Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 71 of 139

🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

6️⃣0️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

LITTAFIN KUDINE DAN DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA SHI HAKKI BAIDA KADAN MUSULMIN KWARAI KE GANE HAKA, , , ,

Kwana biyu na rasa gane mai ke tsakanin su yaya dan ko yaro yasan akwai matsala a tsakanin su don ya jamal idan ya fita baya dawowa gidan sai dare.
Daya shigo kuma ba,a sake ganin shi sai wata safiyan ko ance ya tsaya ya karya zaice yana sauri ne kada hjy taga ya dade zai karya idan ya isa asibitin.
Ashe mama Ramatu ta fahinci hakan a tsakanin sai gashi ta kasa hakkuri muna zaune muna karyawa bayan fitan ya jamal bada dadewa ba tana tambayana .
Zainab niko sai naga kamar yaran nan akwai abinda ya faru a tsakanin su kwanan don gaskiya ba haka na saba ganin su mussanman ma shi jamal da jafar akwai shakuwa na sosai a tsakanin su.
Kofin dake hannuna ina dan kurban ruwan shayi na aje tare da fadin mama nima na kula da hakan saidai ban tsamani abin yayi nisa haka sosai ba a tsakanin su.
Gaskiya suna da matsala don shi jafar baya ko zancen kanin nasa idan ya fito bai ganshi ba da safe idan da dane da mukazo baya karyawa sai ya nemi dan uwansa sun zauna tare.
Ke mijin ki bai fada maki abinda ke faruwa bane tsakanin su da sauri na girgiza kai ina fadin ba muyi wanan zancen dashi ba gaskiya.
Tsuki tayi tare da fadin ina zakuyi wanan maganan don ko yaushe fuskan shi a daure idan bashi yaga daman yin raha don kansa ba.
Zanwa jamal magana idan ban fahinci komai ba zan fadawa hjy ko zata san maike faruwa a tsakanin su haka.
Nidai ban kara tofa komai ba naci gaba da kurban tea din dake hannuna a hankali har nakai rabin kofin na aje.
Yau ma banga shi jafar din ba ko sakkon fita yayi ne don kwanakin nan naga da wuri yake fita sai dare kuma yake dawowa wani lokacin ma bamu haduwa.
Ina ganin kamar ya fita tun dazun don yace yau yana da meetinga office na shara mata karya ina Allah Allah kada kuma ya fito ta gane karya nayi mata ashe.
Sai Allah ya taimakeni ashe ya fita din don na sara a gaba gashi ranan bamu zuwa asibiti duba hjy don tana bukatan hutu don alluran da akai mata tana son dan hutu ya sa sukai muna gargadi da hakan.
Don haka bayan karyawan mu a falo muka zauna da mama ana dan hira da kallo wanda kusan hiran na mutanen kasan da muke muke zancen irin shigan su da yadda suke magana kuma a cikin sauri.
Can mama ta fara jefo min zance kan zaman mu da yaya sai na rasa amsan da zan bata lokaci guda don haka kawai na dan daure fuskana ina dariyan yake.
Amsan da ban bata ke nan din na gane nugun cikina take son tayi taji wani abu a dangane da zaman mu ko shi kanshi yaya din .
Ganin naki bata amsa yasa ta kawar da zancen da fadin ai ban tsamani hjy zata barku ku koma a tare damu ba don naji taja fada tun kafin tafiyan nan wai ya kamata ace kin biyoshi nan kema, sai ku zauna tare a nan.
Amma mama ni nafi son in zauna Nigeria don nan din babu wanda na sani babu dadin zama a kasan nan ga baki daya wallahi.
Budan bakin halimatu dake kallo kamar tana jin yaren su sai cewa tayi amma dai anty aida mu zauna nan din tunda mijin kima yana nan ai inna fa tace kada ki yarda mijin ki yayi nisa dake.
Da sauri na kalli halimatu din ita kanta tasan irin hararan da nayi mata sai ta koma ta kwanta da sauri saman kujeran da take kwance da farko daga haka bata kara jefa muna baki a zancen mu ba .
Barci ne ya dauki mama don haka hiran namu ya tsaya a nan ina zaune sai faman tunanen maganan da mama ta fada min na rashin jittuwa a tsakan yan uwa biyu da basayi a yanzu.
Tunane nake ko a sanadiyana suke wanan fitinan indai hakane kuwa zan tun kari ya jamal da yadaina damuwa da zancen mu don nima hakan yayi min daidai wallahi don ni har yanzu tsoron ya jafar din nakeyi da ganin girman shi akoda yaushe.
Da wanan tunanen har lokacin sallah yayi na tayar da mama do muje muyi sallah kads mu shagala don a rayuwana bana yarda inyi wasa da lokacin sallah ko kadan.
A gurin dana sallame sallah nayi zaune ina ci gaba da tunane a raina na yadda zan tunkari ya jamal din karshe dai na daure dole in hakan garesu a yanzu kada hakan ya kawo masu matsala.
Ban fito ba sai bayan da nayi sallah la,asar koshi na fito ne don halimatu da har lokacin banga ta shigo dakin ba tunda tayi sallah azahar ta fita.
Bata falon danake tsamani don haka kai tsaye na nufi dakin mama da sallama tun kan na tambaya na hango halimatu din kwance tana barci saye da hijjab din datayi sallah.
Wayancewa nayi da gaida mama tare da tambaya ko taci abinci kuwa tace tun dazun mukaci da mutumiyar tawa aini naji dadin zuwa da yar nan kasan tunda gata tana debe min kewa sosai wallahi.
Mama tana dai damun ki da surutun ko yaushe indai halimatu ne shiyasa suke dasawa da ya jafar idan yana gari ai.
Yarinyar tana da shiga raine mahaifiyar ku gaskiya tana ba yaro tarbiyab daya dace wallahi kunyi sa,an uwa tagari ba kadan ba.
Mama mu gode kamar yadda anty fadila tace in dinga fada idan wani ya yaba wani abu nawa daya shafeni.
Yanzu mama yau ba zamu je gun hjy ba ke nan sai ranan da suka bayar za,a ganta yayi wanan kasa gaskiya suna da doka mai tsauri wallahi.
Ai inda sukafi kasan mu ke nan wurin sanin aiki da canne kyale duk wanda zaizo zasuyi a dameta sai idan an hadu da likitan da yasan kansa zai dan tsawatawa mutune su daina shiga.
Dan wanan hiran da mukeyi da mama yasa naji har zuciyana ya dan sake don hira sosai mukayi da ita har lokaci yaja bamu sanda hakan ba.

Zaune a office din shi ya mike kafafuwan shi saman table din dake gaban shi yana rike da kanshi da hannu daya irun zaman da yayi yana nuna yayi zurfi a cikin tunane.
Don alal hakika yana cikin damuwa da maganan da sukayi da dan uwan nasa kwanakin da suka wuya har ranan ya kasa samun natsuwa a tare dashi.
A karo na barkata yana kiran layin kanin nasa yaki ya daga a karshe ma sai computer ke fada mai wai layin na busy ko yaushe idan ya kira.
Yanzun ma daya kira computer din daine ke fada mai yadda ya saba fada mai layin na busy haka yasa yagane dan uwan ya sashi a black list din wayan shi.
Kararawan office din nasa ne yayi kara hakan na nufin akwai mai son shigowa office din a lokacin.
Da kamar ya kyale maishi ya koma ya dai daure ya ya danna alaman ba mai so shigowa daman ya shigo.
Yana budewa suka baiyana mai su uku aboka shi ne tun na kurciya da suke shashancin su a tare wanda kusan ta sanadiyar sune ma ya samu aiki a kasan nasu a yanzu saboda hazakan shi da kuma basu son rabuwa dashi don zaman shi star a cikin su.
Ko wanin su yana cikin shiga ta alfarma kamar yadda suka saba shiga saidai na kananan kayane irin suit.
Ya matsa kadan daga kofan ya basu wuri don su shigo daga ciki basu shiga ba illa kokarin hugging dinsa da sukayi daya bayan daya.
Kafin su wuce suka karasa cikin office din kujerun dake officen din zube gefe daya suka zube a sama.
A sabule ya biyo bayan su zuwa ciki shima ya samu daya daga cikkn kujerun ya zauna a kai dayan mai suna philis yake fadin ya labarine na ganka a haka kuma.
Sai dayan ya karbe da fadin kwana biyu bamuga ka leko club ba yasa yau na gaiyaci friends muzo mu duba ka ko lafiya.
Jafar din bai amsa kowan su ba illa mikewan da yayi zuwa wurin firdge din dake office din ya bude tare da fito da kananan kwalabe ya dire a gaban su ya juya ya dauko kofuna hudu ya dawo inda yake zaune da farko ya zauna.
Ido ya zuba masu mai nuna alamun shi a gajiye yake ba zai iya zuba masu abinda ke cikin kwalban ba a lokacin.
Kallon shi dayan da baiyi magana ba tun shigowan su yayi yana fadin cikin kulawa wai ya nagan ka hakane gaba daya ka birkicewa sanin ka damu.
Jafar din ne ya dago idanunsa da suka kade sukai jawur alaman yana cikin tashin hankali dai sosai.
Mikewa yayi ya nufi wurin window din office din nasa ya zuge wani haske ya baiyana a office din lokaci guda ya gyara tsayuwan shi yana kallon motocin dake wucewa kasan office din nasu.
Binshi sukayi da kallo tare da mikewa suka nufi inda yake din tsaye don da alama jafar din baison damuwa cikin halin da yake ciki din a lokacin.
Ji yayi daga bayan shi a dafashi hakan yasa shi juyowa ga wanda ya dafa shi din cikin su gaba dayan sune a tsaye a bayan shi suma fuskansu ya nuna sun shiga damuwa kan damuwan shi.
Whatff bro wai meke faruwane dakai haka ka fada min damuwan ka mana ko zamu samu mafita akan matsalan dake damun ka ?
Dan dariyan yake yayi yana kallon su kafin ya girgiza kanshi yana fadin banyi tsamanin zaku iya min amfani ba a yanzu don wanan family issue ne ba maganan ku bane ko na wani.
Da matsalane dakai da family din kku ke nan a yanzu ko hakan yana da nasaba da zuwan yan uwanka da tj yace sunyi a gidan ka akan sanadiyar kakanka da bata da lafiya wai ?
Da manaki ya juyo yana kallon su watau taju har ya kasa hakkuri yakai karanshi ke nan a wurin su yanzu wanda shine dalilin zuwan su ashe ?
A dan zafafe ya buda baki da kyat don ranshi ya gama baci dasu yana fadin oh ashe kunzo ne yanzu kuyi min fada ke nan ?
No no no ka fahince mu jackson munzo nan ne yanzu a matsayin abikan ka bawai munzo muyi wani maganan daya shafi tj din bane.
Nima ai a yanzu nafi ma sha,awan ka samu sabon dan hannu dan shi tj din kakai shekuru dashi kuna harkan nan.
Hannu ya daga mai tare da wani irin tsawa yana fadin stop that nose's jooo, wuu bana cikin mude din wanan zancen a yanzu don zuciyana a jagule yake da komai.
Kallon juna sukayi kafin dayan yace dashi ko zaka samu fita yanzu muje kadan sha wani abu ko zaka samu relief a zuciyar ka ?
No ba bazan iya shan komai a yanzu ba don gidana a cike yake yanzu da family dina shan wani abu a gareni yanzu hadarine sosai.
Zaka iya don ba bakon abu bane sha a gareka don haka ka daure kawai mu fita yanzu kadan samu relief a rayuwan kan ko tunanen ka da damuwan ka zai gushe maka na dan lokaci ka koma daidai.
Tun bai yarda da hakan ba har yakai ya yarda ya biyewa son zuciyar su sukaci karfin shi akarshe suka fita tare zuwa inda sukan hadu su hole.
Ranan don bai cikin dadin rai shi ruwan kwalba yaita dinkirawa cikin sa yana kuma jan coicane har ya fara fita cikin hayacin sa.
Da haka har ya raba dare a waje cikin mayen kuma yajawo motar shi zuwa gida don shi din dan hannu ne sosai a wanan harkan.
Ina dakina da nake kwana a kwance na kulle kofa na dinga jin kamar a dukan kofan duk da nasan kofan a bude yake don bani na saba rufe part din ba .
A cikin daurewa da fargaba da tashin hankali na fito a cikin sanda zuwa falon part din babu tantama kofan ne ake duka da karfi.
Allah ya sako min wani dauriya na nufi kofan na bude saidai abinda na gani shine yafi tashin hankalin da nake ciki.
Don ya jafar ne a cikin maye yake dukan kofan gashi rataye da corth din rigan shi a kafadan shi sai layi yakeyi.
Innalillahi wa,inna alahim raj,un na ambata tare da da duban bayan shi ko akwai wani a tare dashi ko wani a falon sam na manta da darene sosai lokacin kowa ya shige part din shi ya kwanta.
Ina can ina tunane ji kawai nayi ya fado min a jiki yana fadin take me to your room zee i want sleep now.
Gabana ne ya fadi jin shi a jikina da nayi lokaci guda ya kara fadi cikin wani murya na maye take me to your bakiji ba ne ?
Ni kan ina zan iya kama mutum kamar ya jafar mai karfi haka da jin koshi a tare dashi a cikin dabara na samu na kaishi dakin nawa ya zube da takalman shi da komai saman gadon ya kwanta rub da ciki ba bata lokaci naji ya fara sakin nasari.
Da sauri na dafe bakina tare da sakin wani irin kuka lokaci guda kamar daga sama naji yana fadin are you crying zeey ?
Dago kai nayi na dan kalli inda yake kwance har lokacin yana kwance a yadda yake din ba tare daya motsa ba yake wanan maganan tashi nayi na sawa kofan dake bude key.
Ban daki na nufa a can na raba dare ina darza kuka a cikin tashin hankali sai maimaitawa nake ya jafar dama dan giya ne ashe.
Don babu tamtama nasan yadda yan giya suke mayensu idan sun sha don muna da yan giya a kauyen mu idan sun shawo muna kanana zamu bisu muna waka sunyi marisa sun sha kwaya har sai manyan gari sun kore mu zamu bar mutum.
Ashe nima zan auri mashayi da zai rika min marisa a gida ina kallo a cikin tashin hankali da fargaba.
Yanzu ni yaya zanyi wani irin hukunci zan daukarwa kaina kan zama da mashayi a gida daya ya zama dole gareni tun ban makara ba insan inda dare yai min daga hannun ya jafar din.
Dama abinda mutane ke yawan fada min kalman inyi hakkuri da hakayan sa da zan gani nan gaba ?
Dama ashe sun san komai suka boye min shima yasan yadda yake ya aureni a hakan don kawai ya cutawa rayuwana ke nan.
Dama wai mami tasan danta haka yake kuwa har ta tsaya tana nuna min wanan kyamar don kawai ina yar talaka ni ko ina yar talakka ai talaka yasan mutuncin kansa da kuma abinda Allah ya hanemu yi.
Gudawa daga garshi ne yazauna min a zuciyana saida kuma ta ya zamu iya gudawa yanzu daga kasan nan tunda shiga jirgima sai idan mutum ya shiryawa hakan.
Ina ko yaya zanyu zanyi ne don mu gudu dani da kanwata daga hannun wanan mashayin tun baikai ga illanta min rayuwa na ba.
Haka nayi rabin kwana a cikin makewayin can na dauro alwala na fito ashe ina ban dakin anyi ta dukan kofan ina ban daki a lokacin banji ba.
Ashe taju ne ya falka yaji dukan kofan da akeyi kamar a cikin mafalki kafin ya nemi tufafi ya saka a jikin shi har mun nufi dakina kamar yadda ya bukata in kaishi dakin nawa.
Ya fito bai ganshi a waje ba ya nufi kofana yana duka don yaji kamshin turaren a falon ya dade yana dukan kofan nawa ba,a bude ba har ya hakkura ya koma daki .
Ranan ba karamin hauka yayi a dakin ba shi kadai dan ya tarwatsa kayan dakin da dama yana hauka wai mun kasance a tare da yaya a daki daya yana zaton wani abu zai wakana a tsakan nin mu ke nan idan mun kebe din mu kadai.
Har washe gari ya jafar din yana kwance bai falka ba ni kuma ina takure a wuri daya naci kuka har idanuwa na sun canza kala don kukan danasha tun dare har zuwa safe ban runtsa ba ga barcin da ban samu ba shima yana barazana a idona.
Karfe taran safe a lokacin nasan su mama sun tashi ko dan ita ta saba fitowa tun safe a gida ko nan din ma da sunyi wankan safe sukan fito falo su zauna.
Ina cikin wanan tunanen lokaci guda naji ya motsa sai kuma ya sake komawa ya lafe ido na tsura mai daga inda nake zaune din a takure.
Can kamar wanda aka tsikara ya mike zubur tare da dafe goshin shi yana murza idanun shi lokaci guda kuma ya bude su ya fara bin dakin da kallo.
Zubur naga ya sauka daga kan gadon tare da karewa kanshi kallon mamaki har lokacin bai ankara dani a inda nake a zaune ba .
Zama ya koma yayi bakin gadon tare da jan wani irin uban tsuki lokaci guda kafin kunnuwa shi ya fara jiyo mashi sautin kukana a inda nake takure.
Da sauri ya mike tsaye tare da nuna ni da yatsa yana fadin ke ke lafiya na ganki haka mske faruwane wai ?
Ya akayi nazo dakin nan wai a nan dakin na kwana kome juyawa yayi ya dan kalli gadon na dan lokaci guda tare da juyowa gareni ya sake kallona yana fadin .
Wai wani abu ya farune kike wanan kuka haka ki fada mi ina tambayan ki kin yi shiru jin da yayi banda lokacin bashi amsa yasa shi jan wani itin uban tsoki ya duka yana daukan riganshi dake saman gadon.
Kai na dago ina kallon shi tare da mamakin shi wai yana nufin baisan abinda ya aikata bane a daren jiya ko me yake nufi da wanan basarwan ?

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.