Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 17 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1ï¸Â⃣1ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH KA KAWO MUNA TSARO A KASAR MUNA NIGERIA, KASAWA WANDA IF,TILLA,I YA FARU DASU HAKKURI DA SANIN KADDARA A RAYUWAN SU, , , , , , ,
DARI UKU NE NOVEL DINA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALLAMA YAR UWA DON TURA KUDI GA NOMBA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN KO EIRTEL NA DARI UKKU.
Abba bai shigo gida ba sai gap da magariba ya dawo lokacin ina alwala a tsakar gidan mu dani ya fara arba.
Ja yayi ya tsaya tare da fadin wa nake gani nan kamar Abu ya fada cikkn mamaki don bai san da zuwana ba ashe sai wanan shigowan da yayi ya ganni.
Amsa na bashi ina mikewa a daidai lokacin ina kai dan ruwa a baki kamar yadda yin hakan ya zama min al,ada tun ina gida ba tafi kaduna har yanzu kuma ban daina yin hakan ba idan na idar da alwala don sallah.
Abba nice na fada cikin dan murmushi Abu ina kika shiga haka babu labarin ki ga kowa ita din da tazo ta dauke ki bamu kara jin wani zance a gareta ba har wanan lokaci.
Safiya bata kyauta muna ba ta barmu cikin zargi da fargaba don ba haka mukai alkwari da ita ba.
Ayi hakkuri Abba kasa anty ma,aikaciya ba ko yaushe take da lokacin tafiya ba irin hakan.
Yar mairo koma menene ai ya dace ta dan waiwayo musan halin da ake ciki dake a can .
Yanzu kai ganin ta yasa ka tsaya nan kana zuba har ka mata irin bakin cikin data jefa ku a tafiyan ta .
Lantana ce ke fadawa Abba hakan tare da mika hannu tana fadin ban ledan kafin ka shiga can a wawashe.
Tana mika hannu ta fisgi ledan daga hannun Abba ta juya tana fada abin kunya yarinya taje gantali tsawon wani lokaci saida tagaji don kanta ta dawo har kuna wani jin dadin hakan.
Abba yai tsaye kamar ba Abban dana sani ba yana bin inda tabi da kallo kafin ya juyo har na bar wurun ina kokarin shiga dakin innan mu ko.
Da mamaki a raina yadda naga komai na gidan namu ya kara hargitsewa ga baki daya na tayar da sallah.
Bayan na idar da sallah muka zauna da inna sai lokacin nayi mata bayanin komai a tsanake har sakon mami na dauko na bata na nuna mata na Abban mu da tace a bashi.
Inna tace aidai bata don wanan yarinyar tana kyala ido a kansu sai taga bayan su a lokaci guda.
Nace koma meye ai dai na isar da sako saidai inna nifa wasu abubuwa da nake gani a gidan suna daure min kai tun zuwana.
Me kika gani daya daure maki kai ai dama shi ramin mugunta kurarene idan wanda akewa yayi hakuri.
Bai wuce dai abinda kikaji ba tsakanin umma da lantana ko wanda kika gani yanzu tsakanin ta da mahaifin ki.
Duk waya ja hakan sai umma gashi kuma tun ba,aje ko ina ba abin ya koma tsakanin su yanzu.
Tana ji tana gani ganin danta yana batun gagaran ta a gidan nan tayi fada har ta gaji ta saka ido idan da can tayi mai aure ne don ni a gidan nan, yanzu bani kaida ke ganin bakin cikin ba harda ita.
Shiru jayi ina tunane a raina tare da fadin mai yai zafi tsakanin Asabe da lantana kuma yanzu.
Abba bai shigo dakin inna ba sai bayan sallah isha,i zama yayi muka gaisa na mike na dauko mai sakon shi kamar yadda mami tace in bashi.
Duban kaya yayi yana juyawa tare da fadin ikon Allah duk wanan matar ta bayar a kawo min nace Abba ai mami mutumiyar arzikice.
Zamanta mai kudi baisa ta raina tallaka ba nan dai na gutsura mai dan labarin mami din da aiyukan da nakeyi a gidan.
Abba ya kalli takardan dake hannun shi yana juyawa a hankali kafin ya fara kokarin budewa kudi suka soma zubowa daga cikin takardan yan dubu daya sabbi fil dasu.
Da mamaki yake fadin yahanasu kudine fa matar nan tayo muna sako a cikin takardan nan.
Na amsa da fadin cewa tayi kudin aikina ne in kawo maka da zanzo duban kudin Abba yayi kafin ya juyo ya dubi inna da ko kallon inda yake batayi a lokacin.
Wanan matar wani irin kudine gareta haka yar mairo ko harda wani sana,a kike mata bayan wanan ?
Gaskiya matar kwarai Allah ya hadaki da ita a birni don ba kowa bane zai iya maka hakan .
Mamaki kalaman Abba ya bani don na dauka zai tambaye fiye da hakan sai ga Abba ya buge da fadin in kara kwazo don gaba ta aiko da wanda yafi wanan din yana mikewa.
Malam iya abinda zaka fada mata ke nan dan ka rike kudin da baka tabbatar daga ina suka fito ba kamar yadda matarka ke fadi kullun.
Bana zargin tarbiyan diya na ko kadan don nasan tarbiyan da muka basu tun farko.
Allah yasa a kanshi take don nina tsuke da sakon wanan matar gaba daya hankalina bai kwanta da hakan ba ko kadan.
Abba yana kokarin tura kudin cikin aljihu yake fadin ance kudi kare magana ganin wanan kudin yanzu ya kara tabbatar min da gidan kwarai diyata take.
Bayan fitan Abba a dakin ne yai shiru na dan lokaci kafin mu fara jiyo hayaniyar Abba da Lantana daga kofan ta.
Lantana ba kunya take fadin yau sai dai a rabamu a gidan nan amma wallahi sai ka fada min abinda kajeyi dakin can ranan girkina.
Kinji ko haka muke fama da fitinan su a gidan nan koda shi koda umma don ni ba shiga shirginta nakeyi ba sai ta koma yi da yara yanzu.
Allah yasa har na tafi kada wani matsala ya faru tsakanin mu nace lokacin inna ke tambayan kwana nawa zanyi nace kwana hudu mami tace driver zai dawo ya daukeni.
Ba zan yarda ki koma garin nan ba batare da wani ya biki yaga a inda kike ba koda malam ba zai tafi ba zan hada ki da kawun ki lawal kuje tare.
Inna hakan yayi daidai don mami ma bataji dadin hakan da aka barni ba wanda ya biyo sawuna tunda naje garesu bayan anty safiya data kaini.
Matar kirkine tunda tayi tunanen hakan duk wata uwa ta gari wanan tunane ne zaizo mata a rai.
Yadda za a sake diya mace haka ba tare da wani nata yabi sawunta yaga inda take rayuwana.
Nagodewa Allah daya karba min addua na danake kullun gare ku hankalina bai taba kwaci ba tun bayan tafiyan ki sai dana samu sakon safiya a boye tana min bayanin halin da kike ciki tare da kwantar min da hankalina.
Tun wanan lokacin na falwala ma Allah al,amarin na kara dagewa da addua a gareku sosai.
Mun sha hira ranan don bamuyi barci ba sai da inna ta labarta min abindaya faru tsakanin Asabe da lantana tun bayan haihuwan lantana gidan nan.
Tunda lantana taga ta haifi namiji kamar yadda umma ke muradin haka a kanta shike nan take ganin ta gama da kowa a gidan nan shi kanshi malam gaba daya an rasa gane kanshi yana ganin itace hasken rayuwan shi ita da danta.
Bata yarda kowa ya taba danta a gidan nan dama ga dan bai faye lafiya ba wai yana da ciwon numfashi.
Subbahanallahi gaskiya banganshi ba tunda nazo ai ba zaki ganshi ba don ba barin shi gidan nan takeyi ba wai kada wani ya halaka matashi.
Tunda an fada masu wurin biye biyen bokayen su cewa wai asiri akai mai yazo hakan ba lafiya.
Jin hakan yasa na ra,ya a raina har na koma bazan taba yaron ba in Allah ya yarda .
Me zai kai ki shiga shirmen wanan mara mutuncin barsu ya kare a kan su ranan dai mun dauki lokaci muna tataunawa da inna.
Washe garin kukan yaron Lantana ne ya karade gidan dashi ina mamakin karfin halin inna data ki kulla al,amarin yaron.
Na fito don gaida Asabe da Abba da lantana sai na samu Abba yana tsaye yana rarashin yaron a waje sai tsala ihu yakeyi uwar na shafa mai magani.
Kasa nakai na gaida Abba na juya don gaida Lantana samu nayi tana hararana a wullakance.
Ban damu da hakan ba na fara gaida ita da kwana kafin nnace Abba meke samun shi tun dare nake jin kukan shi.
Kafin Abba ya furta Lantana ta karba da fadin kuka kan ai dole ne tunda an jefe shi bamu da hutu shi wahala ni a wahalce kullun idan dan ruwa ya tabeshi ko sanyi.
An kaishi asibiti na tambaya ina kallon Abba don ban yarda na kalli lantana ba don yadda naji ta fara maganan ke nan zancen innan mu gaskiya ne da take fadin sune suka jefa mata da don ana bakin ciki dashi.
Ina wanan tsohuwar gidan zata bari akaishi asibiti tace ina saka danta wahala ko yaushe yana kashe muna kudi.
Tunda ni ban yarda ta juyani yadda ta saba ba ace uwar miji komai danta keyi da matar shi idon ta na a kai.
Da dai Abba ka daure an kaishi asibitin birni bana kauyen nan ba aji mai zasu fada tunda yana wahala haka.
Tab abu mai wuya ke nan yaya muka kare da asibitin mu ma na nan balle har nawani birni can tunda ansan abinda aka kulla a kai ai ba a bada shawaran haka ba.
Koke don bakya nan ne ai da an sakaki a cikin wanan sherin don ni yanzu na san zamana da kowa a gidan nan ai.
Allah ya sauwaka sannu kaji na fada ina kallon yarin kafin in juya in wuce zuwa lungun Asabe dana sama tana zuba ruwa a buta zata zagaya ban daki.
Ban manta ba don ban yarda na shiga dakin ba a wajen na gaida ita na juyo na dawo dakin mu inda na samu kannena na shirin zuwa makaranta islamiy a lokacin don boko ana hutu.
Na taimaka suka shirya saida suka fice bayan inna ta basu ashirin ashirin din cin masa idan sun tafi.
Don ba ai abin karyawa ba alokacin lantana ce da girki kuma bata dora wanda za a ci din ba don yaron ta da ya kwana yana rigiman dare.
Wanka nayi na shirya cikin wani dogon rigan atamfa dinkin shi mai kyau ya dan matseni kadan .
Inna sai fadi takeyi mai za,a sayo min in karya dashi nake cewa ta bari a gyara dumame shi zanci don kada in takurawa rayuwan inna din.
Sai ga Abba ma ya shigo gida da leda biyu ya tsaya daga tsakar gida yana sa min kira na amsa na fito ya miko min ledan ya tafi da daya dakin Lantana.
Kosai ne da bread sai kayan shayi a ciki dana bude nake fadin inna ga kosai din ki diba ki karya da bread din don ni ba zan sha ba.
Nace bazan sha shayi ba inna dan dama kosai din zanci sai inna tace daidai ki sha abin ki mu in da sabo mun saba da wanan ai a gidan nan.
Inna tunda ga kudi a hannun ki me zai hana ku sai abinci rabi kuma sai ki juya shi kina dan sana,a dashi.
Shawaran da nayi ke nan a zuciyana Allah ne ya dubemu ya jefoki a lokacin da muke cikin bukata hakan.
Amma malam ya canza yanzu gaba daya a gaban kowa gari zai waye zai fita ya samowa matar shi abin karyawa muna kallo a gidan nan.
Inna ki daina damuwa da wanan tunda ubangiji yana kawo maki mafita da zaki duba diyan ki ki basu abinda zasuci.
Ire iren hiran da muke tayi ke nan a dakin inda na tillasawa innan mu sai data karya kafin yaran ta su dawo su hana taci tunda nasan tana son sha itama.
Karfe goma suka dawo gida da shigowan su abinci suka fara nema a gida suka samu ba a gyara ba zasu ci shi hakana da sanyi na basu kudi suka sayo taliya saratu ta dafa kowa yaci.
Na zaga wurin yan uwa da abokan arziki irin matan da nai sabo dasu ina masu kitso kafin tafiyana kaduna.
Har ya saura kwana daya ya rage min duk da zaman gidan namu babu dadi amma nake ji kamar kada in koma kadunan kuma.
Inna ta danyi kokatin ta sosai wurin yiwa hjy tsaraba irin na kauyen mu da zankai wasu mami din.
Washe gari karfe goma driver yazo daukana inna taso muje tare da kawuna kaninta yaga inda nake saidai anyi rashin sa, a kawun nawa yana da uzuri a ranan don haka muka dauki hanya dagani sai malam usman driver gidan mami a motar..
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.