Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 133 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWAASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI FATAN ANTASHI LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA MARASA LAFIYA ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYAN ALLAH YA KARA MASU LAFIYA AMIN.
YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA KADA MU SHIGA HAKKIN JUNAN MU.
Zowan mami da ta biyo bayan mu ta samu muna zazaune malam na bayani hakan baisa malam din yayi shiru ba a lokacin har saida ya tsaya don kan shi.
Malam ya kare bayanin shi a lokacin jikin kowa yayi sanyi a wurin don irin bayanin dayayi a lokacin kan addinin Allah.
Ya dago tare da fadin kada in katse ku da bayani haka zan so wanda suke da alhakin zaman mu wanan wuri suyi min bayanin komai a tsare yadda zan fahinci zancen.
Sai lokacin mami ta samu bakin magana tana fadin akan meye akai wanan zaman ya mamud ne ya bata amsa da fadin kan matsalan matsayin auren su da kika fara magana ranan muke son malam ya warware muna.
Sai ta dan bimu da wani irin lalattacen kallo tana kawar da kanta gefe daya ba tare datayi magana ba a lokacin.
Sai ya mamud yayi sauri fadin dama watau malam kamar yadda na fada ma dan matsalane aka samu tun farkon auren har yakai an kwashi tsawon shekarun nan, ana zaune ba wani abinda ya taba shiga tsakanin su shiyasa muke son a warware muna matsayin wanan auren a yanzu.
Saboda mahaifiyan mu ta fara furta wanan kalamin wai an dade an dauki lokaci a yanzu kan ba sauran aure a tsakanin su.
Da sauri mami ta dan dago kai ta kalli ya mamud din tana fadin au don hakan dana furta kuka kira malam a kanshi to ai gaskiya na fada dan aure ko watani masu tsawo ya diba ba saduwa a tsakani ai akwai bincike a kai.
Malam din cikin murmushi ya karkada kai ba tare dayayi magana ba sai murmushin da yakeyi a lokacin.
Ya jafar yace dakata mamud jin haka kowa yayi shiru a wurin a lokacin ina faman tunanen zancen ya mamud din da yace mami ne tazo da wanan zancen ke nan haka na nufin mami dai har yanzu tana son in bar mata danta kota halin kaka ke nan yasa take wasu tsire tsire zance a yanzu din.
Sai gashi kuma yanzun din ma ta kara maimaita hakan a gaban kowa ba tare da jin komai ba a zuciyan ta.
Wani dan iska ya furzo mai cike da sautin zafi da takaici irin yadda yake jin kanshi din a lokacin nan dai ya bude bakin shi da yai mashi nauyi a lokacin kafin ya fara fadin .
Watau malam bayanin da zan ma ba akan wanan zaman bane kawai kamar yadda dan uwana daya gaiyace ka yayi maka bayani a yanzu.
Duk kallon shi mukayi kafin yaci gaba da fadin malam ni din dai na kasance mai aikata sabo a baya, da sauri malam yace wa,iyazu billah.
Yace kwarai malam a kuma cikin irin wanan halin na auri matata zainab gata nan zaune a gaban kowa .
wanda da farko nayi wanan auren ne don in fake a gareta da sunan aure a kaina ga idon mutane don kowa ya san ina da aure kada mutane su kawo wani zargi a gareni.
Duk kallon shi sukeyi har ni din da yanzu na kara gaskanta manufarshi a kaina a baya daya aureni din sai naji wani irin bakin ciki ya kara tokare min makoshina lokaci guda kafin sauti muryan shi ya dawo dani a daidai lokacin da yaci gaba da fadin.
Watau malam bayan auren namu da ita hakan baisa na bar aikata fasadi a doron kasa ba wai don ina da mata sai na dauki abin kamar yadda na tsara zaizo min a baya yadda nake so
A gaskiya na auri zainab ne akan zan samu rufin asirina a wurinta don tana yar tallakawa zata zauna dani ko don talaucin ta dana iyayyenta alokacin a yadda nake hange.
Saidai kuma nima ba wai haka kawai wanan tunanen yazo min ba sai bayan nayi nazarinta da irin hakkurin ta naga ya kamata in taimaka mata ta wanan hanyan kaga kenan zamu taimaki juna a takaice dani da ita amma ba cikin ta sanda hakan ba saboda tana da karancin shekaru sosai a lokacin.
A lokacin mami bata gane hakan ba don tana ganin na bijirewa zabin tane don tana ganin zainab din bata cancanceni ba ga aure.
Malam ya dago kai ya dan kalleni a hankali ya mayar da kanshi kasa yaci gaba da fadin.
Sai dai kakata da take jin ina yawan fadin zainab ce ta dace da rayuwana a lokacin duk da bata san mugun halina na boye ba da nake aikatawa a lokacin.
Amma hjyn ta bani goyon baya dari bisa dari ga wanan auren da nake son yi da zainab din.
Inda a karshe da mami din taki jin magana da shawaran mahaifiyan nata muka yanke shawara da hjyn da yayana mamud gashi a zaune kan naje na nemi auren zainab din a boye tunda mahaifiyarmu ta kafe kan sai zabin ta a lokacin.
Wanda ni kuma nake hangen zabin nata a gareni kamar wani hanyar tonon asirinane a wurin jama, a wanan auren na mami, don zai iya jawo min ga duniya don nasan koni waye.
Saidai ashe wanan zaben da nake ganin nayishi ne kawai don bukatana, shine haske a garemu baki daya .
Don shigowan zainab a cikin rayuwana a sannu a hankali ta fara kawo min sauyi na canza min lissafina da nakeyi da farko a kanta.
Kasancewan zainab din yarinya mai wayau da ilimin addini yasa abubuwa suka fara cabe min a rayuwa .
A lokacin haka nake gani don yawan nasihanta a gareni da saka min ido kawai da tayi kan duk wani abinda nakeyi ba tare da takura min ba .
Sai hakan yasa na fara kunyar kaina na da jin nauyin ta har ya kai na rage wasu abubuwan da nakeyi a fili saboda kaucewa idonta din.
Tunda nasan tasani amma bata nuna min tauye mata hakkinta da nakeyi yana damunta ko abin yana bata mata rai sai har idan ta kamani da idon tane mukan kwashi fitina sosai da ita.
Nasan kuma hakan da take min yana a cikin rashi gatan da take ganin bata dashi ko kuma fin karfi iyayyene dake aiki a kanta.
Don ga nawa tunane sai nakan yawaita yiwa iyayyenta da yan uwanta alheri don na kawar da zargi ko kaskanci a idanu su.
Nasha shawaran da zuciyana akan in rabu da ita kamar yadda mahaifiyan mu keso hakan, amma sai in kasa hakan don hankalin yarinyar da nake gani kuma gashi duk da tasan dabi,u na marasa kyau baisa ta wullakantani ba.
Ban kara tabbatar da hakan ba saida na sakasu karatu ita kanwarta da suke tare idon ta ya kare budewa a can chaina din sosai amma hakan baisa zainab ta raini ba ko naji watarana ta fadawa wani ga halaiyana marasa kyau.
Mun sha fama da zainab akan rayuwan maza da maza da nakeyi wanda take iya kokarin ta a kai taga na daina wanan akidar .
Amma sai hakan ya gagareta da farko na dauka tanayine don na kasa, kasancewa da ita a matsayun muna ma,aurata .
Sai daga baya na gane abin ba haka yake ba har kasan zuciyar ta tanayine kawai don ta fitar dani cikin wanan rayuwan na fasadi danake aikatawa.
Yan kungiyan mu sun sha ban shawara in kasheta in huta idan zata kawo min matsala a rayuwana, ko su kansu suyi yunkurin hakan in hana su.
Naji mami tace ikon Allah wai a kashe mutum kamar dan kiyashi kai haba jafar wanan wani irin rayuwa ka jefa kanka a ciki hakane ?
Lokacin na dago kai na kalle shi da idona da yake tab da hawaye bakin ciki tare da tausayin kaina da nakeji akan abubuwan da yake fadi din da bakin sa.
Malam ne ya katse shi da fadin gaskiya malam jafar ka aikata sabo mai girma a rayuwa.
Ya aikata kan sai dai addua a yanzu tunda Allah ya taimakeshi ya daina a yanzu ga baki daya.
Yanzun malam saika fada muna matsayin da auren su yake ciki a yanzu don kowa yasan zaman shi a yanzu din mami ce duk take wanan maganan tana kallon malam din.
Taci gaba da fadin don a nawa fahintar ya tsaya yana gyaran wani zance haka mai tsawo da bashi ya taramu a nan ba tun dazun.
Why mami why zakice kada na fada ya zama dole in fada a gaban kowa don in kara samun addua da taimakon da Allah zai gafarta min zunubai na jafar yace.
Kafada din ba,a hana ba kana kawo muna wani zancen zainab can tun dazun mami ta fada a hasale.
Malam dake kallon su yace Na,am watau ainihi danki yana da gaskiya haka ake son mai tuba da gaske ya kasance kada yaji kunyar fadan girman zunubin sa komai girman sa don tuba.
Haka zalika ita wanan yarinyar ya nuna inda nake yace tayi matukar kokarin azo a yabe ta kuma a sota ko dan halinta.
Don a wanan zamanin ba ko wace mace bace zaki samu da aikata hakan ta iya boye sirin mijinta a cikin ta daga ita sai shi sai Allah kadai su san da sabon da yake aikatawa haka.
Jafar ya tare malam da fadin wallahi malam abinda zai baka mamaki shine ita din zainab ta shiga ta fita a kasan chaina ta samo min maganin da a yau zan iya komawa kamar kowa.
Na,am malam yace tare da kara masha Allah yarinya kinyi kokari da kika samu wanan yabon a bakin mijin ki haka.
Wallahi malam ba gyarata nakeyi ba ko don wani ya sota a yau ina fadin gaskiyan abinda tayimin ne a rayuwa nan dai ya kora masu labarin komai har da na kakana malam da yake bashi.
Humm,umm ita zainab din duk ta iya hakan ashe ba karya ake fada ba da ake fadin yan kauye komai karantan su ka barsu inda ka gansu.
Shige shige da biye biyen malam ya kare a gidin su yau na kara gaskanta wanan maganan .
Kwarai mami in dai wanan din shine shige shige zainab ta shiga inda yafi nan din data shiga ya mamud ya fada.
Don kuwa mu zainab ta gama muna komai na rayuwa tunda ta kwato muna dan uwan mu cikin bala,i.
Rufa min baki kada in saba maka a wurin nan yanzu mami ta fada dama nasan shirin ku akan hakan yasa na biyo bayan ku inji me kuke kullawa.
To bari kuji koda malam yace akwai zama a tsakanin su aure sai na karawa jafar shi tunda nayi niyar hakan kuma zan nuna masa ni na haifeshi ba wani ba.
Enough mami enough don Allah in anyi magana kice aure zaki kara min aure zaki kara min ga abinda ya dace kimin bakiyi ba lokacin da nike bukatan taimako.
Yanzu da zainab din tayi shine kuma abin laifi ai Allah yace tashin in taimakeka baki tashi din tsaye ba a kaina ita ta tashi har yanzu tana a mai laifi a wurin ki mami ?
Me wanan yarinyar tayi maki haka mami kika tsaneta ne lokaci daya haka halarcin zainab a gareki ba kadan bane har idan ke kika haifenin da kike fadi.
Yarinyar da zan yi amai ta kwashe in fitar da kazanta da namiji dan uwana ta zauna tana gani iyaka taci kuka ta gaji ta share hawayen ta bata taba fadawa wani wanan maganan ba har yau itace kike kokarin ganin kin bakantawa mami ?
Wallahi dani kadaine danki mami da sai ince bake kika haifeni ba kila don son baki kawai na kina nuna min don yadda zainab zata zaunar dani tana min wa,azi mami kin taba min hakan ?
A matsayina na mai,aikata babban laifi irin wanan don haka mami ki gafarceni akan zainab a yanzu zan iya batawa da kowa a duniyan nan.
Zainab tayi min komai a rayuwa ta yadda ba zan iya kimanta darajan ta a zuciyana bayan naki daga ke sai zainab ne mata mafi daraja a idona har abada.
Yau zainab ta tunar dani nauyi da kunyar ubangijina da ke kaina wanda na manta dasu saboda rudin duniya da nake bi a baya.
Aiko mami zainab tayi min komai a rayuwana, kukan da nasake ne ina kaiwa kasa ya dakatar da dan rigiman daya kaure a tsakanin su lokaci daya a wurin.
Malam ka taimakeni kai mun rai ka ceci rayuwana ka rabani da ahalin mami ga baki daya a yanzu nima na gane mami ba zata taba kauna ta ba a duniyan nan.
Duk abinda yaya ya fada anyi shi har ga Allah dama wanda bai sani bai fada din ba duk anyi su a baya.
Kuma bayi don kowa ba sai don Allah da halarcin mami a gareni da kuma shi kanshi ya jafar din ya taimakeni da abinda ba zai taba barina a rayuwa na bashine illimi.
Mami ta sanadiyar ta nabar kauye rayuwa na ya inganta a sanadiyar ta haka tayi min riko na tsakani da Allah da ba zan taba mantawa da hakan ba don ita uwace hakkun har gobe a gareni.
Aurena da ya jafar shine kadai kiyayar mu da mami a fahintana don haka malam ka yake duk wani alaka na aure dake tsakanina da ya jafar a yau don Allah.
Na karasa cikin wani irin kuka ma idaga hankalin mai saurarena a lokacin duk sukai shiru suna saurarena tare da zuba min ido gaba dayan su.
For god sake mami dame wanan abin yai kama haka yarinyar nan dai kema kin sani ta dalili ki ta san bros ta kuma fadi don ki take masa komai.
Koma bata fada ba kowa ya sani don zainab yarinyace mai hankali da natsuwa ke kanki kinsha fadin haka ko a bayan ta yan aiki nawa kika canza zuwa yanzu jamal ne mai wanan maganan rai bace.
A ranan nasan tarbiyan yahudawa mami tayiwa diyan ta ashe tunda kowa na iya fadin magana kai tsaye a gareta ba tare da ta damu da hakan ba.
Don da ace hakan yai mata zafi da wata uwarce a take zata yankewa kowan su kauna a wurin yau naga amsan abinda ya dade yana min yawo a zuciyana .
Kan yadda mami bata damu tabi umurnin hjy ba idan ta tsawta mata kan wani abu da takeyi wanda bai dace ba din.
Salamu Alaikum malam ya fada cikin muryan uztazai wanan ya saka masu natsuwa a wurin malam din yaci gaba da fadin .
Wa,izu billah wanan abin bai kawo kallo ba a tsakanin ku watau anihin dai wanan zancen naku yasani nazarin abubuwa da dama a cikin yanayin zancen nan a yanzu.
Da farko na fahinci akwai wani abu da ke a kasa tsakanin ku a gidan nan tun farko sai abu na biyu shine.
Watau ainihi kan zancen wanan boyar Allah watau hjy zainab gata a zaune watau anihi hajiya iyami ina son ki san wani abu.
Shi lamarin ubangiji mai sauki ne idan bawa ya daukeshi da sauki watau wanan boyar Allah ita din haskene a gareku baki daya a gidan nan.
Haske irin wanda ake kira da Nurul dar sai ya kasance a cikin wanan zancen gaba daya kunyi amfani da baiwan yarinyar nan kun kuma amfana da ita ko.
Yanzu duk ba wanan ba don lokacin sallah ya gabato sai mu gagauta yin bayani kan abinda ya kawo mu nan a yanzu.
Na farko dai bayan nasiha da zan ma kai malam jafar akan tsoron Allah a yanzu dai Alhamdullahi sai ka ya waita istgifar wanan yafiya yana tsakanin Allah da bawan shi.
Ba wani dan Adam da ya isa ya furta wani kalami akan hakan face mu godewa Allah ga baki daya muka yawaita istigir akan mu da dukkan musulmi baki daya .
Ke kuma hjy zainab ki godewa Allah da har kika samu yabo haka gun abokan zaman ki ga baki daya ko wanan ya ishe ki alfahari a duniya.
Zancen akwai aure ko babu aure a tsakanin auren nan yanzu zabi ya rage gareka kai mai auren a hannun ka.
Idan kaga zaka bar matan ka auren ku na nan daram har abada sai dai idan kaika janye igiyan auren ta a kanka yanzu.
Aure dai an riga da an daura a tsakanin a bisa tsarin musulunci ba tare da wani manufa ba ga madaura auren ku din a lokacin kaga ke nan aure ya dauro a tsakanin ku ke nan.
Wanan zancen da ake hasashe ba addini ya fadi hakan ba tsarine na wasu mutane da suke fadab hakan.
Amma dai da ace har yanzu baka tuba ka koma ga Allah, ka daina wanan abubuwan bane to sharia ta yarda da a raba auren naku don taje gaba itama ta samu daidai da ita kada ka cuta mata a nan
Sai dai ina kira a gareku gaba dayan ku kiyayye kyautatawa iyayyen ko da a wajen tausasa harshe ga mahaifa musanman uwa .
Duk wanda yaji hakan yasan dalilin fadan hakan da malam din yayi garesu ya kara da fadin sai na karshe mu kyautatawa wanda ya kyautata muna koda na rana daya ne shima zai bukaci kyautatawan ka watarana a kan shi.
Don haka kada mu zamo masu manta alheri komai kankantanshi don kada Allah ya jarbce mu ta hanyar da bamuyi tsammani ba a rayuwa.
Da wanan nake son inyi sallama dakuba taikace Allah ya gafarta muna kurakuran mu da wanda muka sani da wanda bamu sani ba Allahuma amin.
Yayi muna sallama bayan anyi addua an shafa ya mike zai tafi ya jafar ya saka hannu a cikin aljihun shi ya ciro kudi masu yawa yace a bashi.
Da sauri malam din yace sam ba don kudi ko wani abin sadakan ku nazo ba son kunfi karfin hakan a gareni.
Zanso na gana daku ku ukun nan kafin ka bar kasan nan idan kun samu lokacin haka yayi masu sallama ya tafi.
To ai shike nan bukatan kowan ku yanzu ya biya shiyasa kuka dauko min malam khalid don shi din ya inma bakin sa yazo yai muna wa,azi.
Wa,azi kuma mami akan me zaizo yayi maki wa,azi mu mun kirashi ne yazo ya warware wanan zancen kowa yasan matsayin shi.
Please is enough a bar zancen komai a yanzu ke zainab tashi muje gida daga nan ya fada yana mikewa.
Kamar banji me yake fada ba a lokacin kaina na kasa sade ban dago daga yadda nake ba tun dazun din.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.