Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 112 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWAZAINAB IDRIS MAKAWAALLAH YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YASA MUNA CIKIN YAN TANTUN BAYIN SA YA NUFEMU DA AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU AMIN, , , , , ,
LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKI SALAMA DA AMINCEWA DON ALLAH DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACOUNT 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , ,
Washegari mun tashi lafiya tare da kannena dashi mukai breakfast a cikin raha yana zolayan su har muka gama.
Ya mike zai tashi nake cewa dashi zancen tsaraban da za a kaiwa su mami din sa,adatu tace dayani sai naje na gaida mami tunda ba dadewa zanyi a nan ba idan za,a kai masu.
Allah ya gani banda niyar zuwa gidan mami kuma kan abinda sukai mun a ranan yasa na tsani sake zuwa da niyar gaida mami din gidan ta kuma.
Duk da nasan hakan abune mai wuya a wuri amma ba yadda na iya dole na amsa da hakan na dakyau sai naga ya dan kalleni a falaice baidai yi magana ba ya barmu a wurin.
Kamar yadda muka tsara hakan muka shirya da yamma bayan sallah la,asar don fita zuwa gidan mami din a karo na biyu da zuwan mu garin duk da nasan akwai kalubalin da ba za,a rasa ba ga zuwan namu gidan dake jiran mu.
Tunda a yanzu na gane dai ba zan taba haske a wurin mami ba don ta nuna min hakan a zahiri bata dai kaunana a yanzu sam.
Amma don kada kanwar tawa ta gane akwai wani abu a tsakanin mu da mami din yasa na daure don na kaita ta gaida mami din wanda ita take ganin hakan girmamawa ne a wurin ta.
Driver ne ya kaimu a cikin wani haddaden jeep dake fake a gidan tun zuwan mu nake ganin motan a jiye sai gashi yau da moka fito naga itace zamu fita da ita wanda hakan umurnine daga maigidan nasan.
Dukkan mu ukun mun gama haduwa wurin tara kwalliya da kure adaka inji bahaushiya wuri kwalliya muka dauki hanya har da fadila a wanan tafiyan sai da tayi mamakin jin cewa ta shirya zamu fita tare da ita.
Zaune take dakinta tana waya da yar uwanta dake fada mata hjyn su jikin ta ya dan motsa a ranan amma sun kaita asibiti taji sauki a lokacin tana dai kwance.
Bayan sun gama magana ne da yar uwan take tambayan mami din da cewa ashe jafar tare yazo da matar shi kasan wanan karon dazun nake jin haka da suke waya da yaya a falon hjy.
Dan wani basarwa mami tayi kafin tace tare sukazo ai yar rainin wayau yarinya da take ganin yanzu daidai take da kowa tunda ya maida ita wani abu a idon duniya.
A dama haka zata gani yanzu ai yaya tunda ta samu tsuntsu daga sama gasshe a hannun ta ba dole ta dauka tafi kowa ba.
Wai ki duba yarinyar nan saida ta kwana kusan biyar a kasan nan kuma a garin nan fa wai kafin zainab tazo gaidani .
Da sauri mama Ramatu din tace ita zainab din lalai yanzu wuyan ta ya isa yanka ke nan inda uwarta ce a garin zata iya hakkuri har kwanakin bata zo ta ganta ba.
Shina fadi nima Ramatu har yaran nan da basu san ciwon kansu ba suke ganin laifina kan hakan don nayi magana Nuriya kuma take fadin .
Ai bata burge ba tunda basu zo ganin mu da kama hannu ba da zasu zo shine fa wai jafar din har da daukan fushi dani don hakan.
Shi jafar din ta tambaya da mamaki tare da fadin kai yaro kamar wanda aka shanye da asiri kan yarnan wanan abubuwan da yakeyi akanta ?
Barni da mara mutunci zanyi magani su daga shi har ita don ba zai bar kasan nan ba sai da auren wata matar wanan karon .
Ta san cewa ban haifa mata dan ita kadai ba don su juya shi yadda suke so ita da iyayyen nata da yakewa bauta.
Wai yaya kina ganin zai yarda da hakan yanzu dama can bai yarda ba balle yanzu din kuma ya yarda ?
Zan tsaya sauraren shine Ramatu ai wanan karon umurni kawai zan bashi bawai rarashi ba daga shi har ita ai basu fi karfina ba Ramatu.
Zan zauna ne in saka masu ido tsawon wanan shekarun ba haihuwa ko batan wata tare dasu sai bakin kazafi da sheri da suke kokarin kulawa yaro ko yaushe shiko idon shi ya rufe baya ganin hakan ko kadan ?
Ai gara kan a gwada don shi bai sanin dadin hakan sai idan anyi zai gane gata akai masa da yin auren.
Shidai nagani Ramatu amma yaran nan da yake kansu daya duk basu ban goyon bayan hakan ba ai ni zan tsaya bin ta kansune halan.
Aisha ce ta shigo dakin a fusace tana fadin nifa mami ban ganewa wanan mai aikin naki ba fa duk akace tayi min gyaran daki sai wani abina ya bace a dakina.
Wayan ta katse tana kallon yar nata kafin tace wai bata daina wanan halin ba har yanzu kawai wanan karon idan zargina ya zamo gaskiya zan koreta ne don na gaji da zanbar yan aiki a gidan nan.
Kwanaki ina fada maku daga cire agogo in shaga ban daki sama ko kasa na nemeshi ban gashi ba a gidan nan.
Wazai dauka mami banda ita mudai tun barin mu da zee wallahi bamu kara samun yar aikin kwarai ba a gidan nan abu kamar da sa hannu a hakan.
Ita ma din aka sani ko hakan take wanan mai iya kilibibin tsiya da takom saka wa zai sani idan ma tanayin hakan ?
Kai haba mami gaskiya bata taba hakan ba ida ba dai wanan case na yaya j da ita ai zainab mutunce a wanan lokacin.
Tsuki mami din taja tana mikewa ta fito daga dakin tana kwalawa mai aikin kira da tantano tantano hat tana sarkewa wurin daga murya.
Matar ta fito da sauri tana amsawa da akala zatayi haihuwa bakwai ko shidda da haihuwa don dai ta dan manyanta kadan.
Tana fadin gani hjy mami ba tsaya jiran komai ba take fadin wai saunawa zanyi warning dinki kan taba muna kayane idan bamu baki ba.
Ni hjy mai kuma akace na dauka yanzu karya za ai maki muna tare da wasu a gidan nan bayan ke da za ace sune suke daukan muna kaya.
Wallahi sunma tallahi ban daukar maku komai ba hjy ta fada a cikin wani yanayi na bacin rai da rudewa lokaci guda.
A wanan lokacin mukayi sallama muka shigo gidan duk abinda suke fadi a kunnen mu wanda shigowan mu bai hana matar cigaba da magana ba tana fadin.
Hjy mezai sa na dauki abinda ba nawa ba idan ba a banba sai dai idan ba a duba bane da kyau.
Ban duba ba na nema banga dankune dana cire ba na aje saman side drower dina yanzu kuma na nema kaf dakin ban gani ba.
Da mamaki muka karaso tsakiyan falon inda suke matar tace nikan ban dauki dan kunne ba wallahi kuma ban maga yan kunne a wurin ba gaskiya.
Don Allah rufawa mutane baki mutanen banza duk haka kuke sai an yarda daku kwana biyu ku yaudari mutum mami ta fada a cikin takaici.
Wanda nasan gugan zana ce akai muna gaba daya lokaci guda harni dana shigo da yan uwana a gidan lokacin yasa mami fadin hakan don ta sokeni kawai.
Sallama na kara yi don kawai su bar zancen tunda mun shigo muzanci bada kyau a yadda sukewa matan .
Aisha ce ta amsa tana fadin kune a gidan sannun ku da zuwa tana yar sake yake a fuskanta muka karaso mami na fadin.
Ni dai ban taba dace da yan aikin kwarai ba a gidan nan kowa ka yarda dashi sai ya ha,ince ka a karshe ya nuna ma halin yan duniya.
Ta sake fadi a fusace jeki wallahi kifoto mata da dankunen ta kafin na hadaki da security ranki ya baci.
Ta juya zuwa wurin kujera ta zauna muma zama mukayi saman kujerum muna gaida ita .
A cikin mamaki ta dago kai tana amsawa tare da mamakin hakan don bata iya boye mamakin taba na zaman da mukayi akan kujera tana zaune sama itama a lokacin muke gaida ita.
Wanda ta dauki hakan a raini ne sosai a wurin ta, don kamar zaman tsara da tsara ne mukayi da ita a falon a ganin mami din.
Saidai ta daure ta amsa muna da kyat tana wani jan kamshi a tare da ita a daidai lokacin da wani yaron gidan yake shigo da roban da fadila tayi siling din kayan tsaraban Sa,adatu da tazo dashi.
Can ta juyo tana kallon shi tare da fadin wanan fa daga ina haka kuma tana kallon shi tana son karin bayani kan kayan da taga ana shigowa dashi falon.
fadila ke fadin hjy tsarabane da akazo dashi daga anchau shine aka kawo maki.
Inane haka kuma ta fada a wullakance tana dan bata fuska , a cikin dan murmushi fadilan tace mahaifan uwar dakin mu zainab ga kanwata nan da tazo jiya tazo dashi.
Ta dago ido ta dan kalli sa,adatu da mamaki ya fara kasheta a zaune tana fadin owo tazone ashe ?
Babu ko ya mutanen gida sai cewa tayi lafiya dai tazo ko wani abu tazo yi nan din da tazo tare da tsure mu da idanuwan ta tana karewa sa,adatun da mukai matukar kama da ita sai dai hanci da dan dogon fuska da haske kadan dana darata dashi wanda hakan yasa na fita kyau a gani da kuma wayewa shine kawai bambamcin mu.
Kai tsaye wanan karon na bata amsa da fadin duba mu tazo tayi taga saukan mu ta duba lafiyan mu.
Sai ta kawar da kai gefe can Aisha tace meye a cikin roban tana kallona ki duba ki gani mana da idanun ki na fada cikin dakewa.
Mami tayi saurin dago kai tana kallona don jin abinda na fadawa yar nata kai tsaye ta kasa danne zuciyar ta tace koma meye ai ba abinda baki taba gani bane da zai dameki har kina tambaya.
Wayana yai kara daga cikin jakka na sa hannu na dauko sunan ya j na gani a screem din wayan na dauka yake fadin kuna ina nace gidan mami.
Badai matsalan komai ya fada da sauri na ce a wayence babu don kada a gane tambayan da yai min din a lokacin sauran yan matan suka fito dakunan su.
Da yanzu dai ina ganin zaman su ya dawo Abuja ne suma bayan gama karatun su saidai ba wace tayi aure har yanzu a cikin su.
Rufaida ke fadin ba tare data kulamu ba ko tayi muna sannu da shigowa take cewa mami naji kina fada da wanan matar mai shegen baki.
Bari Rufaida macutan mutane ne yan aikin nan dukkan su ka basu amana sai sun yaudare ka maha,inta sai mutum.ya kwaso talaucin shi daga kawai yazo ya sameka da abinka yace zai cuceka har gida.
Af mami ai kin saba da halin su dama wahala ke koro su ai suzo birni aiki kome suka gani sai su dauka a banza ka sameshi kai wasu har su so hada kansu da yan gida su nuna sun fi mutane a karshe.
Dan murmushi na sake kadan ina fadin wanan kuma in kinga haka dama can mutum ba wullakntace bane da baiwan sa yazo .
Wasu ba sunan aikin suke zuwa ba cin arzikine sai kiga sun fi masu gidan iya shege don kawai haye daga sama ba a san kan arzikin ba.
Ai abin ke dai daga Allah ne da yake tsarawa kowa rayuwan shi yadda yaso mu zamu koma mami dama na kawo sa,adatune ta gaida ke.
Ban jira me mami zata fada ba na mike tare da kallon inda su Aisha suke ina fadin mun barku lafiya mun tafi.
Idan mijim ki na gida zan shigo don ina son ganin sa ki fada mai ban ko tsaya ta kanta ba na karasa gaban mami tare dan dukawa ina sallaman ta muka fita.
Shiru motan ba wanda yai magana a cikin mu kowa da irin tunanen da yakeyi a lokaci a zuciyar shi.
Mami kamar bata son ganin mu gidan ta kullun mukazo sai ta dinga daure fuska tana nuna bata son ganin mu.
Babu yadda zatayi ai dole ta ganku tunda danta ya dauko ku gidan shi bai kuma gaza da ku ba a rayuwan shi .
Don haka tayi a banza tunda bata sadai ya sake ki sai dai tace zata kara mashi aure don ki don kawai ta bata maki rai don kiyayya.
Aure kuma aishi yaya din ba zai yarda ba sai dai idan yana ra,ayin hakan dama zai yarda da shawaran nata sa,adatu ta fada .
Nidai ina jinsu ban tanka masu ba ina tunanen wanan maganan da fadila ta fada yanzu don tabbas hakan zai iya faruwa ba wai bs.
Gashi a bakin fadila nake jin zancen don nasanta nasan halin ta idan ta fadi magana kamar ta auna ne kafin ta fada.
Mun tsaya wani shago don sayen yan abubuwan motsa baki da zamu gida dashi har lokacin banda walwala a tare dani har muka koma gida.
Zaune muke a falona muna hira ya shigo da waya a hannun shi yana yi shiru mukayi don shigowan nasa ga waya da yakeyi.
Yana fadin yanzu dai me ya kawo wanan zancen nasan zainab nasan abinda zata iya mami don haka ban yarda da wanan zancen ba.
Na fada maku ban son irin wanan zancen akan yarinyar nan matatace fa zainab don haka yan uwanta nada daman zuwa dubata duk lokacin da sukaga dama.
A hasale yake magana don ranshi daya baci kan abinda mami din ta fada mashi ya karasa zancen da fadin bana son irin hakan .
Wanan dalilin yasa bana son zuwan su nan din tun farko don bana son irin abinda naga anayi din nan gaskiya.
Shiru yayi yana sauraren su kafin muga ya kashe wayan ya tura a aljihun rigan shi ta gaba ya juyo yana fadin meya faru ne da kuka je gaida mami dazun.
Nima da mamaki nace wani abin kuma akace munyi da mukaje ya ja tsuki tare da fadin yanzu mami ta kirani tana fadin wai naja maki kunne kan abinda taga kina son yi mata yanzu.
Ni din bana fatan ranan da zanwa wani babba rashin kunya ko wani abinda bai dace ba don nasan darajan iyayyena da manya na tun kan nakai haka.
Nasan neman bakine kawai sukeyi kan hakan yasa na dauki matakin da ya dace a yanzu kan hakan.
Indai nice su bar bata lokacin su ai na fada ina kawar da kaina gefe don raina da yake a bace.
Ya juya ya fita sai lokacin Sa,adatu ke fadin amma matar nan bata da hali ashe har me akayi bayan sune suke gasa muna magana ba a kula su ba.
Ni yau da nice da sun san suna sake min magana don wallahi ba zan kyale suba su dinga daukana kaskantata koda yaushe bayan Allah ya daukakani a cikin su su nuna min bakin ciki.
Haka kawai zasu azawa mutum tsana da kiyayya don kawai hassada da bakin ciki irin na dan adam me suka rasa a rayuwan su da zasu kyashe da baiwan da Allah yai maki yanzu.
Da nace daku kada mu tafi ai zaku ga kamar banson zuwan kune gidan amma yanzu da kuka gane wa idon ku komai ko na fada nan gaba zaku yarda dani.
Ai itama tana da yara mata a gaban ta bata san inda Allah zai jefa rayuwan su ba nan gaba shi tallaka ba abin rainawa bane sam a duniya.
Ranan sa,adatu tayi fada har ta gaji ta kyale don kanta nidai ba wanan ne a gabana ba don inda sabo na saba da halin mami da yaranta tun kan na auri danta a baya.
Fadila ko cewa tayi idan bata so ai sai ta dawo da tsaraban karshen kiyayya ke nan ai da zata nuna min sa,adatu tace shine ai.
Sai na dauka zasu dawo da tsaraban da muka kai na sa,adatu din sai gashi naji shiru banga an dawo dashi ba har tsawon kwanaki shima bai kara zancen ba.
Sai dai bai kara zancen mami din ko wani na gidan su ba a gaban mu sai mazan ne kan shigo su dubamu jefi jefi zamu gaisa a cikin mutunci dasu.
Nakan yi mamaki sosai yadda mami wai ta manta da komai na halin yaya take kokarin daukan laifi ta dora min koda yaushe sam bata kokarin maganan kan zancen halaiyar nasa balle a san mafita a kan dan nata.
A kan wanan tunanen na tsaya a zuciyana cewa duk ranan da wani zance ya kara hada mu zan fito fili in fada mata hakan don tasan dan da take min kyashin zama dashi fa ba cikakken namiji yake kamar kowa ba.
Sai dai me kuma a bangaren shi yaya Jafar din gaskiya yanzu yana jefa min wasi wasin akan shi ko da yaushe.
Don a gaskiya yana tsayuwan sosai akaina kan yadda mami din take kokarin nuna min zai tsaya ko a gaban kowa ya nuna shi bai yarda da hakan ba sam wanan ya kawo saukin wasu halaiyan da mami din ta dauko nuna min.
Wasa wasa saida sa,adatu ta shafe sati da kwanaki a wurin mu kafin ya shirya zancen zuwa gidan mu a lokacin.
Nayi mamakin irin tsaraban daya shiryawa tafiyan mu din da zan kaiwa iyayyena da yan uwa a gida.
Ga kuma kudi daya ban don kawai wanan tafiyan da har na rasa me zanyi dasu idan naje gida din don yawan su.
Lalai ka bar wanda yafika da wayaushi da hikima a kanka don sai Allah zai iya kwato ka gareshi gaskiya .
Don nikan yaya Jafar ya nuna min ya fini hikima da wayau tare da sanin duniya a yadda yake nuna min kamar babu gobe a kan mu wurin kulawa.
Saidai hakan bai hanani matawa da irin zaman da mukeyi dashi ba duk da yana rudina da abin duniyan da yake gani zai iya matar dani ga komai dake tsakanin din dashi na basajan da yakeyi wa mutane dani.
Wanda ya samu hakan ne ta dalilin hakkurina da zurfi ciki da Allah yai min wanda sam ban nunawa mutane sai idan kana da kula sosai zaka iya gane hakan.
Don ko zuwan sa,adatu wuri mu ban yarda ta fahinci irin rayuwan da mukeyi dashi din ba don yawan shakuwan dake tsakanin mu dashi zaka dauka wani zamane najin dadi akeyi tunda ba a daki daya nake kwana dasu ba.
Muka dauki hanyan garin mu a safiyan tafiyan cike da dauki da ka,idan zamuyi sati daya a gida mu dawo Abuja lokacin.
Na dauki duk wani abinda nake bukata har takarduna da bazan iya bari su a yanzu ba a matsayin riban da naci a zama gidan yaya jafar din danayi dashi.
Tafiyan mota masu lafiya karfe biyu da yan kai muna cikin gidan mu da mukai masu zuwan bazata a ranan do ba wanda yasan da zuwan mu a ranan sak ganin mu sukayi kawai ana muna sannu da zuwa.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.