Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 49 of 139

Yan iya magana sunce kafin kaga biri biri shiya dade da hango ka tundaga nesa karfe goman safe dirka dirkan motoci uku suka tsaya a kofan gidan da muka baro zuwa kaduna yau da safe, a daidai lokacin da mu ke kan hanyar anchau zuwa garin mu.
Su shiddane tafe mutum.bibiyu a mota dayasuke tafe saida suka karewa gidan kallon mamaki dan girman shi da tsaruwan shi kafin su nufi hanyan shiga daga ciki.
Masu tsaron gidan ne suka dakatar dasu da tambaya wurin wa suka zo kallo rainin wayau hjy saudat tayiwa security din tana fadin zai bude kofa su shigo ko sai ranshi ya gama baci yasan kosu suwaye da zai tsaya tambayan su suda gidan dan su.
Yana tsaye ko wace ta fito da abinda take fada mai a lokacin saidai ya kallesu kawai bai iya furta komai garesu ba.
Yasan mami don suna haduwa a can gidan da wani lokaci yasa mami karasowa wurin da kanta gaisuwan girma yaiwa mami din tare da nuna sanaya a gareta.
Tambayan shi tayi da fadin ko grandma da wanan yarinyar da ogan su ya kawo suna cikin gidan nan ?
Da sauri ya girgiza kai tare da fadin babi kowa a gidan su kadai ne a ciki ko zan iya shiga in gani da idona mami ta fada.
Kofa ya nuna tare da dan dukar da kanshi alaman girmamawa a gareta ta nufi kofan sauran dake mara mata baya suka bi bayanta zuwa cikin gidan.
Bin ko ina na gidan da kallo sukeyi komai na gidan abin kallone don ya tsaru iya tsaruwa dai a kasan nan ba karya a cikin sa.
Saida suka gama duba ko ina na gidan guide din na tsaye daga kofa ya rufe fuskan shi da madubin ido baki fuska babu sauki a gareshi.
Da hannu mami ta yafutu wanda ke tsaye a kofa kamar an dasa shi a gurin yazo da saurin shi cikin girmamawa gaban mami din.
Are you sure grany bata gidan nan ko ta zauna tare da wata farar yarinya haka kai ya girgiza yana fadin baiga kowa ba a gidan nan yana fadi yasa kai ya bar gurin ya koma inda ya fito da farko yaja ya tsaya ba tare daya kara kulasu ba.
Yaran nan me suka mayar dani mami ta fada a hasale ta soma tafiya sauran suka mara mata baya suka bar gidan cike da takaici a ransu.
Duk da mami bawai ta saba da ciwa mutane mutunci bane a yau kan data sameni a gidan nan da tayi min cin mutunci ta uwa ta uba don ta kula ba karya mutane ke fadi ba na asirce mata dane da saddabarun mu na yan kauye.
Don wai ba a sako mu daga gidajen a banza kafin mu bargida sai anshirya mu da asiri idon mu idon mazan wasu da yayan su kamar yadda ya faru a tsakanina da ya Jafar din yanzu.
Duk abinda hjy maria ke fadi a gefenta mami bata samu bakin bata amsa ba a lokacin don burin mami ranan shine ta same tayi min koran kare tsakani na da danta.
Inyaso daga baya sai ta nemi shiri da hjyn su su shirya a tsakanin su sai gashi tazo ta samu gaba daya ma yadda ta samu labari mun rigada mun bar gidan a lokacin.
Gida ta dawo bayan ta sallami kawayen nata na birni da yanzu suke manne da ita koda yaushe suna kara sakata shagalta da duniya .
Dakin ta nufa kai tsaye don ta samu natsuwa a yadda take jin kanta magani ta fara sha kafin tabi lafiyan gado ta kai kwance.
A daidai lokacin da barci ke shirin daukanta ne wayan ta yake ruri a jakka har ya katse bata daga ba .
Wani kirane ya sake shigowa again da tsuki a bakin ta takai hannu tana daukan wayan dake cikin jakkan tare da duban screen din wayan nata taga sunan mama Ramatun tace ke kiranta.
Ramatu ta fada a fili tana dauko wayan zuwa kunnen ta tayi sallama tare da gaida ita da kwana.
Sama sama ta amsa mata gaisuwan mama Ramatu ke fadin sai ga hjy ta dawo yanzu wai ashe tana kaduna duk wanan neman da ake mata haka.
Kaduna fa mami ta fada da mamaki kafin tace kaduna gidan wa ke nan wallahi wai ashe tana gidan hjy Tantano duk wanan neman da ake mata.
Wani ajiyan zuciya mami ta sauke kafin tace da wanan yarinyar suke ke nan ko ?
Wace yarjnyar Ramatu ta tambaya kafin tace au nagane ba tare suke ba gaskiya ita kadaice da kayan ta yanzu aka sauketa gida masu shi basu ko zauna ba wai suna saurine.
Guntun murmushi mami ta sake a fuskan ta tare da ajiyan zuciya tace Ramatu yanzun na yarda da ake fadin jika yafi da dadi wallahi wanan abinda hjy tayi min akan yaran nan.
Anywhere zan kira in an jima ki ban hjy din muyi magana tunda yanzu nasan mutanene a tare da ita ina fatan dai baki bari kowa yasan da wanan zancen ai.
Haba dai antyn mu tayaya zan dabawa cikina yuka da kaina kan wanan magana ai wanan ba abin bari na waje yaji bane ace hjy tayi fushi dake tabar maki gida har baki san inda take ba tsawon kwanaki haka.
Bari kedai Ramatu ko wa yan nan dake tare dani ai ban bari sun fahinci yaya kan zancen yake ba sam kinga min yar iskan yarinya zata ja a bagani a bangon jaridan kasan nan don tsiya.
Dariya mama Ramatu ta kwashe dashi tana fadin ai sai dai kada a kara amma wanan yarinyar ta rigada ta cuci mu saidai kawai a dauki mataki don gaba kuma.
Mataki kan kamar na dauka Ramatu don gaba dayab su saina nuna masu kuren su har shi jafar din ina binshi a sannu ne yanzu in samu akaiga auren nan shi da yar gurin saudat.
Har yanzu zancen yana nan ke nan da kawai ki barshi ai daga baya zao gane irin gatan da kike so kimai idan yaga matsiyatan daya jawo a jikin shi suna batun rufeshi da bani bani.
Barni da mara hankali mami ta fada tana maijin zafi a zuciyar ta kan abinda yar uwanta ta fada yanzu.
Bayan ta kashe wayan idanunta ya dade a runtse tana tunane kafin ta mike zubur kamar ta tuna da wani abu a lokacin.
Ficewata da dan sauri zuwa part din dan nata jafar har tana hada kafa a wurin sauri lokaci guda .
Tayi sa,a tana murda kofan taji shi a bude bata tsaya jiran wani abu ba ta afka ciki part din kai tsaye da sallama.
Yana zaune saman kujera sai farar takarda dake nade a hannun shi ya duka yana zukan farin garin dake saman dayan farar takardan dake aje saman table.
Wani irin ja tayi baya kamar zata fadi lokaci guda kuma tabi bangon dakin tana dafa a habkali don yai mata makari daga inda take tsaye.
Saida ta dafa bango ta samu numfashita ya dan daidaita ta samu fadin Jafar sai kuma idon ta ya sauka akan wasu tarin kwayoyin dake watse a gefen shi.
Da wani irin rawan jiki mami ta ke nunashi da yatsan hannunta tana fadin Jafar yaushe ka fara wanan halin ban sani ba ?
Yadda take maganan kamar wacce ke gudun wani yaji abinda take fadi din a lokacin a hankali ya dago kai ya kalli mahaifiyar nasa yana fadin .
Mami kiyi hakkuri bansan zaki shigo a yanzu ba har na kai ga shan abinda zai kwantar minda hankali.
Idan naci gaba da zama haka ban samu abinda zai taimakawa kwakwalwata ba zan samu matsala sosai shiyasa na sha wanan a yanzu don ya dauke mi ragamar hankalina na dan lokaci zuwa yanzu.
Don ba zan iya jure ji da gajin yadda kike kokarin hanani abinda nakeso a rayuwana ba mami sai kuma ya mika mata hannu alaman dai ya fara fita hayaci shi a lokaci.
Kamar wawiya haka mami ta koma lokaci guda do haka tabi hannun nasa daya miko mata zuwa gare shi.
Don bata son ko cikin diyan ta wani ya riskeshi a wanan halin da ita ta riski dan nata a ciki.
A hannu kuera ta zauna ta tsura mai idanu yayin da nasa idanuwan suke kamar a lumshe duk da tasa ba barci yayi ba a lokacin.
Kanshi ta dauka zuwa cinyanta ta fara shafa a hankali take hawaye wani na bin wani suka fara sintiri a idanun ta lokaci guda.
Babu abinda ya fado mata a rai sai irin wasoncin daahaifi su yabar mata kafin bari shi duniya akan ta kula mai da tarbiyan diyan shi kamar yadda sharia ya sharadawa musulmai.
Mami hawaye wasu nabin wasu ta kasa controling din su tuni kanta gaba daya har jikin ta ya dauki canji lokaci guda ta rasa wani duniya take ciki a lokacin.
Wai yau jafar dinta ne haka dumu dumu ta kama shi yana wana dabia da tafi kyamata ga diyanta.
Ta rasa meke mata dadi a ranta gashi tana son fita ta koma dakinta ko zata samu ta fasa hawayen ta su samu zuba kasa ko zataji sanyin abinda takeji a ranta.
Gashi kuma tana tsoron fita a lokacin kada wani ya shigo part din bayanta ya same shi a wana halin ko kuma ganta a cikin wanan yanayin da take yanzu a tambaye ta dalili.
Asalima idan son samune daga ita sai shi idan ya farfado ta samu ta gargade shin sosai kan hakan don ya tsira da mutuncin shi a idon jama, a.
Jin mami ta zurfafa ga tunanen da takeyi ne yasa shi dan dago kai ya kalle ta a hankali ya ke fadin go back to your room mami.
Idan na tashi za shigo muyi magana dake anjima murya cikin rada mami ta sake fadin zan koma amma sai ka ban duk wanan abinda kake sha yanzu na fita dasu dakin nan hankalina zai kwanta.
Murmushi yayi yana dan mikewa daga zaune tare da fadin kiyi hakkuri mami nasan na bata maki saidai nima din ba hakan naso ba dani.
Nasani jafar yarinyar nan ta cuceni ta gama min da rayuwa jafar a sanadin ta yau jafar har shaye shaye ka koma yi haka.
Cikin wani iri kuzari ya dago yana kallonta fuska daure kafi yace mami idan ma cutane ai yarinyar aka cuta tunda ita zata zauna da mashayi irina yanzu.
Wani irin sauti gaba mami ya bada lokaci don ji abinda yake fada a cikin maye jiki babu karfi ta mike tare da aza kanshi saman filo tana fadin .
Ka kwanta da wanan shirmen da kakewa mutane a yanzu yanzun ba lokacin maganan komai bane.
Murya kasa kasa irin na wanda baya cikin hankalin shi a lokacin kamar mai shiri barci yace iam telling you mami itace muka zalinta, , , ,

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.