Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 127 of 139
Asibiti kusan a zaune yaya ya kwana a dakin sai can ya daga ya je dakin da aka kwantar da hjy ya leka ya samu suna barci ya dawo.
Ya kafa sintiri a tsakiyan ward din yana dan buga hannayen shi a cikin damuwa ya kuma koma ya zauna ya tsura min idanu na wani lokaci.
Zuwa asuba na dan motsa ya taso da sauri yana dan kiran sunana na dan bude ido na kalleshi na mayar na rufe kuma kamar ina barci a lokacin kuma idona biyu ba barcin na koma ba.
Saidai dakin da naga yana juya min yasa na kulle idanuna dan in ji saukin hakan .
Kai kai ya fada yana naushin hannu shi cikin dan uwa tare da fadin idan kuka cutawa yarinyar nan i will not spear any one in dat crimme.
A hankali hawaye dake idona suke silalowa gefen fuskana sai yanzu na dan gane abinda ke damuwa na a lokacin wani irin kukane yazo mi har yana dan jin sautin na a lokacin.
A hankali ya tako zuwa inda nake kwancen ya dan sunkuya daidai gadon yana fadin baki barci ba ke nan zainab.
Abinda nake gudan maki kenan ya faru dake tun farko ki gafarce ni zainab nasan na cuta maki da ban fada maki wanan tsarin nawa ba.
Ba a shiga dakina a kwanta saman gadona idan bana cikin dakin wanan dokane hakan shiyasa tun farko ban saba maki da shiga dakin nawa ba ma.
Don irin hakan nake maki gudu duk da nasan ba zasu iya maki komai ba a yanzu warning din ki kawai sukeyi a hakan .
Jin maganan da yakeyi a lokacin kamar almara nakeyi kafin in mayar da idona in rufe ina mai jin wani irin tsanar shi na shiga zuciyana lokaci guda.
Ba zan taba yarda a cuta maki ta bangare na ba zainab ko waye kuwa sai inda karfina ya kare don ke din amanace gareni zainab.
Insha Allahu zakiji sauki ki dawo gare da yardab ubangiji don na fada masu kowa ba zan bari ba idan sun taba min ke wallahi.
A hankali na bude bakina cikin muryan dake nuna zafin ciwo ga mutum don muryan bai fitawa mutum sosai a lokacin da yake son fadan wani abu ga wanda ke kusa dashi a lokacin irin hakane a lokacin nace dashi su waye wayan nan yaya ?
Meye hadin ka dasu har suke bibiyan rayuwan ka dani ya shafeni a yanzu wani laifi nayi masu suke son kasheni ?
Sai lokacin ya dago kai da sauri yana fadin ba zasu taba iya kashe ki ba zainab Allah ba zai basu ikon hakan ba don ya fimu sanin komai.
Ke din ba jinin daya halatta bane a garesu sun sani in ma wani abu suke so sukai maki haka ni zanyi maganin ko menene da yardan ubangiji.
Idona na runtse a hankali don jin abindaya fada tabbas akwai wani kulli tsakanin shi da wasu da ban sani ba amma kuma ai fuskan phlips abokin shi nagani a mafarkin.
Da budan bakina nace dashi your friends philips and others ko don shi nagani a wani wuri a cikin mafalki da ban san ko ina bane wanan wurin.
Kingashi ko zainab na gyada mai kai a hankali ina kawar da kaina gefe daya wasu hawaye na gangarowa daga idona a hankali.
Naji yace good zai gane baida wayau kuwa ido na mayar na kulle a hankali don nikan a zuciya nasan na gama da duniya ke nan tunda na shiga hannun wa yan nan mutane a yanzu.
Yanzu nasan kin fahinci ko meke gudana dani zainab saidai ina son don Allah idan zaki min hukunci kiyi min adalci a cikin sa don ni kaina a haka na tsuci kaina a cikin su badan nasa kaina ba.
Wanan yana cikin abinda bature ke kira da trust person yarda da shakuwan dake tsakanina dasu a baya yasa suka jefani a cikin su .
Don su a wurin su mutum bai zama dan baiwa bai kasance a cikin wani kungiya ba haka wanan shine dalilin kawai da suka halaka min rayuwa a yanzu.
Zakiyi mamaki idan nace dake su a wurin su hakan shine iya kaunan da zasu nuna min na zama tare da mukeyi.
Saidai ina son ki sani duk da sunan ina cikin su ban yarda da dokokin su ba da ake shimfidawa mutum inda na samu dama shine bani na saka kaina a cikin kungiyan ba sakani sukayi da kansu.
Don shi bature yana baka hakkin ka akan ka,ida komai ritsi kuwa ga abu dole sai sun ba mutum hakkin sa a kai.
Duk yadda suke sona a cikin su hakan baisa na yarda na sake ibadana ba don su kamar yadda da dama suke hakan idan sun shiga sai dai rauni dana samu wurun addinin nawa wanda ni kaina na sani kuma abin yana damuna sometimes.
Ina fada maki wanan ne badon ki yarda da abinda nake fadi din ba iya kuma gaskiyan ke nan nake fada maki a yanzu.
Haduwana dake shine sillar tabarbarewan komai a wurina wanda su basu so hakan ba don addinin da na juya yanzu ina yi akai akai yasa mun samu rauni sosai dasu a hakan.
Karshe kuma sai rabuwana da su taju da nabil daya kara tun zurasu suka sake jin haushin hakan da takaicina gashi a yanzu a kullun zasu ganin a kwance tare dakene a kuss dani wanda hakan yana cikin dokan mu.
Ba zamu kwanta da mace don muji dadin ta ba don su a ganin su mace haramtaciyace a wurin su dokane hakan.
Yawan adduan ki idan zaki kwanta yasa basu iya maki komai a lokacin ko jiyan dama suka samu har hakan ya faru dake wanda nasan kuma ba zasu maki komai ba sai tsorata kin da suke son suyi a hakan.
Nasan da ba wanda yasan da wanan zancen duk a kasan nan sai ke a yanzu ke din ma na yarda da sone yasa na fada maki komai don ki sani ki kuma kwantar da hankalin ki kada kiyi tunanen komai kan hakan.
Kuka nake a hankali ya mike don kiran sallah da yakeji a lokacin ko ina a cikin asibitin yana tashi yake fadin ki yi barci a yanzu idan na dawo sallah sai in kamaki kije kiyi taki sallah kada kice zaki tashi fa please ya fada yana fita daga dakin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA.FATAN ALHERI GAREKU MASU KARATU MARASA LAFIYAN MU UBANGIJI ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYA ALLAH YA KARA MASU LAFIYA DA WADATAN ZUCI ALLAHUMA AMIN, , , ,
ANTY COROFFE UBANGIJI ALLAH YASA KAFFARA NE WANAN JARABTAN DA ALLAH YA AIKO MAKI DASHI ALLAH YA BADA IKON CIN JERABAWAN SA AMIN.
AKWAI WATA BOYAR ALLAH TANA BUKATAN ADDU,OIN KU DA BAKUNAN KU MASU ALBARKA ALLAH YA BADA IKON MATA DAMU DA ITA DUKA ALLAHUMA AMIN, , , ,
Tunda na runtse idanuwana ban budesu ba ashe har barci ya daukeni ina tunane a hakan.
Hayaniyan da naji a saman kaina yana tashi a dakin yasani bude idadanu na a lokacin naga har hasken rana ya haska gari a lokacin alaman dai gari ya dade da wayewa ko .
Muryan ya mamud ne naji a saman kaina yana min sannu tare da fadin kin tashi ke nan zainab ya karfin jikin naki ?
Na bude idona tare da kakaro murmushin dole a lokacin a fuska ina dan amsawa a hankali.
Yawa na soma yi da idona ina bin wa yanda ke cikin dakin da kallo na sauke idona a kan mami dana gani can daga gefe ta tsura min idanun ta kuri tana kallona.
A hankali naga ta tako zuwa bakin gadon tana fadin ya jikin zainab da sauki ko min shigo mun samu kina barci.
Da sauki mami na fada ina yunkurin tashi zaune take fadi a cikin sauri kwanta mana ina kuma zaki yanzu ?
Cikin daurewa na soma fadin sallah zanyi mami banyi sallah ba tun dazun na fada ina mikewa zaune.
A take na mayar da idona na rufe dan jiwan da nake gani idon nawa nayi lokacin dana tashi din zaune.
Lafiya mami da jamal suka fada lokaci guda ban iya basu amsa ba sai komawan da nayi na kwanta a lokacin da sauri ina zatane mami jamal ya tambaya.
Wai sallah zatayi ta bashi amsa yake fadin ta bari mana har taji karfin jikin zuwa dan ajima sai ta tashi tayi.
Lokaci yana shigewa idan zata iya a barta tayi ya fada yana karasowa wurin duk suka bishi da kallon mamaki a zukatan su.
Zata iya mana idan basu samu galaba a kanta ba kamar yadda suke son halaka yar mutane batai masu komai ba ya fada a hasale yana juyawa.
Duk da mamakin da yayi da abinda kanin nasa ya fada baisa ya nuna ko gezau ba a hakan sai ma kokarin dukawa da yayi yana tambayana abinda nakeji dana tashi din.
Ban bashi amsa ba sai yunkurawan da nayi da karfi Allah ya taimakeni na tashi da addua a bakina ina sauke kafafuna kasan gadon na sauka .
Kamani yayi da sauri zuwa ban daki da taimakon shi har na samu nakai yafito tare da rufo min kofan na tsugunna da kyar kami nayi sarki.
Ina fitowa a kofan yake tsaye saidai duk wa yanda ke dakin a lokacin sun fita shiya kamani zuwa wurin daya shimfida sallay a dakin nayi sallah a zaune yana gefe saman kujera tare da wayan shi a hannu yana dakila.
Fadilace da sadiya sukai sallama suka shigo dakin da gudu sadiya tayo kaina ya daka mata tsawa kada ta fada min a jikina.
Fadila ko tun a kofa take fadin alhamdullahi jiki yayi sauki tunda mun sameki zaune haka kafin ta juya wurin shi tana gaidashi bai wani amsa mata a sake ba.
Bayan sun gaidani ne ya mike tsaye yana fadin barin leka likitan koya fito kada ki zuba abincin kar taci sai munji abinda likitan zai fada.
Daga haka ya mike ya fice a dakin ya barni dasu yana fita nace fadila kamani in koma saman gadon zan kwanta.
Ta rikeni na tashi muka nufi gadon saidana kwanta tana min sannu ta koma ta zauna saman kujeran daya tashi sama.
Ina nan kwance a wurin suka shigo su ukku da likita sai ya mamud da suke tare likitan ya dan duba yayi rubutun shi yake fadin ba wani matsala har yanzu saidai za a bari har anjima aga yadda na kara ji sai a sallameni mu tafi gida.
Bayan fitan likitan ya kalki fadila yana fadin zaki iya bata abincin yanzu taci tace ok oga tana mikewa tsaye don zubawa .
Da sauri nake fadin bazanci ba don Allah ruwan zafi kawai zan sha na fada ina kawar da fuskana nan ya kama min fada don me ba zanci ko kadan ba inji karfin jikina.
Rabon ki da abinci tun jiya bakici komai ba sai lokacin ya mamud yai magana a dakin yana fadin ka barta ba aiwa mai ciwo hakana a sannu ake bin shi ai.
Ruwan zafin ta hada min nace kada tasa madara haka zan sha tana dan juyawa ta dago kai tana fadin oga kaje gida tunda munzo ka huta.
Ya mamud yace lalai kan zai fi kada kaima ka rafke muna da ciwo kuma ya dan yi murmushi kadan tare da dubana kafin yace.
Mamud mu tafi wurin hjy na kara dubanta kafin na wuce gida suka fita daga dakin ya rage mu kadai a dakin na kalli inda suke zaune sunyi shiru ina fadin.
Kunzo min da wayana suka amsa da eh yana a jakkan ki da muka tafi dashi jiya gashi sadiya tasa hannu ta dauko wayan a ciki ta miko min.
A hankali na bude wayan don malam nake son kira na kalli fadila ina fadin ku dan fita ku ban wuri na min ti uku don Allah.
Da sauri suka mike suka fita na danna kiran malam din ya dauka yana fadin yau uwar gidan jafaru ce da kira da safe .
Maimakon inyi magana saina fashe da kuka inajin yana fadin subbahanallahi me kuma ya faru dake zainab bar kuka kiyi min bayani a tsanake kukan nan naki yana daga min hankali sosai wallahi.
A cikin karfin hali nace dashi malam ina cikin wani hali yanzu haka ina asibiti a kwance tun jiya ance wai banda jini.
Subbahanallahi malam ya fada a kidime tare da fadin meya kawo hakan gareki nan ma wani kuka na sake kafin in koro maganan na fara fada mai tiryan tiryan har karshe.
Wa iyazu billahi ya fada tare da fadi cikin sauri ina zuwa ki kashe wayan nace to malam nagode na kashe wayan.
Banji malam din ya kirani ba har zuwa rana hankalina kuma yana wurin kiran malam din don sai ina ganin shi keda maganin a hannun shi.
Yasa na damu da in fadawa malam din a lokacin karfe hudu likita yace ina iya zuwa gida a lokacin ban bar asibitin ba saida na shiga na sallami hjy itama din ba laifi ta samu lafiya a lokacin.
Mun dawo gida dakina nashiga nayi wanka har lokacin ina jin jikina ba karfi kamar nayi watani a kwance ina jinya nake jin jikin nawa.
Karfe shida sai ga maizube da malam an shigo dasu gidan wanan ya ban mamaki don ban san zasu zo garin ba a lokacin.
Basu huta ba malam ke fadin a kaishi wurina yana son ya ganni a lokacin aka kaisu har dakin ina kwance duk da yamma yayi a lokacin na kwantane don zama bai mun dadi a lokacin .
Yana shigo da sallama a bakin shi bai min magana ba ya fara bin dakin da addua kuswa kuswa na dakin kafin ya dawo ta kofan dakin ya tsaya ya dade yana adduan da bamu ji abinda yake fadi a lokacin.
Yasa hannu ya ciro wani dan gora da rubutu a cikin aljihun babban rigan shi tare da wani fifiken wani dabba mai dan girma yana bin ko ina yana dan yayyayafawa a dakin ko ina har zuwa wurin gado.
Sai daya gama yazo inda nake zaune din ya mikowa maizube wani gora yana fadin ku shiga bayi ki mata wanka da wanan zamu samu abin yin hayaki ko a gidan nan ?
Burner muke dashi na bashi amsa tare da yimai bayanin yadda yake yace zaiyi ai tunda yana fitar da hayakin a jikin shi.
Nayi duk yadda yai min bayanin ayi min koda muka fito basu dakin shi da yaya jafar din hakan ya bamu daman yin yadda yace ayi din maizube na fadin ai da yardab ubangiji komai zaizo karshe ke nan yanzu don sai da malam din yaje Damau yaga aminin shi kafin muzo nan.
Ni da kaina nace aban abinci inci a lokacin ina ci sai barci mai nauyi ya daukeni ban falka ba sai cikin dare sosai koshi fitsarine ya tayar dani a lokacin.
Da safe koda na tashi jiki wasai dashi kamar bani bace a jiya ban ko iya daga hannuwana a lokacin.
Kwanan malam ukku a gidan mu yana burgan gidan damai gidan gaba dayab mu har mami da ya mamud sunzo ya zauna dasu sunyi maganan siri da jafar din dasu .
Wanda ban san abinda suka tatauna ba a lokacin nidai naga mami ta canza min yanzu tun a asibiti naga wani canji a gareta a yanzu gareni.
Washe gari su malam sukai min sallama suka tafi bayab yaja mun kunne koda wasa kada in fada wa wani a gida cewa sunzo nan Abuja .
Kuma haka din nayi duk da inna na kirana mu gaisa ban fada mata ai malam yana wurina a abuja ba.
Duk da malam ya tafi haka baisa mun daina maganin daya bamu inayi ba a kulun har kwanakin daya diban muna din muyi a tare dashi mukeyin maganin kullun kafin mu kwanta barci zamuyi wanka da hayaki sai adduan kwanciya din daya bamu safe da yamma.
Alhamdullahi zance a yanzu banda wani damuwa a jikina ko na tsoro a yanzu tun bayan zuwa malam wurin mu din.
Ana sallamo Hjy gidan mu akayo da ita don can tace a kaita kafin ta koma gida idan ta dan murmure jikin nata.
Mami bata so hakan ba saidai ba yadda ta iya da hakan dole ta barta taje gidan namu ta zauna hakana yayin da mu kuma hakan yai muna dadi sosai don son da mukewa tsohuwar.
Sabon zancen daya taso muna kuma a kan zuwan hjy gidab mu shine dawo da kwanan mu wuri daya da yaya a yanzu don zuwan hjy.
Don tun faruwan hakan ban kara komawa dakin na kwana ba sai yanzun da hjy tazo gidan namu zata kwana biyu damu.
Don sa idon tsohuwar duk da a daki take zama nan take wuni bata fitowa ko falon gidan sai dai kuma suna tare da mama Ramatu a gidan namu.
Wace mami tasa ta biyo mahaifiyan nasu su zauna nan tare da ita don halin jikin nata da take ciki a yanzu.
Hakan yasa a yau dole mu hada daki da yaya din wanda kowan mu na cike da tsoron hakan a cikin zuciyar shi tunda bamu san mai hakan zai haifar muna daga baya.
Na shiga dakin da sallama yana kwance yadda ya saba kwanci wani lokaci ya daga kafa daya ya dora hannu saman fuskanshi ya kare da hannu daya.
Yana jin sallamana ya dan dago kadan ya kalleni ya mayar da kanshi a yadda yaken na tako a hankali zuwa bakin gadon kamar a tsorace nake.a lokacin.
Zama na danyi a baki gadon ban karasa hawa ba gaba daya yake fadin idan kina ganin hakan da matsala ki koma part din ki ko hankalin ki zai kwanta nima ina dauting din hakan a yanzu ban son a kara samun matsala again.
Kada su mami su kara zargina don mun kwasa dasu wacan satin suke fadin wai nine na bayar da jinin ki a wurin tsafina.
Jin hakan yasa na juyo da sauri ina kallo inda yake kwance din yana nan yadda yake yake maganan shi hankali kwance.
Waya fada mata hakan na tambayeshi da mamaki a fuskana shine abinda ya ban mamaki don maganan yana kama da wanda muka sani din don haka yaya akayi suka san da zancen.
Nasan baki fada masu komai ba kan hakan saidai idan zargi sukeyi ko kuma sunji a wurin malaman su don nasan kowa na shige shige a kaina a yanzu.
Wanda ni nasan da hakan ba yau ba sai dai duk bata lokacin su sukeyi ga hakan don hanya fita ciki dayane nina sani idan lokaci kuma yayi zan daina din da yardan Allah.
Wani irin kallo nayi masa na tuhuma duk da bai kalloni ba yasan nayi masa sai naji yace yes matakin da basu so zan dauka shi zai rabani dasu lafiya.
A hankali na jingina bayana saman filon dake gefena nakai kwance ba tare dana iya furta mashi komai ba a lokacin.
Don a yanzu ya daina bani tsoro ko mamaki don sai nake ganin a gadarance yakeyin abinsa kai tsaye duk da yasan hakan ya sabawa addinin mu sosai.
Sai dai maganan malam ce da yake fadin in bishi a sannu don bayin kansa bane hakan zanga kamar komai yana yinsa a cikin sani ne saidai asirine dake aiki a kansa kawai ba a gane hakan ne ko shi kanshi bai gane hakan kai tsaye.
Sai idan an bishi a sannu zai zo ya daina komai wanan ne suka tatauna da mami da malam din ashe da zasu tafi bayan malam din ya fada mata komai akan dan nata da a yanzu ta yarda da komai da ake fada akanshi.
Ba wanda ya sake wani magana a cikin mu har barci ya dauke mu a hakan ko dadin barci ne ya kawo mu kusa da juna kowan mu ya dora hannu saman jikin dan uwa oho.
Sai dai mun tashi da asuba mun samemu a hakan nice ta farkon falkowa nayi mamakin gani shi rungume dani yau abinda bai taha faruwa a tarhin mu cikin jin dadi irin hakan.
Ban gama mamaki hakan ba ya falka shima da sauri ya dan ja baya ya zabura wanda hakan yasani na kara mirginawa gefe daya.
Ganin na matsa yasa shi sauka da sauri ya zauna a bakin gadon na dan wani lokaci kafin ya mike ya shiga ban daki nabi shi da kallon mamakin yin hakan.
Bai dade ba ya fito daga bayin na shiga wanka nayi na daura alwala ina mamakin wanan bakon yanayin yau da nagani a garemu.
Har na fito ban daina mamaki hakan ba ina idar da sallah na koma na kwanta don gari bai gama waye ba a lokacin.
A cikin barcin ne nayi mafalkin ga wasu nata kwasan kayan su suna tafiya kamar masu barin gari ina tsaye ina kallo su sai da suka gama suke dago hannayen su na duba sai banga kowa ba kuma.
Kakan maya na gani tsaye da abu kamar sanda a hannun ta tana min murmushi na mayar mata itama din tabi bayan su suka bace mi tare.
Tashi nayi firgigit ina kallon ko ina na dakin sai lokaci na gane inda nake kwance a dakin yaya nake har lokacin kwance .
Juyawa nayi shine zaune yana aiki a cikin laptop din shi ga tea a gefen shi yana tashin turin hayaki.
Na mike na saka hijab gaidashi nayi na nufi hanyar fita daga dakin naji ya dakatar dani yana fadin mafalkin me kikeyi kuma haka da safen nan.
Dan kallin shi nayi ban furta mai komai ba nasa kai na fice daga dakin kai tsaye zuwa dakina .
Idan ka ganni a yanzu zaka gane ina a cikjn damuwa don yadda na rame na danyi duhu ba sosai ba dai.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.