Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 35 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

2️⃣8️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

LITTAFIN KUDINE DON TURA KUDI ZAKI TURO GA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU NE KACAL KATIN WAYA KI TURA GA WANAN LAYIN 08036959257

YAR UWA DON ALLAH KI DAURE KINA BIYAN HAKKIN MUTANE DON ABIN BAN YAFE BA KALMACE MAI NAUYI GA MUSULMI NAGODE.

Har lokacin idanuwana suna a rufe ga numfashinsa ina jin saukan su a kunnuwana idon na kara budewa don jin shirun da yai yawa na dauka nike haukana a lokacin shi baya ko wurin.
Yana nan tsaye a yadda yaken haka yasa na soma kokarin sunkuyawa ta kasan hannun shi in samu in wuce don tserar da rayuwata ga mami dashi.
Ji nayi ya kamoni ya kankame ni a jikin shi tare da mamaye ni cikin wasu irin abubuwan da ban taba tsintar kaina a cikin ba ko a mafalki ban san da wanan nau,in abinba.
Haka kuma ban taba sanin ana wanan abin ba na dauka sai kafiran turawa da nake ganin haka a film danazo gidan mami.
Suma din kuma idan sunayi kawar da ido nakeyi koma na tashi na bar wurin ga baki daya.
Can kasan makogorna na iya furta innalillahi don Allah ya jafar ka bari kada kayi min sanadin da mami zata koreni gidan nan.
Bai kula da abinda nake fadi din ba yaci gaba da abinda yake min kamar ma zancena ya kara mashi kaimi ne .
Babu inda baya karkarawa a jikinsa don abinda yake min din nikan na sadakar sai hawayen da ke zubomin kamar an sake famfo na barwa Allah lamarin sa duk abinda Allah ya kaddara min mai kyaune.
Muryan shi naji a kunne kamar mai rada yana fadin mami kike tsoro yasa har kika fara guduna kina boyewa ?
Idan mami din ta sakaki ki min hakan ko ta hana ki aure ni kamar yadda na bukata ai ba zata hanani wanan bako ?
Abinda mami taji ke nan a karshe wurin da take tsaye ta mutu a tsaye don mamakin ganin halin data same mu a ciki a dakin.
Da sauri mami ta juya kafin ko wanin mu ya ankara mu farga tana gidan a lokacin ta nufi dakin ta da sauri duk maganan da hajiya ke mata a falon bata jita ba.
Karan sakin kofan da mami tayi ne ya farga damu don dai kawai tsoron dake yawa a zuciyana ne daya rufemin ido ban farga da ita ba tun shigowan ta dakin.
Yanzu kan sheshekan kuka na fara mai don na kula in dai ba mami ba hjy tsohuwa ce ta rutsamu a halin da muke ciki.
Ya jafar don girman Allah don ya rasulillahi ka, , , , , shhh yace tare da fufe min baki da hannun sa na kasa karasa abinda nake nufin fadi karshe.
I boldly care da duk wanda zai shigo ya same mu a haka dake dakin nan idan su basu san soyayya yada yake ba wanan ni bai taba damuna tunda sun hana min abinda nake so.
Naji yaya ba zaka taba damuwa ba don kai nan gidan kune bayan hakan kuma kai na miji ne dama mace itace da kunya ai.
Idan mami ne ta bar wurin nan na tabar da yau ban kwana a gidan nan don ta riga da tayi warning dina tun kan muzo garin nan a kanka.
Babu inda zaki tafi matukar ina raye a gidan nan doIn ko kin tafi dawowa zakiyi ita mami tasan halina idan ke baki sani ba.
Ban taba cewa ina son abu har in sashi a raina ban in rasa samu wanan abin don haka ba zan soma shi a kanki ba.
Naji amma don Allah ka barni in bar gidan nan yanzu tun mami bataji wanan maganan ba yau ta kasheni gidan nan.
Don girman Allah ka daga, daga nan in fice na fada cikin wani irin kuka daya zo min mai karfi.
Maimakon ya daga daga wurin saima naji yana kokarin kara matseni a jikin shi.
Kayi ma Allah kaimun alfama na hadaka da girman iyayyen ka ka daina rike ni haka kana hadani da fushin ubangijin mu.
Ka rabu dani ya jafar ka kyale rayuwana hakana ya huta da wanan ukuban daka sakani a cikin sa yanzu.
Ka taimakeni ka taimaki rayuwana da kake shirin rusa min yau karatuna shike nan na rasa shi tunda mami kauye zata mayat dani ina gap da gamawa.
Nima ki taimake ni zainab don ke kadai zan aura a kasan nan in zauna lafiya dake bani na sawa kaina son ki ba Allah ne ya zaba min ke don hakkurin ki da tarbiyan ki.
Abu daya nake so dake shine ki daina cewa zaki bar gidan nan ko karatun ki zai tsaya ba wanda zai faru daga insha Allahu.
A razane na dago kai na kalle shi kafin in mayar da kan kasa don kwarji da nauyin da yai min ga kallon shi.
Ya daga min gira yana fadin nasan mami zata yarda da bukata na idan na kafe a kanki a cikin sauki.
Don farin cikin ta shine nawa itama nawa shine nata bata taba hanani abu nayi shi ba a duniyan sai wanan karon kinga ko zatayi min adalci a nan.
So da sannu mami zata fahinta ta yarde mana muyi aure in dauki mu tafi can inda zaki karatu sai kince kin gaji da karatu a rayuwan ki.
Wani irin takaicin sa da tsanar sa yake tokare min zuciya ga tausayin kaina danakeji nida kaina kamar in dora hannu aka in ta kurma mai ihun a dakin sai anzo an ceceni.
Sai da ya fahinci ya gama hada min zafi akaina don kansa ya janye min daga banga bangan dayi da farko ya tare ko ina da zan iya sulalewa in gudu daga tsayin dayayi a gaba.
Kamar jira nake ya nuna min kofa in gudu aiko yana nunawa na sheka da gudu ina kuka mukai karo da hjy a kofa da tazo shiga kamar.
Duk da nayi murnan ganin ta amma naji haushin da sai yanzu ta zo dakin duk dadewa da mukayi a tsaye tare dashi zuwan ta yai min kama da zuwan yan sandan indiya da sai an gama cin gari suke isowa.
Fadawa nayi a jikin ta ina kuka take ta rude a wurin tana fadin a rikice maikai mata jafari na fadama kabi yarinyar nan a sannu akwai kurciya a tare da ita yanzu sai ka lalabata tukunna.
Ask her idan nai mata wani abin just magana nayi mata kan guduna da takeyi kawai.
Ba dole ta gujeka ba kaida uwar ka kun saka yar mutane a gaba haka wanan hattaran yai wa yar nan yawa a gidan nan.
Ai saika tashi kaje don uwar taku ta dawo har ta leko nan baka sani ba kana nan kana gyara kanka a wurin mace.
Hjy kefa kikace sai na jata a hankali zata fahinceni na fara hakan kuma laifine yanzu hjy ?
Laifine kan indai zaka dinga sakata kuka haka ko wani lokaci murmushi ya sake mai laushi yana kada kai tare da fadin well i know what to do next barin leka mami ya fada yana mikewa har lokacin ina a jikin hjy ina dan sheshekan kuka.
Yana fita daga dakin na dago kai ina fadin shike nan hjy yau zamana ya kare karatun da nakewa murna ya tafi daga gareno don mami korata zatayi yau gidan nan.
Saboda kawai kun kebe dashi a nan zata kore ki hauka tayi kome daga haka sai kora kawai.
Hjy mami tayi warning dina tun a kaduna kada in yarda in tsaya da danta don ta riga da tayi mai mata ko.
Ita iyamin ta fada maki hakan na gyada mata kai kawai ba baki idan ma har ta fadin hakan ai yanzu bake kika bishi ba shi ya biyo ki ko sai tayiwa danta fada shida ke binki.
Dakin mami ya nufa direct ba tare da jin komai a zuciyar shi ba duk da hjy ta fada mai mami ta leko dakin mu yana ciki yasan kuma ta ga halin da muke ciki a lokacin.
Da sallama ya leka dakin ba,a ansa ba haka yasa kai ya shiga dakin mami ya hango a zaune gefeb gado tayi tagumi da hannayen ta dukka biyu kamar wacce ke cikin tsananin damuwa.
Ta rasa abinda ke mata dadi a duniya yaron nan wani abin kunya haka yake son jawo mata ne duk ita a zaton ta ya bar wanan zance ashe shi yanzu yakema ga zancen wata namiji dai sai a barshi ga abinda yake so ya kwallafa rai kuma.
Kallon mamaki yake mata har ya karasa bakin gadon da take zaune a kai yace mami lafiya kuwa na ganki a haka ?
Wani abu ya faru ne ko wani abin kike tunane haka ke kadai a daki kinyi tagumi.
Ido mami ta dago ta gallamai harara da idanuwan ta da suka kade sukai ja tankar zasu fado.
Ji take kamar ta wanka mai mari da tana iyawa a yanzu so yake ya tozarta ta ya kunyata ta a idon kawayen ta tozarta.
Maganan hjy da take tunawa guda biyu shike taka mata burki ga koran yarinyar nan ta koma kauye.
Saidai idan ta tuna da kalamin hjy da take fadin idan ta kori yarnan a gidan ta sai danta yaje gun iyayyen ta a bashi ita ya aure muddin yaje da waliyan shi makusanta ita kuma a barta tana hargowa a gida.
Ga kuma barazan hjy data ita kuma idan ta matsa sai ta dauke yar ta koma da ita wurinta ta inganta rayuwan ta fiye da tsamanin ta to me hjyn ke nufi da hakan.
Hannun ta ya riko don yaga ko a yanzu da take kallon shi hankalinta na ga tunanen da takeyi a lokacin.
Riko hannunta yayi yana fadin haba mami meye zai sakaki irin wanan damuwan haka kinsan fa yanzu aiki na maki ya, , , ,
Baiyi aune ba yaji saukan mari a lafiyayyen fuskan shi lokaci guda ya dago kai da mamaki yana kallonta da kyar ya iya furta mami you slap me ?
Ko zaka ramane tunda yanzu ka girma har bakajin umurnina kake ganin kaika isa har yanzu kake mamakin na mareka ko ?
Allah yasa yanzu da idona na gama ganin ku da kazaman yarinyar nan a dakin hjy ba wani ya tsegunta min hakan ba.
Yanzun kai bakaji kunya ba ace kamarka jafar kamar kafa kamar kake rugumar wanan kazaman yarinyar zainab yarinyar da wani lokaci ma tsami takeyi da wari.
Da sauri ya dago kai a karo na farko tun bayan marin data kwasheshi dashi ya dukar da kanshi bai daga ba yana dafe da wurin cikin mamaki.
Wari mami wari fa kikace yarinyar nan tanayi ban taba jin haka ba a tare da ita asalima ni yau wani kamshin ma naji a wurin ta.
Mami nifa kome takeyi ina sonta hakana da don itace zabina a duk yadda take ya fada yana kokarin mikewa tsaye.
Jikin mami ya sake yaraf kaman ruwan sanyi a gabanta yau jafar ke wanan magana kan mace macen ma wai yar aikin gidan ta wanan wani irin lalacewa ne ya kama dan nata haka?
Ganin ya soma batrin dakin don tafiya don marin ma datayi mai shiko a jikinshi ya yadda nunata take ta soma magana tana fadin.
Yau da uban ka yana raye jafar zakai min haka ince ga wace nake son ka aura kace kai ba hakan ba yaushe ka fara wanan halin banzan na kafi ban sani ba ?
Mami daddy , aiko daddy yana raye ba zai hanani zaban abinda hankalina ya kwanta gareshi don dama daddy yana raye aida yanzun akaiga matsaya ga zancen nan don shi daddy ban taba ganin ya kyamaci wani a rayuwan shi ba
And mami kin san koda daddy yake da rai mun fi shakuwa dake fiye da daddyn mu
Mami kin kasa fahintana ne kin kasa tausa zuciyar ki akan yarinyar nan why mami zaki hanani abinda nake so.
Ba zaka aure ta ba nace bazaka aureta ba ko dole zakai matane mu gani idan zaka iya No mami ba dole amma nasan itama tana sona don naga alaman hakan tare da ita.
Tsoron warning dinki gareta ne take amma ba matsala zan gwada sa, a ta tunda kinban dama a yanzu.
JAFAR mami ta fada da karfi ya fice dakin ba tare daya juyo ya kalleta ba tunda mami take da danta haka bai taba faruwa a tsakanin su ba sai akan wanan dalili.
Me yaron nan yake nufi dani da wanan kalamin nasa tursasa yarinyar nan zaiyi taso shi tunda a yadda ta samemu a dakin da alaman tsoro shi a fuskana don kuka ta samu ina masa.
Ma,ana dai shi jafar din ne ke bibiyan ta a dole meya gani ajikina har ya mace ga son yar nan haka.
Yarinyar da saida tazo nan ma tadan yi wanan clean din da yake rudin shi ta runtse idanunta tana mai fadin kada Allah yasa so ya rudi yaron na ya aikata wani abinda zaija mata kunya ga idon mutane.
Ya zama dole ta jashi a jiki tasan hanyar data bi ta lalashi da lalama ya janye kudirin shi akan yarinyar na don koranta gidanta baida wani fa,ida a yanzu idan tayi amfani da maganan hjy.
Zeey bata da laifi ta sani amma wanan dalilin ya jawo mata tsanar yarinyar ba gara ba dalili taji yarinyar ta fita mata rai ga baki daya ta wanan dalilin.
A dakin mu hjy ta samu ta lalabe ina kwance lamo sai faman ajiyan zuciya nakeyi ga tunanen abinda ya faru tsakanin mu yaki fita a rai.
Duk motsi nayi sai inga kamar a lokacin abin ke faruwa dani uwa uba ga kamshin turaren jikin shi daya dameni a hancina yana kokarin saukar min da kasala a jikina.
Mikewa nayi zubur hjy dake zaune ta kalloni tare da fadin ina zaki ban daki zan shiga inyi fitsari na fada.
Na shiga ta bini da kallon tausayi tana gyada kai Allah kadai yasan yadda take ji a zuciyar ta kan yaranan a yanzu.
Na dan jima a ciki kafin in fito rike da digana dana cire ina daure da tawul a jikina wanda nake kewayawa dashi don a dakin muka same shi wani babba haka dashi fari mai kyau da yan flawer a jikin shi kanana a gefe.
Dogon rigar yar katin da anty safiya ta saya min da zanzo gidan mami na jawo na zauna saman kujera ina dan shafawa jikina mai don kada in bushe.
Au yar nan wanka kikayi gabanin magariban nan kudai yaran yanzu baku da tadan lokacin yin abu.
Hjy na magana tana kallon gashina da har lokacin yana tuke babu kitso a kaina sai fibon dana daure gashin dashi ta bayan kaina.
Kafin ta mayar da kallonta da kyau a inda nake tanaci gaba da fadin yadda kike nan da tsari irin hakane mutanen boye ke so su shige jikin mutum a sauke.
Mutanen boye kuma hjy na fada ina juyowa gareta tace kwarai kuwa yar nan ai su abinda sukw so ke nan urin wanan sakacin da kukeyi a yanzu take sun shigeka suyi maka illa.
Kinga mu a zamanin mu duk irin wa yan nan abubuwan musanshi iyayyen mu na fada muna mukiyaye don tsaron lafiyan mu.
Hjy daga yau na daina ba zan sake kewaya a wanan lokacin ba in Allah ya yarda tace dadai yafi maki kam.
Waini meya hadaki da mutumin naki ne dazun kike ta wanan kuka ina saka riga a jikina da sauri don maganan da tayi naji wanan maganan.
Juyowa nayi da a daidai ina karasa saka rigan na dauki hulan dana dora saman gado na dawo kusa da ita na zauna tare da dan marairaicewa nace hjy ki taimake ni ya jafar yafita daga tsabgata a gidan nan don Allah idan ba haka ba mami zata koreni ta fada.
Kin taba ganin inda aka cirewa mutum rai ga abinda yake so farat daya wanab sai uwarku da take ganin tana iya hakan.
Wai yau dai ki fada min yar nan shin kina son jafarin nan ko bakya son shi inji da sauri na dago kai na kalli tsohuwar sai kuma na dukar da kaina kasa don bansan amsan da zan bata ba.
Ince ina son sa in kaishi ina ko ince banson jinin ta kiri kiri haka a gabanta anya zataci gaba da sona nima duk da nasan tun kan haduwan mu da jafar din tsohuwar take nuna min kauna sahihi.
Sai kuma yanzu da take nuna min kauna tankar itace ta haifi iyayyena ta san zafina fiye da kowa ta yaya zan iya bude baki ince banson jikanta mafi soyuwa a gareta ido da ido haka.
Nasan wani abu yanzu ma saboda shine ta tsaya min take tsare min komai a gidan yadda ya dace.
Murmushi naji tayi tana fadin to ai abu yayi kyau takwara shiya nake kara sonki saboda halin nan naki na alkunya ga kuma girmama mutum saidai iyami taki gane hakan .
Ke din wani baiwace a garesu takwara naso iyami ta gane hakan amma idonta ya rufe ta kasa hangon hakan da kanta.
Nidai har ta gama maganan daidai ana kiran magariba ga agogon dake dakin namu ta mike da sauri zuwa bandaki do bata wasa da ibanda ta kiran sallah kawai ta kan jira ta mike ko wani lokaci.
Bayan kowa ya kammala komai aka fito cin abincin dare kamar yadda aka saba da kyat hjy ta shawo kaina na yarda na fito daga dakin.
Mun samu mami a falon har ta fito tana zaune tunda muka tun karo wurin ta dago kallo daya tayi min ta kawar da idon ta gareni tana fadin hjy kin fito yanzu nake zancen ko lafiya yau baki fito da wuri ba haka.
Muna daki nida mutumiyar ina bata labari mutanen da can yadda suke rayuwan su ga wuri hjy ki zauna tana fadawa mahaifiyar nata cikin girmamawa gareta.
Kafin ta dago kai inda nake tana fadin cikin bada umurni ke jeki aka hijabi a jikin ki baki ganin gidan nan akwai samari ne kike fitow haka dake.
Ya ilahi nikan ko me zanyi mami a yanzu bata ganin haske na na juya naji hjy na fadin zancen banza ke nan yo ai shigarta yafi naki dana yarki mutuntuwa bakiwa wanan mai zama kamar arniya a gida ba haka kai babu hula ko dan kwali sai wanan da jikkn ta yake a suturce.
Hjy mu muharamin si ne ita fa irin shigar da ta dauko yi ke nan har yaro nan ya jefa kanshi a tarkon ta.
Ita yar nan din tasan ta danawa wani tarko da ace hakan take da baki fada ba da bakinki yanzu don da kin gane kabewa ruwane.
Tsohuwar ta juyo gareni tana fadi jeki ki saka hijabin ki dawo muci abinci nikan ina shiga dakin ban kara fitowa ba na neme wuri na kwanta ina sharan kwalla.
Abuja ba kaduna bane don ko sunan uguwanin su ban gama sani ba sabanin kaduna da tun ban shigo shi ba nake jin sunaye unguwanin cikin shi a bakunan mutanen kauyen mu.
Ina barin wurin mami ta mike ta nufi dakin dan lelen ta a karo na farko tun dawowa shi Nigeria don ba dabi,an ta bane zagaya dakin samari nata.
Kofan dakin yana rufe ta murda taji shi a ruwa saidai karan tv dake aiki ana wasan kwallo tana dan iya jiyo hayaniya daga inda take tsaye.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.