kasan tare da hada hannayena biyu guri daya ina fadin ya jafar na rokeka da kafita harkata kabar rayuwana ya samu sallama.
Yau sanadin ka mami ta koreni gidan ta tayi min kazafi kala kala dani da iyayyena a gaban kowa har sai yaushe kake son kaiwa ga fita a cikin rayuwata hakane ?
Duk wanda ya ganmu a yanzu haka yasan bamu dace ba don ruwa ba sa,an kwando bane ansan ni din ba ajin ka bane sai dai idan da gaske yadda nakejin ana fada da wata manufa kake son yaudarana.
Kamar yadda mami suke fada kowa yasan kaiba tsaran aurena bane yaya tsadadden namiji kamar ka sai mace mai irin ajin ku bani zainab yar matsiyata ba haka don Allah ya jafar ko wani irin manufane a zuciyar ka katai makeni kabawa mahaifiyata ni kada in halaka.
Hjy kaka ita kadai ce mai kaunata tsakani da Allah gaba dayan ku yaran mami a yanzu ban yarda da kowa ba a cikin ku ina maijin wani kunci da bakin cikin a zuciyana saboda abinda ake min a gidan mami.
Wanda hakan ya kara nuna min banda gata da daraja dama a idon kowa wanda hakan ke kara haifan min da kunci da bakin ciki duk a sanadiyan halin daka jefani a ciki.
Jin nayi shiru don kukan daya zomin a lokaci guda yana tsaye a inda yake kamar an dasa shi a wurin yana tsaye yai kasake idanuwan shi a kaina sai zuba hawaye nakeyi a inda nake tsugune na hada hannayena wuri daya alaman ina rokon shi.
Tunane barkatai yake a gurin da yake tsayen ya zuba min idanuwa a lokaci guda ya na kallon yadda nake magana cikin fitan hayaci a tare dani ya rasa lalubo mafita yadda zai haneni fadin abinda nake fadi a lokacin.
A hankali ya fara takawa don barin wurin ba tare da ya iya furta komai gareni don bai san amsan da zai iya ban ba a lokacin yasa ya zabi yabar wurin kawai zaifi mai saukin sauraren kalamina a lokacin.
Duk da bashi ke tuka motan ba haka bai hanashi jin wani iri ba a lokacin don ji yake damuwan shi na kara shiga damuwa a lokacin gareshi.
Motar na tsaya ya fito bai tsaya jiran a bude mai motar ba ya diro daga baya motar ya nufi hanyar shiga cikin gidan.
Wayanshi ce ta dauki kara ya tsaya ya duba ya mamud ne ya gani a layi bai tsaya jiran komai ba yake fadin
Kana ina gani nazo gidan ka wurin su hjy ban sameka a nan ba ya fada yace gani na dawo gida yanzu na barcan din na zo gida.
Kada ka shiga ka jirani a waje ka ban mimtuna kalilan gani tafe insha Allah ya mamud ya fada ya amsa da OK sai kazo.
Daga haka ya mayar da jikin shi gurin motar daya fito ya jingjna jikin shi a kai tare da tunanen dalilin dakatar dashi da dan uwan nasa yayi waje.
Kodana koma ciki hjy tana zaune a inda na barta tayi min kallo daya ta kawar da kanta gareni nasan hakan bai rasa nasaba da shigowan da nayi ina sharan hawaye a fuskana lokacin.
Don irin yadda ta kalloni din yasa na sake shan jinin jikina din tare da samun wuri na rakube kamar wata marainiya dani.
Ban dago kai ga kallon ta ba sai faman dan share fuska da nake lokaci lokaci na tsinkayo muryanta tana fadin.
Yarinya kin takurawa rayuwanki kin hana kanki kin hana rayuwa ki shakat babu farin ciki kullun sai tsangwama sai tashin hankali.
Shima da yake namiji kuma ya dauki duk wani laifi ya hada a kanshi shi kadai bai tayarwa kanshi da hankali haka ba kamar ke.
Mikewa nayi ba tare da nayi magana ba na nufi dakin da muke kwana a cikin sa na daura alwala tare da gabatar da sallah isha,i na kwanta.
Ita hjy a nata tsamanin fushi nake don kawai in koma hannun mami da zama ko wani abu can a nata fahintar ta kasa gano inda na dosa da wanan damuwan da nake saka kaina a ciki.
Don a tunanen ta ai hutu na samu na rayuwa ga hakan don ta dauka nasan koshi din waye da matsayin da yake dashi a lokacin.
Ban kara fita falon ko neman abinda zanci haka na kwanta sai da asuba ba falka koshi itace dai da bata fushi ta tayar dani daga barcin.
Bayan na idar da sallah ne naji muryan hjy na fadin idan kin sallame kije falo akwwi sakon ki a can yai min nauyi ne naga gara dai na barshi falon harda safe.
Ban damu da nasan ko sakon may ba don ni gaba daya yanzu kowa ma haushin sa nake ji idan mutum ya shafi bangaren mami din.
Taci gaba da fadin yanzu sun canza magana wai yau din nan zamu bar garin nan karfe bakwai na safe don haka ki tasho ki fara shirin tafiya ta kare da bani umurni.
Dan juyawa nayi na kalli bangaren da take zaune ina mamaki a raina yadda kowa ke juyamu yadda yaga dama tun yanzu na fara fuskantan abinda ke gabana gaskiya talauci wani abin kine a rayuwa don zance talauci ne ya jawo min wanan gararan ba da walagigin rayuwa tsakanin mami da ahalin ta a yanzu.
Badan naso ba namike don zuwa falo saboda abinda hjyn ta fada a karshe da cewa wata kila akwai wani fitinane kuma daga wurin uwar tasu yasa suka sauya ranan tafiyantamu.
Nima zan fi so ai mu tafi yau hjy na matsu in bude idona in ganni a gaban iyayyena hakana .
Au ashe ni ke nawa haukan ke nan yar nan ina ce ai yanzu daga gidan nan sai dakina zamu dira idan mun tashi nan.
Ban yarda na juyowa ba a lokavin don jin abinda ta fada din don bansan amsan da zan bata ba kuma idan har na tsaya din don tsohuwar ta cancanci kawaici sosai a wurina.
Akwatinane har uku a tsakiyan falon da sauran tarkace da ban san meye a cikin su ba tsaye nayi daga kofa kamar mai nazarin kayan a lokaci sai da murya hjy din ya dawo dani hankalina da sauri na dan zabura tare da kaucewa a hanyan da nake tsaye.
Karaso man ki gani ta fada tana kaiwa zaine a saman kujera ga carbi a hannun ta tana ja tace jiya kin kwanta yaron nan jamal ya shigo da kayan nan .
Tare da bayanin yau karfe bakwai na safe mu zauna a shirye kafin su shigo ban daga a wurin ba kuma banda niyar hakan .
Kina tsaye kimkam dake a wuri daya ki zauna in maki bayanin komai kamar yadda sukai min kan kayan.
Hjy ba sai na ji komai ni kawai a mayar dani gida ko zan daina jin abinda nakeji a zuciyana.
Af kinsan Allah idan kin mun tsiya yanzun nan zan saka a fasa tafiyan nan ga baki daya, da sauri na dago ido na dan kalle ta sai kuma abin ya dan ban dariya nake fadin .
Hjy ba haka nake nufi ba ai kawai dai na fadi hakan ne don ki ce wani abu gashi ko kin fada din tace yo dama ai nasan don ni kika fada ai.
Don shi jafarin baya laifi a gurin ki sai ni da kika raina yar nema kikewa shegan taka irin haka ko ?
Kinga maza dauki kayan na kije ki saka idan kinyi wanka donni nan da kika ganni a shirye nake ko yanzu suka shigo gidan nan na gama shirina tsab.
Kallon ta nayi da mamaki a fuskana kamar zanyi magana don dai ni kan bana son in taba komai a cikin kayansu karshe mami tazo tai min gori tunda ma yan kayan dana tara a gidan ta bata yarda nabar gida da ko tsunketa ba .
Haka na fito tsula sai dan jakkar littatafaina da nayi karfin halin daukowa a lokacin don ba zan taba yarda in zubar da karatuna ba a duk halin dana samu kaina a ciki.
Sallaman da akayi a kofan dakin ne yasa mu dago kai don amsawa da sauri naja baya ina gaida shi yace zeey baki shirya ba ke nan yanzu ya J ya umurce ni daga massallaci in nufo nan nakaiku airport direct.
Yanzu nan zancen da nake mata ke nan maza dauki wanan jakkan ki shirya a gurguje bamu da lokaci hjy ta fada .
Ba musu na dan dauki jakkan data nuna min zuwa ciki ban tsaya ba wanka na shiga agurguje din da tace na fito.
Sai lokacin na bude jakkan dake makare da kaya nau,i, nau,i na mata da sauri najawo wani jan material dake sama ko tsayawa dubawa ban yi ba.
Sai danake sakawane na fahinci tsadan kayan a lokacin tsab na shirya a lokaci na fito na samu suna magana kuskus da jikan nata saidai gaba daya yanayinta ya sauya lokaci guda.
Kalma daya naji shine tace ai gara ayita ta kare yau din a gaban iyayyen yarinyar nan tunda ba lalama take so ba ita.
Jikina yai sanyi a hankali na tako zuwa inda suke hjy ta kalloni tana fadin kinbar kayan a ciki ne kuma don yanzu tafita zamuyi daga nan ba zancen karyawa a nan kuma.
Zan mike ya jamal yace barshi na dauko da kaina ya mike ya shiga dakin bai jima ba sai gashi da dan troler din hade da school bag dina dana bari a ciki.
Babu wani alama daya bari na shedan mun zauna a gidan kafin mu bar gidan zuwa airport ba bata lokaci jirgin mu ya daga, don mun so makara zuwa wurin.
Baifi yan mintina ba ni a ganina sai gamu kaduna har jirgi ya diremu ko ga motoci sunzo daukan mu a filin jirgin .
Nikan ina biye da hjy a bayan ta sai ya jamal dake directing din mu akan komai motan bai tsaya damu ba sai Anchau.
Abin kamar a mafalki nake ganin shi son tafiya sai yake min sauri kamar masu tafiya a gajimare ba a mota ba.
Ba farga a garin mu nake ba sai lokacinda aka karya kwanan unguwar mu abin ya ban mamaki matuka sai kawai gamu a gaban gidan mu.
Mota biyu mukai amfani dashi a tafiyan ina kokatin fita daga motan don zumudi naji hjy na fadin ki bi a sannu ki tuna kina da aure a yanzu din.
Don haka ki natsu sosai ki tuna ko a nan din kina da makiya tare da mahasda da zasu so suga faduwan ki don haka sai ki natsu kiwa kanki fada da kamun kai ki fara nuna yanzu ba da bane garesu.
Hakan yasa naji wani iri n natsuwa yazo min lokaci guda na tuna da abinda na bari a gidan namu tun farko don haka har gyalen jikina saida na gyara yafashi kagin a bude muna mota don mu fito a lokavin dirin motar yaja hamkalin kannena sun fito don ganin ko waye yazo.
Sannu a hankali aka bude kofan daga waje a bangaren da hjy take zaune kafinta ta fito a hankali ta sauka daga motar.
Driver ya dawo bangaren da nake zaune ya bude min kofan a hankali na dan dauki lokaci kafin in sako kafana a kasa na sauke su a cikin kasan kofan gidan namu.
Kyau ta kalman dake kafana kawai ya isa daukan hankalin wanda ke gurin a lokacin na karasa fitowa waje ina dan gyara gyalen kaina da kyau a hankali.
Duk yadda zan kwatanta maku haduwa a lokacin ba zaki gane yadda shigan ya mayar dani ba sai dai idan kin gani a gaban idon ki.
Takalma iri hill shoes din nan ne fari sol a kafata sai madaurin sarka fari da yake dashi.
Dinkin material din dake jikina mai kama da half gown sai ta kasan shi akai ado da wani yadi mai kama da lace mai kore da baki a jikin shi.
Hannun rigan yana da dan shara sharan hannaye har zuwa kasan hannun.
Hjy ce gaba ina daga bayan ta rike da yar karamar jakka mai kama da post a hannuna shige guda da takalmin kafana ina takowa a hankali.
Ga kannena ina gani kamar in shaka in rugume su sai dai ina ganin irin kallon basu gane mai shigowan ba da suke min a lokacin.
Sai da muka karaso gaban sa,ade a hankali na bude baki kamar ban son magana tare da fadin haka aka koya maki taron baki.
Wani ihu ta yanka tare da fadin wallahi yayan muce ta kwasa cikin gida da guda tabar kayan da take suyan awara a kofan gida.
Ihun tane ya jawo hankalin kowa a gidan yayi daidai da Abban mu na gida dakin lantana a lokacin duk da misalin sha biyun rana ne lokaci ya nuna a garin.
Abin mamaki sai ga innan mu a guje don ranan bata nuna wanan kawaicin ba nata da take nunawa a kaina na yar farin ta.
Saidai gani tare da hjy yasa taja ta tsaya kuma da dan tsohon cikin ta da ya fara baiyana a lokacin a jikinta.
Nikan ganin inna taja baya ta tsaya don ganin tsohuwar mai kamala da muke tare yasa na kasa daurewa na nufi wurun inna a cikin sarsarfa na rugumeta.
Ina jin wani farin ciki da shaukin ganin mahaifiyata da nayi yau sai nake jin kamar anyayye min duk wani matsalolin da nake ciki a lokacin don ganin mahaifiyana a gabana.
Wai abune kowa nake gani haka a idona Asabe ke fadi daga bayan mu ta fito daga dan lungunta ds yanzu duk ya gama yakucewa ba gyara kamar farko da Abban mu ke yawan gyara mata idan ya dauko lalacewa.
Itace fa Asabe sa,adaty ta cabe tana fadin yau Allah ya dawo muna da yar uwan mu gida yan bakin ciki yau kan sai dai su mutu ko a kasa barci don bakin ciki.
Masu farin ciki kuwa yau barci harda nasari don Allah ya baiya na gaskiyan shi a filin Allah kowa ya gani.
Daga inda hjy take ta amsa da fadin kwarai yar nan dama haka al,amarin Allah yake ai idan ya tashi ikon shi ba wanda ya isa ya hana hakan.
Yau ga yar ku ta dawo gare ku a matsayin matan jikana al,amarin aure daga Allah yake matar mutum kabarim sa.
Da sauri Asabe tace balle munan ai kowa dan farin cikine da hakan ai hjy kayya hjy ta fada a daiyi sha,ani ai da ba haka akaso gani ga jikan nawa ba.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.