Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 50 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU SIRI NE 🦅

4️⃣2️⃣

ZAINAIBA IDRIS MAKAWA

ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA DA FATAN KOWA NA LAFIYA UBANGJI YA BAMU HASKE GA AL,AMURAN MU AMI YA ALLAHU, , ,

YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI TUNA HAKAN DON ALLAH KADA MU RIKE JUNA DANI DAKE DARI UKU NE KACAL SISTER TA BANK KO KATIN WAYA NAGODE, , ,

Kai duniya muji tsoron Allah wai mutane yanzu basa tunane ba a duniya za a tabbata ba zamu koma ga mahailicin mu Allah .
Amma saboda son kai sai kaga idon mutum ya rufe akan duniya ya manta da za a koma wurin ubangijin talikai ya dinga yin abinda ya ga dama.
Mami batai tunanen laifin daga gurin ta bane sai kokarin dora laifin abinda idon ta yagani akan dan nata yau takeyi a kaina.
Tana tunanen da badon ni ba da danta bai shiga wanan halin ba data sameshi a ciki don kawai wanan matsalan har yakai ga wai ya fara shaye shaye haka saboda idon ta ya gama rufewa a lokacin.
Ta dade kwance ita kadai a dakin kafin tayi karfin halin mikewa tsaye don zuwa gahatar da sallah la,asar da yayi tun dazun tun safe ta kasa kai komai a cikin ta har zuwa lokacin.
A Inda ta idar da sallah take zaune har lokacin tana cikin zulumi da tunane halin data riski dan nata a cikin .
Wayan dake gefen tane yake ta ringing ta kasa tashi ta dauka sai bin waya takeyi da idanuwa kawai a saman gadon.
Mami wayan kine fa ke ringing Aisha ta fada daga kofa tana shigowa daki lokacin idon ta akan mahaifiyar tasu dake zaune wurin da take sallah.
Dago kai tayi ta kalli yar nata a ciki wani irin yanayi na ban tausayi a gare ta da wanda ya ganta a lokacin dole ya fahinci bata a cikin hayacin ta.
Mami lafiya Aisha ta fada tare da kaiwa zaune a bakin gado tana kokarin daukowa uwar wayan dake kara saman gado.
Ajiyan zuciya ta sauke kafin tace duba min yayan ku idan ya dawo daga wurin aiki har ta mike tace ya mamud ke nufi mami kin yanzu bai dawo ba ai sai after six zai shigo.
Hannu biyu ta dauka ta dora a fuskan ta a cikin yanayin nuna takura a rayuwanta a lokacin sai kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciya da tashi hankali.
Take hankalu Aisha ya daga sai wanan lokacin ta fara nadaman rashin grany dinsu a tare dasu yanzu ina tasan zata dosa da wanan matsalan na uwar su da bata san abinda ke damun ta ba.
Mami Aisha ta fada a sanyayye mami lafiya meke faruwa ne wai dake barin duba idan ya j na gida na kira maki shi.
Karki soma ta fada a cikin wani murya mai nuna cikkaken umurni a gareta da sauri don tsoro ta koma ta zauna a inda ta tashi da farko.
Ido ta kurawa mahaifiyar tasu kamar tana nazarin ta kafin tayi karfin halin fadin mami koma meke damun ki kiyi hakkuri don Allah ki daina zubar da wanan hawayen haka.
Aisha will you believe da irin halin dana riski dan uwan ku yau a ciki koda yake barshi kawai bai dace ma in fada maki ba a yanzu.
Mami wani abin yayi kuma after all he has gone through na yin aure bai fada maki ba ko ya dauko zeey din ne zuwa gidan na kuma ?
Wani kallon takaici ta jefawa yar nata tare da mata gargadin ke yarinyace Aisha ta kawar da kanta ga kallon ta do takaici data kara bata na ambatan sunana a wurin.
Aisha ta dade a zaune tana kallon yanayin mahaifiyar tasu dake a cikin tashin hankalin data kasa gane dalilin hakan a yanzu.
Mikewa Aisha tayi daniyar barindakin dob ba zata juri ganin uwar a cikin wanan hali ba na bacin rai.
Sunanta mami ta ambata ba tare data dago kai a yadda take ba taci gaba da fadi kada ki fadawa kowa halinda kika sameni a yanzu.
Naji mami Aishan ta fada har ta soma tafiya taja ta tsaya tare da fadin but mami da sauri ta fara tafiya bayan hannu da uwar ta kara daga mata kuma.

Koda Abba ya dawo gida da dan ledan shi dayayo cefane din a dafawa hjy ya samu hjyn ta fito zasu tafi don azzarlazalan da ya jamal ke mata tafito kada su makara.
Af hjy wai tafiya zakiyi ne yanzu ga abin tabawa har na sayo a gyara maki kada kizo garin baki taba komai ba.
Cikk yar fara a da nuna jin dadin yadda ake kulata a gidan namu hjy tace ai yata ta gama ban komai yaushe rabona da nasha fura da nono haka mai dadi.
Ga kawata ta nuna Asabe bayan innar mu tana fadin ta kawo mi ganye shima na taba ko hakama aina gode.
Ta nunani tana fadin saidai ga matar jikana nan don Allah ina son a bata duk wani kulawan daya dace da ita don yanzu ita din ba abin wasa bane a guri kowa.
Kanne dakr gefe tsaye duk suka kalloni a lokaci daya don jin abinda hjy din ta fada akaina suna murmushi.
Nauyi da kunyane ya kamani lokaci guda muna gaba nan muka barta da Abba da innar mu da Asabe suna maganan abinda bansan kome suke fada ba a lokacin.
Muna tsaye a bakin mota tare dasu ya jamal duk da dai gaisuwa kawai mukayi dashi ya juya abinshi bai kara bi ta kan mu ba kuma.
Wanan fa mai kama da balarabe yayar mu amma dai bai iya hausa ba ko don naji hausan nasa kamar da turanci ya amsa mana.
Yayan mune ba bata amsa dashi batare da kara furta komai ba hankalina yana gun abinda suke tataunawa a kai.
Abba ya san fito ya bar hjy da innan mu sai can ta fito ta amemu a wurin motar hannu ta mika min na nufi wurinta don na gane abinda take nufi da hakan.
Dan rugumeni tayi kakar mai rada take fadin in kula da kaina zamuyi waya idan ta isa gida tana son in zama mai biyayya a duk yadda na riski kaina a ciki da mijina.
Nauyi da kunya ne suka dan rufeni saiga idanuwana suna dan ciciko da hawaye a lokacin guda kamar kada in rabu da tsohuwar muna kalo haka ta barmu a gurun suka tafi bayan alherin databi kowa dake wurin dashi na kudi.
Mun juya da zuman shiga gida muka tsinkayi muryan Abba da lantana har da innan mu da sauri muka karasa zuwa ciki don ganewa idon mu abinda ke guda.
Lantanace ta cikuwaikuye abban mu dake tare ta a dole sai ta karbi ladan da Abba yabawa inna mu a gyara min abinda ya sayo a yiwa hjy dan abin motsa baki.
Tunda na tunkaro wurin nayi arba dasu a halinda suke ciki na runtse idanuwana a hankali do abinda idona ya gane min .
Kai kai kai amma yar nan baki da albarka yanzun nan da bakin ma a gidan sai kinyi wanan saida halin da kika saba ashe.
Da badon mutane na sun tafi ba haka zaki barmu da abin fade a gidan nan saboda baki fitina irin naki.
Inna don Allah ki mika mata ko manene a daina wana fitina indai a kaina ne ake wanan abin na fada cikin dan marairaicewa inna mu din.
Ba ita kadaice mai bakin ci ba yau ina sin i gani idan na karfi ne tazo takwata tunda an fada mata mu bamu da hakki akan shi komai sai itace za a sayawa taci muna kallo.
Af don kin fadawa yarki tsoron karba zanyi ko me ni kunya ma kika ban ace wai yarka ta dawo yawon bariki haka tana haska gari har zaki tsaya fada kan wana dan ledan hannun ki.
Ina kwalayen da kaya dadin da aka saba zo maki dashi wanan karon ta kwabe ba a kawo din bane ko meye don naga kamar su dawo muka da gaiyan tsiyan ku gidane sun gaji da kwallon mangoro sun yar sun huta da kuda .
Inna mu dai bata sake ledan ba tayi daki dashi muka bita ga baki daya mu yan dakin namu saboda Abban mu dake wuri ya hana ai magana a lokacin.
Muna shiga daki akan kwalayen da aka jera a daki wanda lantana kewa gatse sa,adatu ta nufa tana tambayana ko kwalayen meye ina mata bayani .
Banso akaiwa lantana ba a lokacin kada ta dauka don gatsen da tayine yasa aka kawo mata din kuma in ba akaidi ba inna tace sai tace ai daga bayane aka sayo aka kawo muna.
Kwalayen madara ne na tea sai milor da sauran tarkacen kayan tea da katon din lemoka na sha masu tsada wani abinma sai baya mun bude muka ga meke cikin don har da kaji da ke dankare da kankara ga buhun shimkafa har uku ajiye.
Kamar ba gobe har ina mamakin hali iri na innan mu kamar ba yanzu lantana ta gama mata cim mutunci ba don haka aka diban mata komai aka kai mata Asabe hakan aka kai mata komai da mukazo dashi.
Mamakon injin tace a dawowa inna da kayan sai naji tana fadin wallahi karba zanyi ko yanzu don ba a barin mugu da makami ai.
Ba a san zafin nema ba tunda ba jikin mutum aka kurza ba wanda yaje shi aka sani kuma sunan shi ya lalace ai.
Kowan mu a dakin yaji me take fadi saidai da idanu kawai innan mu ta kallesu kowa ya shiga natsuwa a cikin dakin da alama dai warining inna ta bayar gaba daya a dakin .
Allah sarki wallahi yahanasu ko yau na fadi na mutu a gidan nan kin biyani don bani da kaico gurin haihuwan ki don yar ki zata iya rungumar ku a yanzu ta zame muna gata.
Gorin da aka zugani nasha maki na rashin haihuwan dana mijin yau ga diya macen ta jawo muna arzikin da za,a fade mu a gari muma.
Aiko Asabe bata rufe baki ba saiga lantana na fadin kai Allah mungode ma dadin mu da gobe saurin zuwa wallahi.
Yanzu ai sai muga ankai mutum makka shine zamuyiwa mutum ai murna ko a sauya mai gida kinga an rufe baki zagin diya mata a gidan nan ga baki daya.
Har sukayi suka gama ina lafe a dakin inna ban samu abindana fada ba sai faman tunane nake a kasan zuciyana.
A yanzu zancen ya jafar ya fara tasiri a zuciya don gaskiya innan mu tana so hutun da yake kira masu a yanzu.
Ba inna kadai ba har yan uwana da Abban mu shi kanshi yana bukatan kulawan daya dace a yanzu.
Kafin innan mu ta karasa girkin ta har barci ya daukeni a gurin saida akai kiran sallah a zahar kafin sa,adatu ta tayar dani daga barcin da ya dab daukeni.
Sai lokacin na fito waje tun bayan shiga dakin daga wurin rakiyan hjy da muka tafi tun lokacin ban fita wajen ba ina dakin mahaifiyar a ciki damuwa .
Nazo gida ban huta ba a can kuma ba zancen hutu ko kwanciyan hankali a gareni fara ma nan din na samu na lafe a dakin innan mu din.
Bamu samu natsuwa da inna ba sai dare baya kafa ya dauke ne muka zauna zaman hira da inna din.
Ban boye mata komai ba yadda komai ya faru a tsakani na da mami na labarta matashi a cikin daren nan ko zan samu sa,ida ga abinda nake ji a raina.
Ikon Allah Inna ta fada tana ajiyan zuciya tare da fadin wata sabuwa cakwakiyar kenan ke shirin tunkaro mu ashe.
Yanzu ita hjy da kanta take kyamatar ki da danta don kina yar tallakawa ko don wani mugun halin naki da koka boye min bansan da shi ba ?
Da sauri na dago ido duk da babu wadattacen haske a dakin lokacin inna taga kallon razanar da nayi mata alokacin .
Inna ki yarda dani da tarbiyan da kuka dorani tu farko ban kara wani hali ga wanda kika sanni dashi da farko ba ban yarda duniya ta rudeni ba inna don nasan kudi daine iyayyena komao dadewa wurin ku zan dawo zaman can din na dan lokacine.
Kafin in kara inna ta tare da fadin kimar ki da kamalanki ne ne basu kai ta hada iri da ke ba kamar yadda mafi yawan masu hannu da shuni suke da wanan akidar bawai ke dince bata so ba a zahiri a yadda na fahinci zancen.
Inna bata sona yanzu sam zama kawai nake a gidan dan hjy da danta daya jamin duk wannan abin a yanzu.
Inna har fa sata mami da yar ta suka dora min a gidan sai da shi dan nata ya biya kudin yakuma sakatar dani duk wani aiki da nake a gidan da sunan biya haka na zaune a cikin su babu walwala ko sakewa komai akan hattara da tsamgwama nakeyin shi gidan na karasa fadi a cikin kuka.
Subbahanallahi wanan wani irin rayuwa muke shirin fuskanta karfin mu ba daya ba balle na nuna jayyaya ko nace zan kwatar maki hakkin ki garesu.
Bazanyi izzigili acikin sha,anin aure ba don aure abune mai rai da Allah ya hallita kamar rayuwa idan kaddara sai anyi shi idan kuma zama ya kare ko ana so sai an rabu a tsakani.
Shine dalilin da yasa akeson musulmi ya yadda da kaddaran ubangiji maikyau ko marakyau ka yarda daga Allah komai yake.
Kuka na sakawa inna don gareta kadai na dogara da zata tsaya ta kashe wanan auren don ita kadaice nake hango gatan mu a gareta da tausayawa don Abban mu yanzu sai a slow tun shigan lantana rayuwan shi.
Da mamaki inna ke kallon yar nata a cikin tausayi da kulawa take fadin menene ne a ciki aure ne bautan ubangiji kowace mace da yadda akasin nata yake zo mata.
Idan ma wani mugun haline gareshi har yake boyewa na roki Allah a sandiyar ki ubangiji ya sauwaka mai ko menene a rayuwan shi.
Idan kuma da zuciya daya ya aureki ubangiji ya kara mashi sonki da kaunar ki a rayuwan zaman ku tare da zuri,a masu albarka.
Bazan taba ja da ikon Allah ba don haka kema nake gargadi ki da ki yadda da kaddaran ki a yadda tazo maki.
Allah yasan hikimar daya shimfida a nan ya tsameki daga cikin mu ya kaiki can cikin su kika zauna tare dasu har hakan ya faru yanzu.
To a barwa Allah sanin sa a hakan illa iyaka gobe zan turaki can gurin kawuna Inda addu,oin da zai baki sai ya taimaka muna dashi kafin nan nizan fara zuwa naimai bayanin komai insha Allahu.
Dan sheshekan kuka nakeyi kafin inna tayi shiru tana saurarena ba abida nake tunawa sai irin tsana da kiyayyana da yanzun nake hangowa a idon mami din ko yaushe.
Sai zuwa can naji inna tace yoke ai ya kamata ki hankalta tun daga yanzu ki sancewa ubangiji mai sonki ne yar nan baki da wani zabi dayafi kita godewa ubangijimu .
Dazun nan kika shigo gidan kin dai ga abinda ya faru a gidan nan shi kadai ya isheki ishara a rayuwa duk wani izzigilanci da ji da kai na lantana bai hana ta karbi abinda kika kawo a karkashin ki ba.
Ko wanan ai wani babban baiwa ne da cigaba a wuri Allah wanda yake zaton ka da komawa baya yau a wayi gari yaci ta karkashin ka.
Don haka hakkuri zakiyi kaddarar kice a hakan haka ubangiji ya tsara maki baki isa ki kaucewa hakan ba.
Don yanzu idan nayi fushi nace zan kwata maki hakkin ki da karfi da yaji na dauki mataki sai mu taru mu nunawa ubangiji ke nan bai isa garemu ba.
Haka dai inna tayi ta rarashina har barci ya dauke ni ban sani ba tun ina dan bata amsa har taji nayi shiru hakan yasa ta gane barci ya daukeni ne ta shiga nata tunanen a nan don abubuwan da take hangowa bata dai yarda ta nuna min hakan bane kawai.
Tasan ina ciki wani mawuyacin hali mai wuyan sha,ani da wanan baiwar Allah da Allah ya hada rayuwana da ita don mutum ya nuna bai kaunan ka a cikin ahalin shi abune mai wuyan sha,ani don ita kanta zaman abinda take fuskanta ke nan in badon ta kwabe tsakanin lantana da Asabe ba aka gansu a rana.
Don haka dole itama ta jajirce ta dinga yiwa yarta adduan fatan alheri ga halinda ta riski kanta a cikin shi duk da tsohuwan bata boye mata komai da take hasashe ba kan wanan auren nawa.
Don haka take son inna ta kara kwantar min da hankalina na samu tsuwa ingano mai hakan da yayi, yake nufi akaina dashi din.
Dole sai a cikin hikima da basiri inna zata iya fahintar dani manufan hakan a yanzu don hakane kawai zan samu natsuwa akan zancen.
Washegari tunda ba idar da sallah barci na koma duk daba gajiya a jikina saidai rashin barcin da bamu samuyi da wuri ba nida inna.
Can ciki barcin wani hayaniya ya kara tayar dani don muryan lantanace har kofan dakin mu tana magana kamar a cikin dakin take a lokacin.
Da mamaki na mike kome ya faru suke wanan fitina haka da sassafen nan a cikin maganan na dan tsunci zancen daya hada fadan wai ashe lantana tace bata yarda da rabon da inna tayi a jiya wanda asalima ba inna bace ta raba kayan sa,adatuce ta diban masu komai ta aika dashi.
A hankali nake gyara rigan barcin dake jikina a lokacin tare da fadin inna don Allah kuyi hakkuri meya kawo wanan zancen yanzu kuma.
Daga gefe dayan kanwata ke fadin wai shikafa aka aika mata dashi shine tace yayi maya kadan ko jiya dai ta karbi abinda aka kai matane.
Shine tazo yanzu take wanan fadan da innar mu wai sai an raba daidai ko a kara mata Abba kuma ya daure mata ginda a hakan wai a kara din.
Karbo roban ki kara mata din Allah halima wanan fitina ya kare hakana baza a karaba tayi abinda zatayi din sa,adatu ta fada a hasale.
Sa,adatu dan Allah ki bari a bata koda baku bata karewa zaiyi don ba zaku tabbata dashi ba ai har abada nafada tare da mikewa na nufi kofan dakin da lantana take tsaye.
Abin mamaki ba lantana kadai bane akofan har abban mu yana tsaye a bayan ta tare da dan yaron su rungume a jikin shi da ganinsa a ckin damuwa yake sun kwana suna fitina kila a dakin.
Buhu dayan na mika mata iyakata kofa dashi tana ganin haka tace yanzu naji magana kan dama wanda bai fita ya nemo ba yafi me nema rowa ai.
Tana kokarin jan dayan buhun da muka kai mata kofa zata tafi dana baho da aka zuba nace halima dauki na bahon ki kawai kaka ta kara.
Daya da rabi zamu tsira dashifa yayan mu kanwata Amina ta fada cikin dan marairaice murya nace ki godewa Allah da wanda kuka samu Amina.
Kinsan wanda zaku samu gobe ai,shi alheri takine barta Allah zai kawo muna wani wanda yafi wanan din data dauka.
Nayi mamakin ganin tunda safe ashe girki inna ta hada a gidan lafiyayye da zamu karya dashi da kayan miyan daya hadasu fada da lantana wanda Abba ya kawo muna da hjy.
Kowa na gidan saida ta zuba mai daga Asabe kakarmu har lantana naji tace a kaiwa dan lantana abincin ma,anade tayiwa dan lantana kara.
Wa yan nan dabi,un na inna sukan ban mamaki zakaga an mata abu saudayawa da zaran ta mayar da marta jan abu daya ya waddatar da ita ke nan bazata sake bi kan abinba kuma.
Tana gamawa wanka ta shiga a gurguje ta shirya tare da fadin zata dan fita unguwa mukai mata sai ta dawo wurin muka zauna zaman hira da yan uwana ranan sa,adatu batayi sana,a ba sai labarin abinda daya faru bana gidan suke ban.
Wanda hakan yasa na kara jina wasai kamar babu abinda ke damuna a rayuwa neme kuncin da nake ciki na rasa ga baki daya sai fari cikin daya mamaye zuciyana.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.