Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 64 of 139

Suna zaune da ya mamud a haraban gidan mami zaune suna shan iska yazo mami bata gida ta fita zuwa unguwa yasa shi fitowa haraban gidan ya zauna nan ya mamud ya saneshi suka zauna suna magana.
Ganin yadda yake ta bayani dan uwan yai shiru ya zurfafa a cikin tunane yasa ya mamud din dan kiran sunan shi a cikin kulawa tare da mayar da hankalin shi gare shi.
Jafar meke damun ka na ganka haka yau ko wani abu ya farune yana kallon fuskan shi cikin kulawa yake tambayan shi.
Ya sauke ajiyan zuciya firgigit yana kallon dan uwan nasa ya mamud din ya sake fadin meye matsalan kane jafar a cikin yan dakiku ya mamud din yake jera mai wanan tambayan.
Ido ya lumshe a hankali tare da sauke numfashi mai kama da ajiyan zuciya yana fadin watau mamud ina cikin matsala da damuwa dani kadai na sani.
Sai kuma wani abin mamaki shine a dawowan nan nawa da nayi sai na sake tarar da wani abin mamaki a gidana wanda shine ke kara ban mamaki a yanzu.
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya numfasa yana kada kafa a hankali yayin da mamud din ke sauraren shi.
Ido ya bude yanaci gaba da kada kafan shi yace abin mamaki wanda ban taba tunane bashine waina dawo gida na samu wanan yarinyar gaba daya ta sake min lokaci guda.
Guntun tsaki ya mamud din yaja lokaci guda yana fadin yanzu akan wanan har kabi katada hankalin ka haka sai kace wanda yake cikin wani babban matsala.
Shi girman ya mace aiba wani abu bane duba ga irin rayuwan da a yanzu take a cikinsa ko kana nufin a yadda ka dauketa haka zata tabbata a gidan ka koda yaushe.
Kai ya girgiza yana fadin bashine nufina ba mamud sai ka jira kaji karshen zancen mana kafin ka yanke min hukunci kasan abinda ya sakani a damuwa akan hakan.
Ya mamud din yayi kasake yana sauraren dan uwan nasa tare da zuba mashi ido don a yanzu ya tabbatar da duk abinda kanin nasa ke shirin fada mai matsalace babba don ba akan girman nawa dayaga na masa bane lokaci guda.
Huci yayi ga bakinsa sai wani gumi dake tsarso masa a goshin sa tankar wanda ya watsa wa kansa ruwan zafi a lokacin.
Shikan mamud yana ganin yanayin dan uwan nasa yayi saurin fadin wai jafar meke damuwan kane haka ?
Nifa gaba daya duk ka sauya min kamar ba kaiba wanan wani irin damuwane akan zainab din wanda ya susutaka haka har ka tayar da hankalin ka haka wai ?
Mumushin karfin hali yayiwa dan uwan nasa yana fadin mamud kafi kowa sanin bawai na auri yarinyar nan bane don na zauna da ita irin na ma,aurata a yanzu.
Jafar wai wani irin magana kake kokarin fada min a yanzune wai don me ake aure a rayuwa badan mutum ya aje iyali ya haiyayya fa shima ya bar baya kamar yadda iyayyen mu suka barmu.
Yanzu fa jafar kana kokarin rufe bayan talatin da biyar ne a rayuwa don in ban manta ba wacan zuwan naka mami ke fadin kana talatin da biyu a duniya.
Me zaka jira da matar ka Allah ya baka mace ta gari da zaka inya controling dinta yadda kake so agidan ka tun a yanzu kan kanta ya karasa wayewa.
Nida aca tun farko irin matar da mami ta zaba min ke nan ba wanan ba da nake fama da ita a gidana yanzu don ban isa in tsayar da Nuriya wuri daya ta tsaya ba.
Shine abinda nake lurar da mami akan auren ka da yarinyar nan zainab a kullun do ko ita mami Nuriyan bata ragawa ba kasani.
Jafar din ya dukar dakai kamar yana sauraren dan uwan nasa abinda yake fada nan ko wani duniyan tunane ya fada a lokacin.
Can ya dago kai yana kallon dan uwan nasa kafin yace a cikin kyarmar murya kaman mai shirin kuka a lokacin, mamud mafita nake so a yanzu kan wanan auren nawa.
Shiru mamud din yayi don ya rasa inda dan uwan nasa ya dosa da maganan shi yaji jafar din na fadin bana son in rasa wanan yarinyar a yanzu mamud don ina matukar jinta a cikin raina rasa zainab a rayuwana tankar rushewan wani bangaren rayuwanane a yanzu.
Cikin mamaki ya mamud ya dago kanshi yana kallon dan uwan nasa da mamaki don har yanzu ya bai fahinci abinda dan uwan nasa yake nufi ba.
Can ya dago kai yana ftambayan kanin nasa No jafar ka daina fadan haka don Allah ko akwai wani abinda yarinyar nan tayi makane kake son ka boye min dai ?
Kai ya girgiza yana gyara zaman shi tare da lasa saman labben na sama yana mai shafo kanshi a hankali cikin damuwa.
To jafar wanan wani irin wullakanci kake son yiwa yarinyar nan haka koka mai damu mutanen banza a daukemu wawaye wadanda basu san abinda sukeyi ba .
Nace ka fada min meye damuwan ka da ita kana kawo min wasu dalilai marasa tushe a yanzu.
Mamud ba zaka gane bane amma gaskiya nasan bazan iya kula da hakkin yarinyar nan a yanzu ba ko nan gabama.
Innalillahi ya mamud ya fada tare da wani irin zabura daga inda yake zaune din kafin yakai ga cire hulan dake kanshi yana dan fifita dashi a hankali don ya samu iska a jikinshi.
Kafin ya iya buda baki ya furta a sanyayye jafar baka da lafiyane ko wani abinne ya sameka kake boye muna.
Kai jafar ya kada mai alaman a,a ba hakan yake nufi ga maganan shi ba da akwai dai wani zance can kasan zuciyar shi.
Jafar ka tuna koni wani abin ya shigewa duhu daya shafi rayuwana kai nake nema in fadawa ka ban shawara akan hakan don me kai a yanzu ba zaka fada min naka damuwan ba a gabana.
Mamud nasan da hakan shawara kawai nake son ka ban har lokacin da komai zai daidai min a rayuwa na fuskanci matata.
Wani irin ajiyan zuciya ya mamud din ya sauke lokaci guda tare da fadin anya jafar kana da lafiya kuwa ?
Yanzu dai na gama fahintar wanan yarinyar batai maka komai ba don haka koma menene yake damun ka a rayuwa ka lalaba matar ka ta hanyan kyautata mata a rayuwa ta yadda zaku zauna lafiya da ita.
Saidai ka tuna kada ka yarda ka cutar da yarinyan nan da yawa katuna ba a duniyan nan zamu tabbata ba har idan ka cutawa rayuwan wanan boyan Allah Allah zai saka mata ta ida baka zata ba.
Kai jafar din ya sunkuyar a kasa don baida abinda zai fadawa dan uwan nasa a yanzu saidai ina son wanan maganan ya tsaya iyani dakai kafin komai ya daidaita ya mamud din ya fadawa dan uwan nasa.
Da sauri jafar din ya dago kai yana fadin nima hakan nakeso bazan so mami taji wanan zancen ba don zata dauke shi da wani fassara na daban.
Kada kaji komai jafar ka tuna duk abinda ya same ka mekyau ko mara kyau kamar ya shafeni ne koni.
Saidai zan so ka maganan ta makakewa ya mamud din don motan mami daya shigo gidan zuwa parking spece yasa suka mayar da hankalin su gareta tare da mikewa suka nugi wurin motar nata lokaci guda.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.