Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 132 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ZAINAB IDRIS MAKAWA IDRIS MAKAWAZAINAB IDRIS MAKAWAZAINAB IDRIS MAKAWAASSALAMU ALAIKUM YAR UWA ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA ALLAHUMA AMIN ALLAH YA TAIMAKI MUSULMI A DUK INDA YAKE AMIN YA ALLAH, , , ,
Yanzu sai kuma zaman namu ya dan sauya don wanan kalman daya furta min din sai nake ganin ai
kawai a yanzu na haramta a gare shi .
Zuwa wurin shi din bai zama wajibi a gareni ba kada muzo mu aikata wani zunubi a hakan do gashi yanzun da dabi,an son rugumeni a jikin shi ko yaushe .
Wanda hakan nakewa tsoro tunda ban san matsayina a zuciyar shi ba kamar yadda malam din yayi min bayani.
Don haka a yanzu ya zama dole a gareni na nisanta kaina dashi don ina ganin rashin dacewan hakan a garemu baki daya gujewa afkawa ga fushin ubangiji a kan mu.
Gashi a yanzu duk wani laifi nasa dake zuciyana a baya na daina ganin hakan illa zalla tausayin shi dake cikin raina a yanzu.
Ba komai nakewa tausayin ba na farko dai ko dadin bakin mazane da yaimin daya nuna shima kamshi baisan lokacin daya fara wanan harkan ba.
Haka zalika badon kudi yake irin rayuwan ba kawai dai don giyar kurciyane dake diban mutum a ganuwan kurciyar sa.
Malam kuma ya fada min cewa akwai asiri a kanshin tunda kurciya akaso ya lalace saidai da yake a lokacin mahaifin su yana nan bai zauna hakana ba yasa asirin a lokacin baiyi tasiri a kanshi ba.
Amma yanzu da uwar suce kawai wace tafi maida hankali ga aiki da neman duniya kawai bata da lokacin tambaya da neman taimako akan zuri,anta a yanzu.
Sai uwa uba irin nuna min da yayi shi a yanzu ko ance ba auren mu don irin dadewan da mukayi da taimakon dana bashi baiga wata macen da zai kara zama da ita da sunan aure ba a duniyan nan bayan ni.
Wanan hujojin yasa na hauna zauna a kai ina jin tausayin mu a zuciyana don yanzu in ma haushine nafi jin haushin mami fiye dashi don ganin da nake kamar ita duk munanan halaiyar sgi ba dame ta ba ita.
Bata dauki hakan abin kyama a gareta ba kodan rayuwan turai da tayi ta saba da ganin hakan har yasa take daukan abinda karamin zunubi a wurinta oho ?
Idan nace bata damu ba ba laifi bane duba ga yadda wasu mata a yanzu suka ba aikin su muhinmanci sama ga zama su ba yayan su tarbiya da kansu inganttace .
Nasan wasu na da lokacin hakan saidai kosu ba yadda ya dace din bane akeyi a yanzu don ya zama dole a gareki ke uwa kisan a ina kike barin yayan ki idan zaki fita koda kuwa ba wuein aiki bane a yanzu.
Cusawa yaro tsoron Allah tun yana karami a zuciya da irin azabobin da Allah ya shimfida ga wanda ke masa sabo.
Wanan idan uwa tana hakan yana kawo yaro ya tashi da tsoro a cikin zuciyar shi sabanin wasu uwayen na yanzu da yaro zai ga abin asha a tv yana kwakwayo uwaye su zauna suna dariya ga abinda yaron ke koyo na bata tarbiyan shi.
Zama da dan ki walau namiji ko mace kuna hiran abokan sa tanan zaki fahinci dawa danki ke mu,amula a bayan ki.
Yawan dafa kai ko a cikin wasa kina sakawa dankin albarka tare da adduan kariya yana sa yaro ya kara imani yaji tsoro da tausayin ki ke uwa azuciyar shi koda bayan kine kalan irin yabon da kike masa zai tuna ya fasa aikata wani abin.
Idan kinga da ko yar wata ta lalace bakin ki ya saba da fadin ubangiji Allah ya shirya muna ku kiyi shi a cikin jam,i kada a zauna dake ana gulman dan wani dan sheri jifane dawo kan maishi yakeyi komai dadewa ubangiji ka bamu ikon gyara halayen mu da zurian mu Amin.
Naga abinda nakeyi tsab na shirya kamar yadda na saba samun shi a dakinshi in mashi ina kwana idan yana bukatan wani taimako nayi mai a gurguje in fito.
Yau ma hakan nayi na nufi dakin sai kamshin oud din jikina ke tashi duk inda nabi don a cikin gida nake nakan shafa abina son raina don gasu nan aje kala da kala a dakin wani ma ban taba amfani dashi ba.
Da sallama a bakina na shiga dakin nasa zaune na hangoshi saman gado ya mike kafafun shi ya harde su a wuri daya tare da hade hannayen shi suma ya saka a tsakiyan cinyar shi yana aikin tunane.
Kallo daya za kai mai ka gane yana a cikin wani yanayi na damuwa a lokacin duk gaba daya ya fita a hayacin shi a yanzu.
Kai ya dago a hankali yana kallon kofan tare da amsa min sallaman ya mayar da idon shi kasa wurin kafafun shi yana kallo.
Ina kwana yaya na fada tare da jan in tsaya daga dan abin zaman bakin gado da ake ajewa a yanzu gaban gadajen kasan waje a yanzu.
Ba tare da ya amsa min ba Kai ya sake dagowa a hankali ya kalleni da kyau kafin inga ya dan sake murmushi a fuskan shi can kuma ya girgizan kan nasa a hankali.
Zainab na gane yanzu guduna kikeyi bakya kaunan zama a kusa dani ko kadan a yanzu ko kema kin koma kyama nane a yanzu abinda bakiyi min ba lokacin da nake cikin aikata sabon da nayi a baya.
Ko kuwa har yanzu kina zargina a rankine akan ban daina abubuwan da nayi a baya bane a yanzu ?
Idona kura mai a inda nake tsaye ina kallon shi tare da sauraren abinda yake fadi a lokacin har sai daya dakata na dan gyara tsayuwana ina fadin.
Ba haka bane yaya ina gudun mu fadawa fushin Allah ne ga hakan tunda kayi wanan furcin a gareni nake tsoro da taka tsantsan a zaman mu yanzu.
Me zaisa na gujeka a da can ban guje maka ba balle yanzu da nasan kafi bukatan a zauna dakai zan fara gudun ka kuma ?
Laifi Allah kawai ai yaya yanzu tsakanin kane da ubangijin ka kanemi gafara a aurin shi mu kuma na tare dakai mu taya ka.
Murmushin da yanzu ya kara zama dabi,an shi ko yanzu shiya sake min din don abindana fada a lokacin gefen shi ya dan bubuga alaman in zauna a wurin.
Kallon wurin nayi kamar mai nazari kafin nayi ajiyan zuciya na kai zaune a hankali kamar mai tsoron hakan.
Zamana dan shiru dakin yayi kafin yace dani banyi tsamanin za a samu matsala a kan zaman namu ba a yanzu sai dai shi tambaya yana da amfani don yanzu ban kaunan wani abu da zanyu wanda zan sabawa ubangjji na a yanzu.
Wanan yasa nake son nayi tambaya akai dan kada muzo mu tabka sabon Allah kema in jefaki a cikin fushin ubangiji.
Ni kaina zainab nasan na cuta maki na tauye maki hakkin ki daya rataya a kaina kuma kikayi hakkuri ga hakan bawai don abin hannu yasa kikai hakkurin zama dani di ba a a .
A yanzu na kara fahintar kawai dai Allah yayo ki mai tausayine da jin kai na tare da ita tun a zamanin zaman ki gidan mami na fara fahintar haka.
Saidai ban gaskantan hakan ba sai zamana dake a yanzu na kara fahintar hakan akanki any way anjima ki shirya zamu fita sha biyu zuwa gidan mami akwai malamin da za a kira jan matsalan namu a can yau.
Gabana ne naji ya fadi lokaci guda har yakai ba dan dago da sauri ina kallon shi ido ya dan lumshe tare da kada min kai alaman eh.
Nayi karfin halin fadin Allah ya kaimu a sanyayye ko dan ya kawar da zancen ne a lokacin ya jefo min tambaya da maganin nawa ya kare ke nan naga kin daina ban.
Ajiyan zuciya na sauke tare da fadin iya adadin da akace ayi amfani dashi ke nan na fada ba tare dana dago kaina ba.
Hjy fa ta fito yau kuwa ya sake jefo min tambaya nace yau banji motsin ta a falo ba ta fito ba tukun na dai je mun gaisa da ita dazun tana lafiya.
Yunkurawa yayi yana fadin muje dakin don da ita zamu tafi gidan mami din an jima ya fada yana tashi zaune kafin ya mike nabishi da kallo.
Kada kiji wani abu zata kai masu ziyarane ita ba abinda zai kaimu zai kaita ba ya fada yana tsaye.
Ban bishi dakin hjy dakina na wuce ina tunane kafin na kira layin inna na labarta mata abinda ke faru sama sama.
Sai ji hankalin ta ya tashi lokacin kuma nayi dana sanin sanar da inna din duk da ban fito fili na fada mata ga dalili ba amma sai ta rude .
Har na dan fara zargin iyayyena a raina ina fadi cikin zuciyana wai ko sun damu da damuwana kuwa ?
Sai nake ganin kamar dan abin duniyan da ya jafar ke basu akai akai yasa basu ganin laifin shi a kan komai .
Saida abinda ban sani a lokacin shine komai munin aure ga diya babu uwa ko uban da zasu so auren yarsu ya kare sai in hakan mukaddari a wurin Allah dama akai rabuwa a cikin auren .
Sai dai kuruciya ya hana in gane hakan a lokacin nake ganin laifin iyayyena kan son na zauna gidan jafar don abin duniya da ya rufe masu ido a lokacin.
Kafin sha biyu har na shirya shi kawai nake jiran fitowan shi don bani da kwanciyan hankali a lokacin son har na fara yanke hukuncin abinda zanyi idan na bar gidan nasa don kada rayuwana dana iyayyena ya wahala gaba.
Sai gashi ya shigo dakin nawa a cikin shirin shi yasa wasu shadda masu ruwan sky clour dinkin su ya tsaya masa iya gwiwan shi hannun rigan karami shima iya gwiwan hannu ya tsaya mashi sai kamshi ture ke tashi a jikin ranan har yar hula baka mai kyau ya saka a kanshi sai hakan ya kara fito mashi da kyawon shi fili duk da ya rame a lokacin.
A falo muka samu hjy zaune tana jiran mu yake fadin lalai hjy kina jin fita yau din nan har kin rigamu fitowa ke nan suka dan taba wasan jika da kaka kafin mu fita daga gidan.
A gida nabar sadiya don tace bazata gidan mami ba ita dataji can zamu tafi duk da fadila nasan tasan komai dake faruwa a gidan sabanin sauran yan aikin da basu san abinda ke faruwa ba sai aikin gaban su da sukeyi.
Amma ita kan nasan ta san komai dake faruwa a lokacin nuna kawai take bata sani ba nima kuma ban mata wanan maganan ba sam.
Ko lokacin da muka fito zamu fita din dagani akwai magana a bakin ta saida babu idon yin maganan ne a gareni balle ta tambayi abinda take son ji din.
Mota daya mukai amfani dashi zuwa gidan mami din shine gaba zaune da driver muna baya nida hjy.
Dan tafiya muka shigo unguwar su mami din ban dago kaina ba daga yadda nake zaune a bayan mota nayi tagumi sai faman sake saken da nakeyi a cikin raina .
Tsayawan motan yasa na dago kai ina kallon get din gidan da maigadi ya bude a lokacin a raina nace kila zuwan karshe kenan da zanyiwa gidan nan a hankali na mayar da idona na rufe har muka karasa shiga cikin gidan.
Muryan jalal yasani bude ido don jin yana fadin a, a bros kune tafe ashe gara da ban fita ashe tun dazun ya fada yana karasowa bakin motan.
Ganin hjy yasa ya koma kanta yana janta da ba,a har dai muka shiga cikin gidan yana wani ja mata hannu suna tafiya a hankali ina bayan su nima tare da yaya dake waya daga gefena.
Gaba dayan su kowa na falon zaune kasancewa ranan ba aiki duk suna gida ga baki dayan su har mami tana falon tare dasu.
Sallaman suka amsa na jalal amma sai idon su ya dawo a kaina sun kasa boye kyashin su a zukatan su a kaina.
Gaida hjy sukeyi da yayan su sai Na,imace take ce min zainab sannu da zuwa na danyi murmushi ina amsa mata a cikin dan fara, a har take fadin ga wuri kizo ki zauna tana kokarin tashi ta ban wuri.
Da sauri nace a,a anty ki barshi in zauna a nan na nuna kasa yace No cikin dakewa ya kalli Rufaida yace ke bata wuri ta zauna.
Saida tayi wani iri kafin ta mike a cikin fushi zata bar falon mami tace keko tsiyana dake ke nan wallahi saurin fushi Rufaida.
Tace to mami sai kuma tayi shiru ta kasa karasawa don wani irin kallo daya watsa mata yasa tayi shiru.
Dole ta dawo ta zauna a gefen mami din tana wani irin shagwaba mami tace kedai zuciyar nan naki zata wahal dake wallahi .
Ni kan zaune nakai a bina duk ina kule dasu irun yadda kowan su ke satan kallona tundaga kafa zuwa samana.
Na fara gaida mami bayan na zauna ta dan juyo da dan fushin fadan da takewa Rufaida ta amsa min tare da fadin ya gidan ya dawainiya da hjy.
Nayi dan murmushi na gyara zama bayan haka ba wace muka gaisa da ita a cikkn in bayan Na,ima da tun shigowan mu tayi min magana.
Sai suka wayen ce hakan da hira da hjy na nuna ban masan suna hakan ba gareni ina dakalan wayata daya dauke masu kuma hankali ga ganin ta.
Jamal ya shigo shima da alama baisan da zuwan mu ba sai lokacin suka gaisa da dan uwan shi nice na fara gaidashi yake fadin.
Zainab kun sha Nageria fa nasan ba don ciwon yaya ba da yanzun kun koma ai jalal ya karba a bayan shi daga inda yake tsaye.
Me zaisa ta damu ta koma tunda ba karatu takeyi ba yanzu Aisha da tun shigowan mu batayi magana ba ta fada a yanzu.
Ke lokacin da aka dawo kasan nan ai kuka keyi zafi ya isheki zaki koma jalal ya fada budan bakin ta sai cewa tayi aini a lokacin na tashi cikin jin dadi na sai kawai a daukoni a kawoni nan.
Amma kuma a yanzu kinsan zainab ta fiki samun dadin da kike fadin kin samuba can don haka ai ba abin mamaki bane don tace zaman Nigeria ya ishe ta a yanzu.
Wani tabe baki tayi tana kawar da kai gareshi bata ji dadi amsan daya bata ba daga inda mami take zaune tace koma dai meye a yanzu ba zaka taba hada Aisha da zainab ba ko ku ke nan kullun cikin gwatsale yar uwan ku a gaban kowa.
Look ba nazo nan da mata na bane don a riga challangen din ta haka koma meye a yanzu zainab zamana takeyi bana son jin wani zancen bataci a gareta again.
Falon yayi shiru kafin hjy tace dasu banda abinku ai ka zama matar mai hali yafi ace ai yar me halice ke a wanan zamanin.
Kafin wani yayi wani magaba akai sallama aka shigo ya mamud ne a gaba sai wani mutum mai cikar kamala a bayan shi suka shigo.
Nan aka shiga gaidashi sai lokacin na gane shine wanda zai warwale matsalan zaman mu da yaya din da mukazowa jin abinda hukuncin ya tanadar muna yanzu.
An dan taba hira kafin su mazan su fita su barmu a falon kamad kada yaya ya fita duk sai naji na tsawala a lokacin cikin su sai dai da yake hjy na wurin ba halin wani yai min wani maganan banza.
An dan dauki lokaci kafin yaya mamud ya shigo yana fadin zainab dan zo mijin ki na magana dake a waje.
Duk suka bishi da kallo ya fita na dan daga nabi bayan shi nima nasan kallona sukeyi a lokacin ba mamakin hakan a garesu.
A can na tsinkaye su zaune saman fararen kujerun roba su hudu na isa wurin da sallama a bakina suka amsa min.
Kusan a tare suke nuna min wuri in zauna na danja kafa a hankali nakai zaune a takure nake cikin su din kafin naji mutumin ya fara jan dogon addua tare da godiya ga Allah daya hadamu a wanan wurin.
Kafin yace ina gida zaune dazun malam gashi ya nuna ya mamud ya sameni da wani zance wanda ya daure maku kai .
Sai dai Alhamdullahi don addinin islama yazo da wayen kaine ga al,umman Annabi ga baki daya Annabin rahama bai bar duniyan nan ba saida ya warware muna irin matsalolin nan idan zun taso gare mu.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.