Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 121 of 139
Wasa wasa har abu yakai ga karawa yaya jafar ruwa don rshin karfin jikin shi da bayayi a wanan lokacin dole mami ta tsareshi saida aka kara mai ruwa don ya dan samu karfi.
Duk suna falo gaba dayan su sun sakashi a tsakiya sai ya dan ci abincin da mami tazo dashi don ta fahinci rashin cin abincin sa a yanzu.
Mami na fadin kawai zaka halaka kan ka kan wata yarinya can da bata damu dakai ba kana kokarin jefa kanka a cikin halaka haka.
Kai haba mami na fada maki bafa wani wuri ta tafi ba tana gidan yar uwan maman suce ashe a kaduna .
Nayi mamakin ma rashin dawowan su jiya da basuyi ba don kwanakin dana bata ya cika jiya ya fada yana bata fuskan shi.
Kaiya yanzu kuma hakan suka tsarama cewa zata dawo din bayan ka gama fadin ta bata har kana batun yiwa mutane hauka.
Mami ai dole ya damu rashin jin ta a waya da baiyi ba na kwanaki kin san yadda kasan nan ya koma fa a yanzu ya mamud ya fada daga gefen shi.
Tama bata din mana Aisha ta fada waya damu da ita idan ta bata tunda ita bata san ciwon kanta ba ta tashi taje wuri ba tare da fadawa mutane ba.
A cikin wani murya yake fadin AISHA ya kalleta kawai ya kawar da kanshi tare da gyara kwanciyan shi saman kujera.
Kai haba Aisha wanan wani irin maganane haka kuma ku kullun baku son gaskiya wallahi Na,ima ta fada tana kawar da kanta gefe.
Kaji kuma Na,ima da wani zance ai gaskiya aka fada rufaida tace kawai ta tayawa mutane da hankalin a banza.
Do kawai taga kamar yanzu din daya take da kowa har zata tafi wuri haka ta share mutane don kawai ta dagawa mutane hankali ta karasa kasa kasa don tasan kwanan wasan.
Nifa ku bar wani kame kame a gaban shi mami ta fada idan ma zata tafi ne ta tafi din aini har na fara murna tafiyan ta sai ga mamud na fada min wai rudun jafar ne taje wurin yar uwar maman sune ashe.
A daidai wanan lokacin suka ganmu kwatsam a bazata daga ni sai sadiya da hjy umma muka shigo don a dakatar da zuwan mu da maizube don kada su dauka wani abinne hakan.
Ashe ko hakan yai muna daidai do yadda muka samesu gaba dayan su a gidan zaune a falo lokacin.
Da wani irin mamaki suke kallon sadiya dake shigowa gidan jaye da dan troler kayan ta kai tsaye.
Da sauri ya dan dago daga kwancen yana fadin sadiya kune tafe ashe ina yayar taki take duk wanda suke zaune a falon suka kalli juna lokaci daya.
Sadiya tana fadin gasu shigowa suna baya tare da gwaggo data rako su da zamu dawo a daidai lokacin muka shigo ni da umma da Nafisa.
Basu ba duk mun dan kadu muma da ganin su sai dai mun dake mun shigo kamar babu komai a rayukan mu lokacin.
Nayi wani haske fayau dani don dan raman danayi a lokacin saidai hakan kuma bai hana kyauna ya kara fitowa fili ba sosai a lokacin.
Gaba dayan su idanuwan su ya koma a kanmu sai Na,imace da su ya jalal ke muna sannu da zuwa don mami ta ma kasa magana a lokacin .
Saboda bata yarda da abinda suka fada ba ta dauka shirine kawai don su batar mata da hankali suka shirya hakan.
Muna amsawa ya dago shima don ganin mu tare da umma yana mata sannu da zuwa dole yana kallon gefen shi su Aisha da sauran sukai saurin mikewa suka bamu wuri muka zauna.
Gaisuwa aka fara a tsakani su da umma bayan mun zauna din kafin umma tace ashe kuma bayan tafiyan yar nan jikin maigidan nata ya kiya haka ?
Ya mamud ya saurin fadin eh wallahi da zazzabi ya dawo kasan da yai tafiya kuma sai gashi ya kira layin ita zainab baya shiga gida kuma sunce basu sameta ba a lokacin ya dada tayar mai da hankali.
Kai ai zainab bata bata a kasan nan in ba wani ikon Allah ba hikiman ta dai na yarinyane zakaje wuri ba ka fadawa mijin ka ba ya sani don hakane ma da akace ya bugo bata nan .
Yasa nace ai sai muzo tare nida taje wurina in bashi hakkuri kan hakan da tayi kasan yaran yanzu basu daukan irin wanan da muhinmanci su.
Kai haha mama aida baki taso ba ko ita dayan ma ta dawo ai yasan gida taje gashi an dade ba ahadu ba dole ta dan zaga ta gaida ku ai.
Hakane amma zuwan zai sakashi jin dadin hakan don yasan an mutuntashi kaga gaba sai ya bata bakin zuwa ko ina ta duba mu ko ?
Shi dai yana gefe sai dan murmushi yakewa umma din ba tare da yayi magana ba a lokacin .
Kallon tsab mami takewa umma tunda ta fara magana sam batayi kama da irin yan uwana da take daukan sune gareni ba kawai.
Don umma dai in ba don da duniya ya basu baya ba a yanzu tana cikin matan da a zamanin baya suke fada a kaduna aji.
Ya jafar ya dan kalleni cikin kulawa yana fadin ki shiga dasu ciki su huta ko kuna da gajiyan tafiya a yanzu zaka dauka wani zancen soyayya mukeyi dashi a lokacin duk suka zubo muna ido duk da basu jin me yake fadi.
Ganin hakan na mike tsam daga inda nake zaune ina fadin Nafisa mu shiga daga ciki ina daukan jakkar umma dake gefen ta aje inda ta zauna.
Duk suka bimu da kallo bayan mun mike din don basu so hakan ba a rayukan su gaskiya jin karin bayanin da umma din tayi masu don kwana uku na kara ga kwanakin daya bamu din muyi a gida ke nan.
Wanan ita din wacece mami ta tambaya bayan mun shige ciki yan aikin gidan kuma suna shigo da kayan mu a cikin gidan har lokacin zuwa dakunanan mu .
Ai ba lalai bane ya san yan uwanta duka duba ga yadda aikai auren su din kinga ba wai ansan yan uwan zainab din bane duka.
Bata daiyi kama da yan kauyen nan ba ita kila a wani birni take zaune Aisha ta fada.
Amma kema dai kina da yan uwa a kauye ko don ba kowane zaune a birni ba ina su hjy dasu mama Ramatu duk a kauye suke zaune.
Jamal ke fadin hakan ba tare daya dago kanshi ba daga latsan wayan da yake yi tun zaman shi a falon bai furta komai ba tunzuwan su sai yanzu.
Mami tace cikin tsawa zaka fara ko tun dazu nake kule daku kuna kokarin hana yarinyar nan shan ruwa ya fada mata.
Bata da kunyane mami ana magana sai ta dinga saka baki a maganan wataga ya saka baki a cikin zancen cikin mu ?
A daki kan muna shiga umma tana zama take fadin ikon Allah gaskiya dai tayi halinta don wanan matar bata iya boye bakin cikin ta ba sam.
Haka muke umma na fada ina kokarin cire lafayan dake jikina daga sama ina juyawa Nafisa ke fadin aini umma ban ko tsaya kallon su ba ni mamakin gidan nan nakeyi kamar ba a cikin kasan nan ba.
Ita da tasan kanta ai kinga wanan bai rudeta ba ko umma ta fada ai idan ranka ya baci ko ka hango abinda ba daidai ba har kana da zuciyar kwarai abin duniya baya rufe ma ido sam.
Hakane umma don mai daki shiyasan inda ruwa ke masa yoyo akace ita da ke zaune cikon su tasan irin rayuwan da take yi a nan.
Sallaman Fadilace ya katse muna zancen mu ta shigo da dan fara,a a fuskanta kadan tana fadin ina baya tun zuwan mutanen gidan su oga sai yanzu ake fada min kin dawo ashe.
Nan dai ta juya tana gaisawa dasu umma tare da tambayan lafiyan su inna tana tambayan sadiya sai gata ta shigo dakin tana fadin.
Anty wai yaya yace ga bakon mu ya shigo shima a kawo masa abinci da abin sha a falo.
Sai dai ganin anty fadila yasa ta dakatar da maganan da takeyi ta makaleta don murna a lokacin nake fadin bakin falin sun tafine ko suna nan.
Tace babu kowa yanzu a falon ina ga sun tafine don basu falo sai fadila ke fadin ai sun tafi yanzu ina shigowa dakin nan.
Nikan wanka na shiga don hakan ya zama min kamar dabi,a na yanzu ance zama da madaukin kanwa don haka shima yaya din yake da tsabta dole nima na iya hakan.
Abinci lafiyayye Fadila da a yanzu nake ganin sauyi a wurin ta suka gabatar muna tare da sauran yan aikin dake shigowa muna gaisawa dasu a lokacin.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.