Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 36 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2ï¸Â⃣9ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA DON TURA KUDINSA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN DARI UKU KACAL A WANAN LAYIN 08036959257 NAGODE GA WANDA YASAN ZAFIN ABINDA NA FADA.
Da mamaki ta juya don a zaton ta yana cikin dakin sai dai bataji alaman mutum a part din ba haka ta dawo dakin ta ta nufa direct .
Har ta zauna ta bude system dinta da niyar tayi aiki a cikin sa sai zuciyar ta ba zai barta tayi abinda take so ba a lokacin.
Har dare duk wanda ya shigo gaida ita tana tambaya idan ya dawo sai suce basuga shigowan shi ba kuma security din shi basa nan saidai ga wayan shi na shiga kuma karshe taji wayan a kashe.
Washegari wanan dalilin ya hana mami fita aiki da wuri ni dai nagama mata komai tana bandaki kafin ta fito na karasa na fita daga dakin shiryawa nayi a gurguje kar driver dake kaimu school ya jirani.
Mami ta gane me nake nufi don ta fahinci tun jiyan ina gudinta don ban fito ba ita kuma bata tambaya ba duk ta san banda laifin kan hakan amma zuciyar ta ya kasa daina jin haushina.
Zazzabi mai karfe gaske yake ji a jikin shi tunda ya falka da safe da kyat ya iya shiga bandaki yai wanka ya fito yayi sallah asuba ya koma ya kwanta.
Mami ta fito daga dakinta ta samu hjy zaune a falo ita kadai tana kallo wa,azi da takance kafin mu kai mata kafin mu fita da safe.
Mami ke fadin hjy tun jiya banga shigowan jafar ba ko kinga fitan shi da safen nan da mamaki hjy ke fadin yanzun nake maganan shi a raina ni kadai.
Ko tafiyan yayi babu salma kuma wanan karo ma mami ta dan yi tunanw tare da fadin anya don bai dade da dawowa ba da wuya ya sake fita.
Part din shi ta nufa tana fadin bari in dubashi ko yana ciki har yanzu idan ba fita yayi ba.
Murda kofan tayi taji kofan a bude yake haka ya bata daman shiga dakin kai tsaye tsab falon yake kamar kullun sai kamshin dake tashi a cikin sa.
Cups har biyu ta gani aje saman dan table din glass din dake gaban kujera sai fararen takardu dasu laptop a gefen kujera aje.
Kai tsaye ta nufi dakin kwanan shi ta fara kwankwasa kofan ta fara kwankwasawa sai gana ukune ya amsa da kyar ya iya yin magana ya tambaya da waye ?
Nice ta bashi amsa a gadarance ba tare da ta kara furta wani abuba a kai.
Kofan a bude yake ya fada yana kokarin cire bargon dake jikin shi rufe mami ta tura kofan ta shiga daga cikin dakin.
Ta hango shi yadda yake kwance saman gado ya dan rufe rabin jikin shi da bargon.
Lafiya kake kwance haka a rufe tun dare baka leko muba baka kuma shigo da safen nan ba mami ta fada tana karasawa bakin gadon nasa tana zama.
Sai daya dan dago daga kwancen cikin yanayin yamutsa fuskan shi yace yau bana jin dadi ne amma yanzun nake son in shiga.
Baka jin dadi shine zaka kwanta a daki kai kadai haka ba wanda ya sani kamar karamin yaro mami ta karasa fadan nata da tambayan wai meke damuwan kane.
Cikin dauriya yai magana da kyat yana dafe kirjin shi mami ina jin kirjina na ciwo da zazzabi.
Wani kallo tayi mashi kafin tace dashi ai saika tashi kaje likita ya dubaka ko ?
Mami ba sai naje asibiti ba nasha magani dazun da zan kwanta tace ka karya ne da kasha maganin ?
Baida matsala mami yanzun zan fito ya fada yana maida kanshi ga filon da ya dago akai.
Ido mami ta dan kura mai kafin tace zaka jawa kanka matsala akan wanan yarinyar har da kwanciya ciwo don kawai na fadama gaskiya.
Murmushi kawai ya danyi tare da lumshe idanun shi ba tare daya iya mata magana ba ta mike tana fadin idan ba zaka iya fitowa insa lami ta kawo ma abin karyawan ka nan ka tashi ka karya ko zakaji saukin jikin.
Sai lokacin ya iya magana yace ba sai ta kawo min ba mami zan fito da kaina ai ya sake lumshe idon shi a hankali.
Mami a cikin dakewa take da karfin hali a lokacin don gaba daya hankalinta ya tashi ga halin data samu dan nata a ciki wanda take tunanen maganan su najiyane yaja masa wanan kwanciyar haka.
Hjy na zaune falo tana dakon fitowan hjy sai gata tun kan ta karaso take tambaya kin same shi a ciki ?
Yana nan hjy wai ashe baya jin dadin jikin sane yakw kwance daki shi kadai bai fadawa kowa ba.
Subbahanallahi me ya sameshi haka har yaron nan yake kwance bamu sani a cikin gidan nan.
Ciwo yake son jawa kanshi kawai hjy don nayi masa fada jiya shine yake wanan ciwon don batacin zaijawa kanshi ciwo ya halaka kansa akan abinda baikai ya kawo ba.
Hjy bata ba mami amsa ba sai mikewan da tayi tana fadin bari na leka shi inga halinda yake ciki tabar mami na kiran lami daga falon.
Dakin shi hjy ta nufa daga kofa ta tsaya tana kwala sallama daga can ya jiyo muryanta ya yunkura da kyar ya taso zuwa falon.
Da kyat ya iso yana kokarin zama saman dogon kujeran tare da fadin hjy kin tasone yanzun nake son tashi in shiga mu gaisa dake ai.
Kai da baka da lafiya aikai ya kamata azo a duba koda yake uwarka tace kaine kajawa kanka ciwon bansan dalilin ta na fadin hakan ba.
Hankalinshi yaji ya kara tashi lokaci guda idon shi suka kada sukai jawur gashi abinda yake ji a zuciyar shi kamar ya fita a lokacin ya aikata saidai baison ya biyowa mami ta wanan hanyan da yake ganin ranta zai mugun baci a karshe.
Gashi hundred pacent ya amin a zuciyar shi da zabinshi yasan da farko ba son yarinyar yakeyi har cikin ranshi ba.
Illa tausayinta da taimakon kanshi ya zauna lafiya a rayuwan shi don itace kawai fufin asirin shi a rayuwan shi.
Zai iya samunta da sauki fiye da wace mami ke shirin aura mai yasan ko wacece indai yaran ire iren kawayen mamine dole idanun yarinyar a bude yake itama.
Sai dai kuma daga jiyan da mami ke kara ikirari akan ya janyewa yarinyar nan zeey abinda ya faru tsakanin su yasa yana jin wani irin feeling yana matukar jin yarinyar a ranshi.
Fiye da yadda bai taba tsanmanin faruwan haka ba a tsakanin su tunda yake mu,amulan shi da mata a rayuwan shi badai wani abune ke shiga tsakani su ba sai dai hugging da dan kiss a tsakanin su kawai.
Hannun shi yakai a kai yana dan shafan kanshi tare da jin wani wutan son yarinyar na kara ruwa akansa.
Tankar yadda wutan kara yake kamawa gadan gadan yana saurin yaduwa a duk lokacin daya kama a cikin jeji.
Jafari ka sassauta zuciyar ka kabi lamarin nan a sannu kamar yadda na fada ma da farko kada kajawa kanka ciwo idan har iyami bata yarda da bukatan ka a cikin lalama ai tana da magabata ko, wa yanda zaka iya gani bayan ita.
Saida ya sanye harshen shi ya lashi labbansa da suka bushe masa yana cike da takaici da kunan ran wanan lamarin da mami ta bijiro masa.
Kafin yace hjy mami bata sani ba idan har tace a yanzu ba zata yarda da zabina ba sai dai in fasa auren duk wata yarinya da take fadin zata hadani da ita a kasan nan.
Ni namiji ne fa ina da daman da zan zabawa kaina abinda nake son rayuwana dashi don ba wani ne zai zauna da ita ba saini.
Ta bangarena ranan dai naje school ne amma babu abindana iya tsinta a cikin abinda akai muna don tune biyu daya tsaya min a rai.
Na farko shine mami yadda take min din nan abin ya fara tsoratani sosai duk a kan danta take nuna min wanan kyamar dana kasa gane dalilin ta nayin hakan gareni idan nayi dubaiya ga yadda muke da, da ita.
Amma sanadiyar bullowan wanan maganan gaba daya mami ta sauya min ga sabon halin disgani ko agaban waye data dauko yi min yanzu wanda hakan ya fara taba min zuciya duk da ina yarinya.
Sai nabiyu abinda ya jafar yai min a jiyan ya tsoratani matuka gaba daya ya dasa min tsoron shi a zuciyana.
Haka muka dawo gida ina a cikin damu tun daga ranan na daina fitowa falo idan ina gidan har ma in na fito sai idan zan shiga kitchen dauko abinci ko wurin su mama kande mudan taba hira.
Gashi tun ranan ban kara saka yaya a idona ba saidai nasan yana gidan ba tafiya yayi ba don ina ganin security din shi da safe idan zamu tafi makaranta.
Ta hakan na gane yana gidan bamu dai haduwane dashi ko kuma mami ta shawo kanshine ya yarda zabinta gareshi.
Yanzu ya gane niba ajin sa bace ya wuce ajina ga aure saidai diyan manya irin su can irin wanda mami keson ya aure har hakan ya jawo matsaloli a tsakanin mu.
Na fito ina tafiya kamar yadda na saba zakace ko ina tsoron kasa ne yadda nake takona, ga uniform din jikina sun karbeni sosai.
Kamar ance in daga kai in kalle saitin dakin ya jafar daga inda nake tsaye jikin mota ina jiran fitowan yaran yaya mamud mu kama hanya.
Caraf idona ya hadu da nasa daga inda yake tsaye jikin aindon shi yana sanye da bathrobe a jikin shi ya bude gaban rigar yadda zaka iya hango six pack din shi na kiran maza a waje.
Yana rike da cup din farin glass a hannun shi idanun shi a kaina da sauri na juya na bashi baya daga kallon shi da gujewa nashi ganin kuma.
Kai ya girgiza cikin dan murmushi yana mai jin dadin yanayin danayi din don shi abin nawa ma dariya yake basa ko yaushe a yadda nake nuna tsoro idan na ganshi.
Yasan bayin kaina bane hakan mami ce ta riga da ta dasa min tsoronta a raina akan shi don hakan dole inyi hakan don tserar da mutuncina a furin mami din.
Har muka shiga mota yana tsaye a gurin yana dan kurban abinda yake sha a hankali a cikin cup din.
Sai da motar mu ta daga na sauke wani irin nauyayyan ajiyan zuciya a fili tare da lumshe idona a hankali ina mai jin wani iri a raina.
Haka shima ya jafar din bai daga, daga wurin ba saida yaga motar tamu ta bace ga ganin shi ya sauke wani irin ajiyan zuciya lokaci guda tare da juyawa yabar wurin da sauri.
Mami na zaune dakin ta tana shiryawa adaidai lokacin yayi sallama ya shigo dakin direct inda take ya nufa ya danyi hugging din ta.
Tare da fadin morning mami kanshi ta shafa tare da fadin dan albarka ka tashi lafiya lafiya kalau mami ya fada ya koma bakin gadon ya dan kidinshida tare da daga kafan shi daya yana duban wayan shi.
Friend wai gaba daya ka sauya dabi,un ka yanzu har abincin dare ka daina zama dani muci ka kuma san wanan time din ne kawai nake dashi danake dan kebewa daku.
Tunda ba fitowa kake da safe ba kafin in wuce wurin aiki balle in ganka shiru yayi bai bata amsa ba sai ta dauka hankalin shi yaga wayan hannun shine hakan yasa ta juyo tana kallon shi.
Saidai ganin sabanin hakan garshi lokacin data juyo din yana kallon wani wurin na daban tare da yanayin tunane a fuskan shi.
Friend wai me yake damun kane haka ina magana ka lula wani duniyan tunane me kake tunane hakane wanan kwailar yarinyar zeey ka saka a zuciyar ka ko ?
Kan shi ya dago a hankali ya dubi mami tare da fadin babu komai mami me kika gani halan.
Kai ta girgiza tare da juyowa gareshi gaba daya tana fadin babu yadda za ayi kace babu komai duk mutum mai hankali da zarar ya dubeka yasan kana cikin yanayi na damuwa.
Amma dai tunda ba zaka fada kuma ni nasan zancen yarinyar nan ne har yanzu ka saka a ranka kamar yar wani da wata.
Kai yanzu kana ganin kafanka ya kama kasa ban isa kai min abinda nake so kayi a matsayina na mahaifiyar ka balle har kace ba zaka fada min abinda ke tsoce ka ba sai dan dogon wuya kake ajewa kanka.
Mami na fada maki bani tare da wata matsala kirjinane kawai har yanzu bana jin dadin sa zancen zeey kuma aini na fita wanan zancen yanzu, don shirin komawama nakeyi tunda an fasa zancen auren kince bakyayi da zabina sai a fasa auren a yanzu sai na laluba wata kuma.
Mikewa mami tayi tana fadin kaima kasan hakan ai ba zai yuyu ba ka koma ba tare da aje iyali ba .
To mami ki bari in auri zabina don shine rufin asirin daki dani daku ga baki daya ba ko wace mace bane zabin namiji ko wani namiji da kalar macen da yake so a rayuwan shi.
Haka kace ke nan ni bansan abinda zuciyar ka keso ba ke nan na zaba maka nawa ra,yin ko to tashi ka ban wuri .
Ga mamakin mami sai taga ya mike don barin dakin kamar yadda ta umurceshi ya bari din.
Har ya fice daga dakin mami tana binshi da kallon mamaki da tsoron abindaya fada yanzu a gabanta wanda ta kasa gane me hakan da yaron nn ke fadi yake nufi ne ?
Ya dan jima tare da hjy a falo suna fira inda yake fada mata zai koma bakin aikin shi bada dadewan nan ba.
Hjy ta dago kai tana fadin har tafiyan ya karaso ke nan yaya zancen auren naka don idan ka koma a yanzu wayasan ran dawowan ka wanan kasar jafari ?
Hjy zan dawo a daidai lokacin daya dace sai dai wanan sirine tsakanina dake ki kula min da yarinyar nan yadda ya dace zan dan barta ta kara wayau da sanin kanta.
Yanzu zan nunawa mami ni yarinyar bata gaba sai daidai da lokacin daya dace in dawo gareku da wanan zancen zan dawo da nuna mata gaskiyata.
Ban fahinci maganar kaba jafari tsohuwar ta fada yacs zaki fahinta hjy don koma a bayane zaizo maku hjy.
Mikewa tsaye yayi yana kallon agogon hannun shi tare da fadin zai soma tafiya a rude tsohuwar ke fadin don Allah dan son manzon tsira ka saurareni kada ka je ka dan dakata mu kara fuskantar iyami na dan lokaci.
Shu,umin murmushi shi kawai ya sakar ma tsohuwar ba tare da ya tsaya ya furta wani abuba akai yai mata Allah bamu wuni lafiya yasa kai ya fita daga gidan.
Ashe hjy ta samu mami ta yi mata tas akan ya jafar tare da lurar da ita halinda take son jefa danta a ciki takare da fadin idan kin kashe shi ko kika bari ya tafi yabar kasan nan kan wani dalili naki can baku fuskanci juna ba kanki zaki tarawa bakin ciki.
Shi auren gatan da kike fada bashi bane kukaiwa mamud yanzu ki fada min dadin da kukaji a cikin wanan hadin na mamuda din.
Ke kanki ba dadin yarinyar nan kike ji ba ina gani sai taga dama take shigowa nan koshi sai da wani dalili mai kwari shi mamudan basai ya fada ba da ganin sa kasan a tauye yake da ita duk dai saboda ku a gidan nan.
Iyami da zaki gane abinda nake nufi a nan da sai ince ki kyale yaron nan ya auri zabinsa tunda dai hakan ba haramun bane.
In kin hanashi auren wacce kika san halinta ai zai kwaso maki fitsarariya da zata zo ta wargaza maki gidan ki.
Kindai ji ikirarin da yaron nan keyi a gaban ki ko yaushe da yarinyar nan itace daidai dashi kinsan abinda hakan ke nufi a zuciyar shi ke baki kwantawa ki auna me hakan da yake fada ko yaushene yake nufi.
Maza fa ba ayi masu dole ba kamar mata suke ba su ki barshi da zabin sa abinda yagani da idon sa yace yana so.
Ai gara wanan din ma daya zaba kinsanta kinsan ta kinsan halinta ciki da bai kina yi tankwasa ta aduk yadda kike son ta ba kamar wanan ta wurin mamudan ba.
Sannan har idan itama yarinyar nan ta kamu da son yaron fa kinga kin zalunce su tunda itama a karkashin ki take.
Har in kina gudun tayar da alkawari ne ga iyayyen wacan da kika nema masa ki barsu dashi shida kanshi zai nuna masu halinshi ita din ba zabinsa bane amma ina amfanin ayi abu adawo ana danasani akansa haka.
Iyami ki rabu da dan yau idan ya furta baison abu to ki kyaleshi yai wanda yake so matukar ba abinda zai sabawa mahaliccin shi bane abin.
Gaba daya jikin mami yayi sanyi lokaci guda hankalinta da natsuwa suka zo mat lokaci guda ta bude baki tace hjy ni kaina kalamin yaron nan yana sakani a duhu ko yaushe idan na zauna nayi tunane mai kalman nan da yake yawan fada min haka yake nufine gareni .
To kin gani ABU A CIKIN DUHU SIRINE shi yasan me hakan ke nufi ya kuma barwa kanshi sirin abin a zuciyar shi maza ba kamar mu mata suke ba yaron nan shi yasan me yagani gun yarinyat nan ya dahe mata har baijin kwabon ki a yanzu.
Hjy zan ga iyayyen yarinyar mu zanta zancen dasu in Allah ya yarda hjy tace ba sai na shiga zancen ba ke nan yanzu.
Hjy basai kin kara magana ba in Allah ya yarda zan zauna da yan uwana muyi duba dakyau ki barmu da kaina zan gyara kurakurena zan shirya komai.
Hjy tace koke fa Iyami Allah yayi maki albarka ya daukaka maki zurian ki ya kare ku daga sherin makiya da mahassada.
Naji dadi kwarai da kika fahinci mai nake nufi kafin wani abinda ba a so yazo ya faru kan maganan nan yanzu.
Duniya yanzu idan zaka biyewa mutanen cikin ta ba zaka taba aikata daidai ba a rayuwan ka sai a baka gurguwan shawara idan ta kwabe adawo ana zunden ka a baya.
Sai yarinyar nan ya zama dole yanzu ki gyara mu,amulan ku da ita tunda kin riga da kin bata komai a tsakanin ku don dai yarinyar ma mai hakkurice da sanin yakamata.
Ba kowa bane za a nunawa hakan ya iya shanyeshi a zuciyar shi ki gyara tsakanin ku kada yazo ta rike abin a ranta ki nuna mata mu ba butulai bane kuskure aka samu a baya hakan ya faru.
Nayi mamaki sanin kankine aurene fa yarin ga yace yana so da yar nan taki don yarinyar ta zama yarki halal malal sanan aure sunnan ma,akin Allah ne.
Bai kamata kiyi shishigi da nuna iko a cikin lamarin aure ba hakan nan kizo ki mutu akuma yi wanan auren idan da rabo a tsakanin su azo ana fadan da baki mutu ba ba za,ayi wanan auren ba.
Idan ma baki mutum ba ayi ba acikin yardan ki ba kikuma gansu a tare da babu yadda zakiyi da hukuncin ubangijin ki a kansu.
Wani hawayen bakin cikine ya zubu a idon mami lokaci guda tace wallahi nima hjy na rasa me yasa bana son wanan auren ko nayi niyar barin shi yayi abinsa.
Don zeey har ga Allah abin asone a gida dubaga irin hakkurin yarinyar da sanin yakamatan ta kamar ba karamar yarinya ba da ita.
Gata abin tausayi to hjy na rigada nayiwa hjy saude alkawari akan yar ta duba da yadda muka dade da ita muna amintaka yau ace naki hadin da take so a tsakanin mu.
Hjy tace ai itama ta haifa tana dasu ba zataki abinda danta zaiso ba har in son gaskiya take maki bazata taba ganin laifin ki kan zancen nan ba.
Tunda ba kece maiyin auren ba wanda zaiyi yace yarta batai mashi ba sai dai tayi hakkuri yanzu kan.
Tana fadan haka ta mike tana fadin ni zanje inyi alwala inyi nafila lokaci na kure min.
Nan tabar mami zaune da dinbin tunane a ranta na yadda zata bullowa wanan al,amarin da yaronta ya bijiro mata dashi a yanzu.
Don ko ita dadin tane ta sani nan gaba don samun yarinyar garesu ba karamin alheri ba wurin jafar sai dai kawai ace babu good backgraund gareta ne na iyayyen da suka isa gare ta shine kawai abin duba.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.