Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 110 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWAZAINAB IDRIS MAKAWAYAN UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA YA IBADA ALLAH YA BAMU KARFI DA LAFIYAN BAUTA MASHI BAUTA TSAKAKAKE A RAYUWAN MU ALLAHUMA AMIN
LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA SAUKIN FAHINTA BA TARE DA DAUKAN HAKKIN KOWA BA A KANKI, , , ,
DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACCOUNT 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , ,
Babu wanda yai magana da dan uwa tun fitowan mu cikin gidan mami din sai tafiya yake damu a guje a haka har muka karasa bakinn wani plaza ya juyo inda sadiya take yana fadin ya sadiya mu tsaya a sai wani abune a nan ?
Da sauri ta girgiza kai tare da yaya muje gida kwai hakan ya nuna itama din a tsorace take a lokacin da abinda ya faru.
Ya mike zuwa hanyar gidan namu horn ya danna saiga masu get sun bude da sauri don sheda horn din motan da sukayi.
Motan na tsaya nayi saurin fita daga motan na dauka shima fita zaiyi a lokacin saidai muna fita sai naga ya juya ya fita daga gidan.
Muna shiga falon fadilace ta tare tana muna sannu da dawowa na amsa take fadin ai ta dauka zamu dade ashe yanzu zamu dawo.
Eh na bata amsa dashi don ina ganinta zancen ta da mukayi ya fado min a rai lokaci guda ina ganin ta na tuna wai ashe ita din yar sandan ciki ce take zaman leken asiri a gidan mu to akan me na tambayi kaina ?
Maimakon na zauna a falo kamar yadda muka saba nake fadin bari kawai na rage kayan jikina sai na nufi hayar dakin inda sadiya ma take biye dani bata zauna ba a falon itama.
Mun wuce munbar fadila da mamakin mu a fili kafin ta sauya tunanen ta da cewa wata kila gidan mami muka je aka bata muna rai a can.
Tsoranta nake ji yanzu sadiya ta fada a bayana yasa na juyo ina fadin tsoron wa ke nan anty mana naji yaya yace ita din yar sandace wai .
To kinga kada ki soma yin wani abinda zata gane kin san komai a wurin ta tunda har mun gane ta sai mu bita da hakan shike nan.
Wa zata kama a gidan nan anty da take zaune a nan nima tunanen da nakeyi ke nan sadiya saidai nasan don yaya take wanan aikin a nan mukan meye ruwan mu a ciki tunda bamuyiwa kowa laifi ba .
In ma har mamice ta turota nasan ba zata taba kamani da laifin komai ba tunda banyi ba insha Allahu.
A dakin muka kwana tare da kanwata da barci ya daukemu bamu ma sanda hakan ba tun muna hiran abinda ya faru a gidan mami har mukai shiru muka fara barci.
A cikin dare na falka a dan tsorace na tuna ban rufe kofa ba lokacin bayan na rufene na shiga bandaki na dauro alwala ba abinda nake tunane sai kalamin Nuriya wanda nasan dani take wanan maganan .
Ba komai yasa haka ba sai hangen nesa da take min tana ganin kanar duk dadin duniya da daula ya kare a gareni yanzu.
Wanda ita bata san ABU CIKIN DUHU SIRINE BA ba ko wani dadi yakan daure a dadin da take zato ba ba tare da kalubalin rayuwa a bawa ba.
Hawayen takaici da bakin ciki suka fara zubo min masu zafi daga idanuwana a daidai lokacin da wani tunane ya ziyarci zuciyana na mike lokaci guda na fara ibada sai bayan na dauki lokaci na shafa tare da waigawa inda naji motsin sadiya ina kallon ta sai barcinta take a tsanake hankali kwance nace kin huta baki da damuwa sadiya.
Washe gari tun bayan idar da sallah mu da asubah sadiya ta koma dakinta ta kwanta nasan tayi gudune don kada ince ta tsaya muyi tulawan safe da mukanyi wani lokaci idan ta kwana dakina da safe.
Nima din ranan ban iya tabuka komai ba gado na koma na kwanta tare da dunkulewa wuri daya a haka barci ya daukeni kuma.
Tun daren jiyan ya kasa tsayar da tunanen shi wuri daya har zuwa wayewan garin da bai samu sukuni a tare dashi ba.
A gaskiya ya jefa yarinyar nan a cikin wani hali yasan shikan da badon Allah yai mai zabin mata irin zainab ba a rayuwan shi da yanzu kila ya auri mata sun fi a kirga yana sakin su don halin shi.
Shidai yasan bai iya tsinanawa mace komai na abinda ya shafi jin dadin aurataiya har ya kai ga an samu ciki don tara zuria.
Sam irim wanan tunanen baizo mashi a raiba da farko sam ya manta babu wani babban buri ga dan Afirca kamar ya ga ya tara iyali a karshen rayuwan shi.
Yau sai gashi tun ba,aje ko ina a gaban shi an fara suka na da zance mafi tayar da hankalin wanda ake fadawa hakan.
Nuriya why zaki shigo cikin lamarina haka da gagawa ki bata min tsarin komai da nake shiryawa a kan mu.
Yasan wanan zancen ba waiba zai iya jawo masu matsala a tsakanin shi shida zainab din komai hakkurin ta kuwa.
Don komai hakkurin ka akai ma gori akan haihuwa kuma laifin ba naka bane dole ranka ya baci ga hakan.
Balle shidin da zainab da ba wani irin wanan mu,amulan a tsakanin su da har zai kai ga tunanen haihuwa nan gaba.
Idon shi ya lumshe a hankali yana sauke ajiyan zuciya don numfashin shi da yake ji yana harde mai lokaci guda daga inda yake kwance saman gadon dakin nasa.
A hankali ya fara tunu abubuwan da suka faru dashi tun farko har ya tsunci kanshi cikin wanan harkan duk da ba zai iya cewa ga dalilin fara hakan ba gareshi.
Da idan akwai wanda ya tsani wanan halaiyar a bayan shi yake sai gashi dumu dumu yau a cikin wanan harkan daya tsana din yana yi.
Wani irin nauyi yaji zuciyar shi na mashi lokaci guda da har bai iya sauke numfashi ya sauka mai yadda ya dace.
Da kyat ya dago daga kwancen yana dafe da zuciyar shi ya kai zaune har lokacin hannun shi na saman chest din shi kafin ya samu ya sauke numfashi da karfi yana runtse idanun shi .
Ya dade zaune a hakan kafin ya mike cikin rashin jin dadin komai a lokacin ya nufi hanyar fita daga dakin nasa.
Direct part dina ya nufa kai tsaye ya tura kofan dakin ya jishi a bude duk da safiyane sosai a lokacin yayi mamakin ganin kofana a bude.
Kai tsaye yasa kai ya shiga babu kowa a falon ya nufi uwar dakin da yake tunanen ina ciki a lokacin.
Can ya hangoni kwance tsakiyan gado na dunkule a wuri daya ina barci kamar a wahalce nake yadda na kwanta din.
Ya dan dade tsaye yana kallona yasan dalilin maganan jiyane daya faru a gidan mami din ne ya kawo min rashin barci a daren jiyan.
Kamar zai fita sai kuma kawai ya nufi gadon ya hawo a hankali har zuwa inda nake kwance din ya kwanta ya rungumeni a jikin shi.
Ga mamakin shi sai yaga na gyara kwanciya ina kara shigewa cikin jikin nasa duk a ciki barcin da nakeyi nayi hakan .
Shima ajiyan zuciya ya sauke a nasa bangaren yana jin tausayin kanmu a karo na farko da nadama a rayuwan shi.
Ga kamshin bodyspray din da nake amfani dashi yana shiga mai hancin tare da saukar mai da wani irin yanayi a zuciyar shi da ba zaice ga irin abinda yake ji ba lokacin sai kara rungumeni a jikin shi dayayi a hakan.
Mun kai wani lokaci yana shakan kamashin man gashin da nake amfani dashi wanda har yakai ga daukan hannun shi a hankali ya cusa a tsakiyan gashin kaina dake kwance lub yasha gyara yadda na kamashi wuri daya da zan kwanta tunda ba kitso muke samun yi ba.
Can a cikin barcina nake ji nauyin mutum a jikina sai nake gani kamar mafalkin haka nakeyi kafi hakan ya fara hanani barci don wasan da yakeyi a kaina din.
A tsorace na bude idona tare da dan zabura a firgice a cikin razana ina kokarin yin ihu don tsoro .
Sai nake gani abin kamar a mafalki don bude idanun da sukai min nauyi don barci da nake ji a lokacin ga kuma mutum a tare dani da ban kawo cewa shine ba sam a raina.
Common relax zainab its me jafar kin faye tsoro da yawa now jin hakan bai hanani yunkurin kwance kaina daga gareshi ba a cikin tsoro.
Sai kara rikoni da yayi a jikin nasa babu yadda zanyi in kwace kaina a lokacin don irin rikon da yai min din.
Meye haka yaya zaka shigo min daki ina barci har ka hau min gado ka rike ni kuma ?
Baiyi magana ba sai dan murmushin da naji ya sake da baikai ciki ba dayayi a lokacin.
Kafin can inji yace zainab zuciyana kamar zai fashe nakejin sa na kasa rike kaina da kaina ina neman inda zan raba naji sanyi ne a rayuwana.
Ba tare da na juyo ba don babu daman hakan saboda irin rikon da yai min ba daman na kaucewa hakan.
Amma a cikin karfin hali irin namu na mata nace mai babu sanyi ko sauki a tare dani yaya don babu abinda zan ma a hakan ka sani.
Nima din da ka sani da baka nufoni ba don a hakan yadda kake ka sameni a yanzu don ba kai kadai ke cikin bacin rai ba yau.
Na sani zainab ya fada kamar wani karami yaro dashi yana kara cusa kanshi a kaina yadda muke kwancen.
A cikin wanan yanayin fadila ta fado dakin ta samemu ta koma baya da sauri tana dafe kirjin ta do abinda idon ta ya gane mata a lokacin.
Wanan wani irin mutum ne da ba,a gane gaban sa sai da ina gab da hada komai dana samu gareshi yanzu kuma zai canza min lissafi ?
Idab na bada shedan shi din guy ne bai aikata wani abu da matar shi fa yanzun ga idona kai haba ashe malam biri yai kama da mutum na kasa gane gaskiyar yarinyar nan tun farko.
Ashe akwai abinda ke wakana a tsakanin sune wani lokaci yasa take kin fada mi komai idan na tuntube ta da zancen nasa.
A dakin kuma shiru ne ya biyo baya kamar ba zai yi magana ba sai can yace a naki ganin ke nan zainab ?
Amma at list ko wanan rikon da nayi maki naji sanyi a raina ba kamar yadda na shigo dakin da kumci ba a zuciyana da farko ba.
Da karfin gaske na kwace kaina a jikin shi jin abunda ya fada din ina fadin duk wani jin dadi ko walwala ka haramtashi a zukatan mu yaya.
Yau sanadin ka har ake daukan laifin da banawa ba ana dora mi duk da bansan yadda ubangiji ya halicceni ba tun farko ko ni din mai haihuwace ko akasin hakan .
Amma a yanzu kam laifin hakan yana wurin ka yaya don dama na dade ina tsoron wanan ranan duba ga yadda mutanen mu suke nan akan aure.
Tareni yayi da fadin na fiki sanin duk wanan matsalan yana tafe muna komai dadin dadewa watarana za a samu wanda zai muna wanan korafin na haihuwa a tsakanin duba ga yadda muka dauki shekaru a tare dake.
Amma sam banyi tsamani hakan zai fito daga bangarena ba sai dai daga gun yan uwan ki nafi zaton hakan.
Zainab nasan kinyi hakkuri ga komai game da zama dani a hakan don banda abinda zan iya saka maki dashi a rayuwana da zan maki na ga na saka maki ga hakkurin ki.
Nima din a yanzu nakan yi nadaman hakan saidai ba kowa bane zai yadda da hakan sanin ni ko waye ke tare dake kuma kikai hakkuri kika zauna dani hakana.
Duk da nasan Nuriya ta yi wanan zancen tana daukan kece mai laifin rashin haihuwan a tsakanin mu duba ga irin rayuwan da kike ciki a gidana.
Wanda nasan zafi da kishi irin naku na mata yasa ta fada muna wanan maganan haka a gaban kowa don dai kawai taga ta bata maki rayuwan ki.
Saidai da tasan abinda kalamin nata zai jawo a gareta da bata furta hakan da nufin tozarci a gareki ba don ba iya ita wanan kalaman zai shafa har mijin ta da kowa a yanzu hakan zai shafa.
Kara matsawa nayi dan nisa dashi a cikin murmushi nace kaiyya idan kai hakan ga yaya mamud baka kyauta ba kuwa .
Don baka da dan uwa mafi soyuwa a gareka bayan shi da jamal duk da ban zauna dasu ba munyi wanan zancen amma naga damuwa karara a tare dasu kan sanin ko kai waye da sukayi.
Shiru yayi gashi yana son bani hakkuri saidai ya rasa kalman da zaiyi amfani dashi wurin bani hakkuri a bakin shi don shi a nasa ganin tsaya a bata lokaci wurin ba mace hakkuri wani abune can na daban .
Gyara kwanciya naga yayi ya mike saman gadon tare da lumshe idanuwan shi sai hakan da yayi min a daki ya zama min wani bakon al,amari kuma tunda ban saba ganin hakan ba ni.
Sai mukai shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunane a ransa sai da na jefo mai tambayan da baiso ne ya bude idanun sa lokaci guda da nace.
Yaushe ne zamu gida muga su inna na tambaya cikin kallon shi inji amsan da zai bani lokacin sai cewa yayi dani sai idan kun kara hutawa zan shiryawa zuwan ku din.
Ba wani hutu don ba aikin komai nakeyi ba ko wani abu a nan yanzu don haka gida muke son zuwa mu ganesu.
Zaku tafi amma ba yanzu ba ya fada yana kara gyara kwanciya vikin dan kara lafewa saman gadon kamar mai shirin yin barci a dakin.
Iya kuluwa na kulu da jin amsan daya bani a lokacin don haka ban ko iya bude baki na ce dashi wani abu ba sai faman tunane da nakeyi a can kasan zuciyana wanda na kasa tsayar da zance guda kan hakan.
A hankali nake ji saukan numfashin sa dake nuna min ya samu barci ne a hakan na sauka saman gado a hankali zuwa bandaki don i kewa ya daga nan na tsaya yin wanka.
Har na fito yana a inda na barshi a kwance yana barci bai tashi ba balle in sa ran fitan shi daga dakin nawa sai abin nasa yake ban mamaki.
Haka na daure na karasa bakin mirrow ina shafa mai a jikkina da sauran al,adun mu na mata idan munyi wanka.
Kamar ance in daga kai yana kwance ya lafe a inda yake din ya kura min ido yana kallona nayi sauri kawar da kai daga hada idon da mukayi dashi da sauri.
Mikewa nayi zuwa wardrobe dina na bude sai lokacin nace dashi an lodawa mutum kaya haka kamar wanda zaiyi wani abu dasu ba sakawa ba.
Idan basuyi maki ba sai ki kyautar ya fada yana juyawa daga barin da yake kwance din nace har yaushe zamuyi amfani da wanan kaya haka wai ?
Har na gama na shirya a boboye duk yana dakin banu abinda nake ji sai haushi da takaici nasa na yadda ya zauna min a dakin da bansan dalilin hakan ba.
Bai fita dakin ba nima kamar an dasani a dakin haka muka zauna sai wuraren sha biyun rana ya bar dakin ya nufi part din shi.
Nima daki na gyara duk da wata tazo wai itace mai gyara amma ban yarda da hakan ba dana tashi kafin tazo na gyara dakina tsab balle yanzu da nake jin tsoron duk wanda ke gidan tare damu zaune sai nake masu bugu daya gaba dayan su ma aikatan gidan.
Ban fito ba saida sadiya ta shigo dakin tana fadin yayan mu kun tashi ke nan dazun nazo zan shiga anty ke fada min yaya yana ciki kwance.
Fadila fa na fada da mamaki tace eh ita ke fada mi hakan sai na koma barci yanzu na tashi yunwa nake ji sosai tana shafan ciki ta.
Ina mamakin fadila a raina nace ke nan bakici abinci ba kema tun dazun jin hakan yasa na mike muka fito falon tare ganin fadila dake mazurai yasa nace barin duba yaya ya fito mu karya na nufi part din nasa.
Na samu yayi wanka har ya saka tufafi a jikin shi a cikin daure nake fadin wai sadiya bataci abinci ba tun dazun tana jiran mu fadila ke fada mata kana dakina.
Bakiji lokacin da ta shigo dakin bane muna kwance ya fada na zaro ido waje a cikin mamaki yace eh ai hakan yayi kyau don zata shiga duhu kan abinda take hadawa yanxu.
Haka dai muka fito suka shiga gaidashi yana amsawa cikin basarwa har ya zauna yana fadin kanwata ya akayi baki ci abinci ba kika tsaya jiran mu ?
Haka dai muka zauna duk abin yana daurewa fadila kai don ta kasa fasara matsayin da yaya j yake ciki a yanzu don bayanin data tara nata yanzu ya bayar da ita kuma.
Wayan shi ne ya shiga kuka alaman kira na shigo mashi a lokacin ya basar kamar bai ga kiran ba haka yasa na duba ya mamud ne na dan dube shi sai ya dauki wayan ba don yaso ba sun gaisa yake tambayan shi naji yace bana gida na fita tunda safe.
Haka yasa na dago ido ina kallon shi vikin mamaki don da alama abinda ya fadi yake shiri sikatawa don laifin daba nasu ba ya shafi kowa a yanzu ke nan.
To meye laifin su ma akan wanan maganan dashi ya jawa kanshi hakan kome aka fada ai naga shiya jawa kansa dai hakam.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.