Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 70 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA
[13/02, 21:24] +234 706 064 0038: 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5ï¸Â⃣9ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA DARI UKUNE KUDINSA DON ALLAH DON SON ANNABI KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH.
Dakin na mayar na rufe kafin in koma in kwanta a takure a wuri daya saman gadon ba mama Ramatu kadai ke tsoron wanan gidan ba harni kaina tsoro gidan ke bani don girman shi.
Wanda zuwa yanzu ban gama tantace cewa gidan ko mutum nawa ke cikinsa ba komai kan yaji na alatu saidai gareni hakan duk raggagene a idona.
Don a yanzu dai na fara fahintar akwai wani boyayyen al,amari da ya jafar din yake boyewa mutane wanda kuma dan uwan shi yasan da wanan zancen a yadda yai min magana dazun kafin mu shigo daki.
Koma meye ina rokon Allah ya kara tsareni daga fadawa cikin halakan shi don ni zuciyana yafi tsaya min da shan jini kila yakeyi.
Idan ba haka ba ta yaya mai shekaru kamar ya jafar zai tara wanan arziki haka a duniyan nan .
Mutum nawa yazo ya sama a duniya suna neman kudi fiye dashi basu tara hakan ba wani irin tsorone ya lulubeni lokaci guda ni kadai a dakin.
Can barci barawo ya fara fisgana naji kamar ana dukan kofan dakin da nake ciki a dan firgice na bude idona na saurara da kyau.
Kofan ne ake kwankwasawa ba karya kunne ke min ba saida aka kwankwasa kusan sau uku na mike tsaye a cikin kyarman jiki nakai kofan tare da tambayan waye ?
Ki bude kofa kin tsaya kina tambaya a ciki rawan jiki nakai hannu na bude kofan daga ciki shine a tsaye yana saye da kayan barci a jikin shi yana kare min wani irin kallo da bansan na maye ba.
Bayan sa nabi da kallo kamar ina tunanen zanga wani tare dashi ya taka zuwa cikin dakin yana fadin da a haka kika kwanta ba tare da kashe wuta ba ?
Kasa nayi da kaina ina wasa da yan yatsun hannuna da nakejin kamar suna taimaka min wurin kare kaina daga abin sherin daya zo min a lokacin don zuciyana ta fara zargin sako.
Kizo ki zauna magana zamuyi dake da fatan zaki fahince ni ya fada yana mai bina da kallo inda nake tsaye.
A rude na kai kasa ina fadin don son da kakewa manzo ya jafar kada ka cutar dani kamar yadda kaiwa iyayyena alkawari hakan kafin ka daukoni daga gidan mu.
Yarda da amicewa yasa suka bakani da kuma girman mami da suke gani ga idon su don Allah kayi hakkuri bazan kara ba .
Zaune yayi sororo da mamaki yake kare min kallo tare da sauraren abinda nake fada mashi din a cikin tsoro.
Cikin karfin hali ya iya furta zainab wai meke damuwan kine haka naga a tsorace kike dani tunda muka sauka garin nan .
Ko kema kin fara daukan zancen mutanen me a kaina yanzu ki zo ki zauna magana nazo muyi dake don Allah ban kuma son ganin wanan hawayen da kike zubarwa tun safe a gidan nan yanzu.
Jin abinda ya fada yasa na dago ido na kalli fuskan shi babu wasa a cikinsa ko kadan a lokacin yasa na dan tako zuwa bakin gadon nakai kasa zaune.
Kai kawai ya girgiza tare da bina da wani irin kallo kafin yace ki saurareni da kyau kiji abinda zan fada maki yanzu.
Kindai san bamu kadai bane a wanan gidan yanzu akwai mama da jamal sai kuma hjy dake asibiti kafin ta dawo gidan nan ko ?
Daga inda nake zaune na gyada mashi kai a hankaki yace good abinda nake so dake shine yanzu kin daiji maganan da mama Ramatu tayi dazun wurin cin abinci ?
Kai na sake dagowa na kalleshi gabana sai faduwa yake lokaci guda don bansan abinda zai fada ba kan maganan mama din.
Yace kokin manta da abinda ta fada na a matsayin ma,aurata muke don haka a daki daya zamu zauna dake right ?
Na gyada mai kai a tsorace alaman eh nagane yace toh don haka zan baki zabi duk wanda yafi maki sauki zaki dauka a ciki.
Na farko zaki dinga zuwa dakina da sunan kwana a can dan kaucewa idanun mama tunda ta fara wanan maganan ina zargin ko mamine ta sakata saka muna ido a gidan mu.
Sai zabi na biyu ko ki bar kofan ki a bude zan dinga shigowa karfe hudu na asuba yadda zata dauka a nan gurin ki na kwana tare dake .
Ido na sake zubo mashi lokaci guda don jin abinda ya fada din ya gane me nake nufi sai naji yace indon ni ki saki ranki don mata basu a gabana ko kadan .
Do bantaba daga ido na kalli wata mace da sunan sha,awa ba a rayuwana saidai inwa mace kallon dayan biyu shine ko in kalleta a matsayin yar uwa a gareni ko kuma abokiya kawai ni haka rayuwana yake.
Don haka zuwanki dakina bashi zaisa wani abu ya kasance a tsakanin muba dake zuwa kawai zakiyi don kaucewa idon mama da sauran mutane.
Ajiyan zuciya na sauke lokaci guda ta yadda har yake iya jiyo sautina daga inda yake zaune baki ya mere min tare da fadin wani kika zaba yanzu.
Na amince na bar kofana a bude ya tareni da fadin baki gudun mama ta gane wanan din plain ne muka shirya hakan dake ?
Sai nayi shiru kaina a kasa don haka ni zabina shine ki je can part dina zaifi min kwanciyan hankali don ba daki daya bane a gun saiki zauna a cikin guda hakan yayi maki ko ya kika gani.
Yayi min na fada ina maidana sanin zuwa wanan tafiyan da hjy ta saka ayi dani ina zaune kalau a gida a cikin kwanciyan hankaklina.
Ya mike tsaye a daidai lokacin tare da fadin sai ki tashi mu tafi part dina a yanzu saidai ban son sa ido ga duk abinda zajiji ko ki gani a can din wanan ba hurumin ki bane kinji.
Ya fara tafiya ni kuma na kasa tashi don jin irin dokokin daya tsara min wanda nasan suna da wuya in iya ketare su duk lokaci guda.
Jin ba motsa daga inda nake ba har yakai kofa ya jiyo gareni yana fadin ki tashi mana kinyi zaune ko baki fahinci abinda na fada bane yanzu ?
Da sauri na mike na dauki hijjab dina da zanyi sallah dashi nabi bayan sa kofan ya rufe da kansa muka nufi part din nasa.
Tsaruwa iyaka ke nan dan an narka dukiya wurin hada part din kamar wani aljannan duniya wani daki ya bude min muka shiga yake fadin nan yayi maki ?
Kai kawai na gyada don a tsorace nake da za ai min ihu koda kadan ne zan iya sake fitsari ko in ruga da guda a yadda nake tsorace.
Zaki iya yin komai iyaka dakin nan daga haka ban yarda ki leka ko ina ba idan kin shigo dan dama da rana kina da right din shiga ko ina na part din nan daga haka ya fita naja wani irin ajiyan zuciya tare da bin ko ina na dakin da kallo.
Na gano inda bandaki yake na shiga na dauro alwala don in gabatar da sallah saboda barci ba nawa bane kuma yanzu ya zama dole in kai kukana a wurin Allah maji rokon bayin sa.
Ban yarda na gusa daga kofa ba nan a kasa barci ya kwashe ni a gurin da nayi sallah tare da jera kirari gun ubangiji mahalicci ina mika rokona garesa.
Rashin barcin da ban samu da wuriba yasa har na makara ga sallah asuba sai da rana ya haskani ta window dakin na tashi ina sallati na nufi ban dakin da sauri.
Ban fito ba saida na gabatar da sallah a kofa mukai kicibis dashi a cikin shirin sa naja baya ina gaida shi da kwana ya amsa min a dake kamar bashi ba kuma.
Dakina na nufa sai dana kusa na tuna da dan makullin dana aje a dakin don haka na nufo don na dauko a kofan muka hade da taju dake fitowa shima a cikin shirin shi.
Ban ko tsaya gaida shi ba na wuce dakin ya bini da wani iri kallo nidai na shige na dauko key din na fito na bude dakina na shiga.
Zuciyana fam da tunanen me kuma ya kawo taju part din sa tunda safe haka ban tsaya ba na fada ban daki nayi wanka na fito na shirya a cikin wani dogon riga baka ta mutanen kasan Egypt mai hannu shara shara rigan barci ne fam a idanuna don haka na kwanta don in rage nauyin da idona yayi min na rashin samun barci.
Barci sosai ya daukeni lokaci guda saida zasu karyane ya leka dakin nawa ya sameni ina rankon barcin da ban samu nayi ba da daren.
Baiso ya tashini ba saidai don asibitin da zamu gurin hjy dole yasa ya tayar dani din ta hanyar dan bubuga nin da yayi na falka dan razane.
Ki tashi ki karya zan kaiku ku duba jikin hjy ne yanzu ya fada har lokacin babu walwala a tare dashi ban tsaya bin ta nasa ba na shiga bandaki na kewaya na fito na samesu a dining zaune nima na zauna tare da gaidasu da kwana.
Kai kekan ai garin nan yayi maki barci haka kamar mai sabon ciki kodai dan nawa ya aje kwansa ne bamu sani ba.
Fuskana na daure don na fahinci me maganan ta yake nufi don haka ko idona ban dago na kalli wurin da take zaune ba.
Har lokacin da muka gama aka fito zuwa asibitin wanan karon bashi ke jan mu ba don yace akwai inda zai tafi zai samemu a can asibitin.
Mun samu hjy tana barci saidai bamu dade a dakin ba ta falka daga barcin muka shiga yi mata sannu da jiki tana amsa muna a hankali.
Ya Jamal ne yake fadin ko yazo yaja mata kafan da aka daureshi da wasu karafuna tace tunda kafi dan uwanka rashin tausayi.
Shida ya kawoni nan ban ganin kowa ko sallah asuba yanzun haka ban samu yinsa ba na rasa yadda zan masu bayanin ina son inyi sallah tun dazun.
Har muna hada baki wurin kiran subbahanallahi nida mama Ramatu mama tana fadin ashe bayi ke nan idan ba ibada shi bai fada masu idan lokacin ibada yayi su taimaka maki kiyi ibadan ki ba.
To ina nasani yar nan ni wanan abin ai ya koma min ciki yanzy kan ace mairai ba zaiyi ibadan sa ba yana kwance haka sharkaf.
Fita ya jamal yayi sai gashi sun shigo tare da likita yana masa bayanin ba za a bar ruwa ya taba kafan nata ba sai bayan kwana uku don hakane ma ake mata wanka a kwance.
Nan dai ya dan kara bayan nan shi ya fita ina zaune nayi tagumi can na nisa nake fadinb hjy ko za a kawo maki dutse kiyi niyar taimama akan sa.
Haka za a yi yar albarka kinga abinda yafi ke nan gareni yanzu ya jamal ya fita ya dan dade kafin ya dawo dauke da wani dan dutse a hannun shi karba nayi na shiga ban daki na sanke shi da kyau na fito dashi .
A natse tayi komai kamar yadda sharia,a ya fada har sallah a kwance tayi don nasan hankalinta ba zai taba kwanciya ba idan ba sallah ta samu tayi ba.
Mun dade a wurin hjy har karfe dayan rana kafin yaya din yazo tare da wanan bindin nasa yana biye dashi a bayan shi kamar jelan shi.
Ni yanzu yakai ma bana son sam naga wanan mutumin don haka kawai nakejin na tsaneshi a cikkn rayuwana na kula bani kadai na tsani wanan mutumin ba har ya jamal ma ya tsanesa sosai don ban taba ganin lokacin da suka gaisa dashi ba
Bayan tambayan jikinda yayi ne yake dan duba jikin nata musaman kafanta dake daure da karfe yace ya kike jin jikin ta dan dago tana fadin da sauki sosai saidai sallah da bata samun yine a nan.
Yanzuma sai zuwan mu ta samu tayi sallah ga shawaran dana bayar tana dan saka min albarka tare da fadin kaikan jafari kayi dacen mata wallahi tafi matar mamud sau dubu a gurina.
A gurinki kikace hjy shima ko mamud matar shi tafi mai kowa shima a wurin sa kai rabu dasu ka kara rike matar ka kaji wa yan nan suma a sannu zasu gane abinda nake nufi watarana.
Mama zaku tafi gida ku huta ko ya jafar ta fada kamar yana son a kawar da zancen zamu tafi kan ko don mu samu muyi sallah muci abinci.
Sai kuzo a mayar daku gida yanzu dan ni office zan koma daga nan ba gida nayi ba yanzu ina da aiki da zanyi sai dare sosai zan dawo gidan.
A tare muka fito dashi sai da ya dan tsaya da kaninsa sukai magana lokacin har mun kai bakin mota muna jiran a bude muna .
Kafin su tako zuwa inda muke tsayen har lokacin ban yarda na daga idona na kalleshi ba don tsoro shi dana fara ji a yanzu.
Cikin basarwa yace zainab lafiya ko kike ko dai ganin hjy a hakane yasa na ganki wani iri dake yau ?
Wanan haka take bata da sabo kullun a cikin jan jiki takewa mutane dan bambamcin su kadanne da matar mamud don ita din akwai girmama na gabanta gaskiya.
Karasowa yayi inda nake tare da dan dago habana yana fadin ki kula da kanki don Allah wanan shirun yayi yawa sosai.
Ya fada yana dan buga min kafadana a cikin wasa dan dariyan yake na sake mai na bishi a yadda yake so muyi gaban mutane da wasan basajan nasa.
Kamar ance in dago ido daga wurin motar shi taju ne ya kura muna ido kamar maye yana kallo abinda ke faruwa a tsakanin mu.
Wani kallo tsana na watsa mai yayi saurin kawar da kanshi gefe daya a raina nake fadin sai nayiwa wanan mutumin tsiya zai rabu dani da wanan kallon nasa na maita.
Saida muka wuce kafin su biyo bayan mu idona naga window mota idan ba idona yai min gizo ba zan iya cewa kamar na gansu suna kiss a cikin motan saidai bazan tabbatar da hakan.
Kuma ni san ban kawo komai a raina cewa wani abinda bai dace ba sukeyi a tsakanin su don ban zaci hakan ba ga ya jafar din gaskiya.
Innalillahi danaji ya jamal ya fada ya dawo dani ga dan tunanen da nakeyi a lokacin ne kuma naji mama daga gefena tana fadin kai jamal lafiya kake wanan tsabihin haka ?
No mama babu komai ya fada yana dafe kanshi a cikin takaici mama ta kara fadin ko mantuwa kayi a asibitin mu koma ?
Babu komai mama wani abu dai nagani ya daga min hankali kin dan kasan nan ba na musulmai bane tace nima haka nake gani ai kamar ma matan su a tsirara suke waisu wayewa.
A gidan ma bayan munyi sallah mun fito cin abinci kasa fitowa ya jamal din yayi a lokacin saida kyat mama ta samu ya fito.
Ina kula dashi bai wani cin abincin ba sai tasa shi gaba dayayi yana faman tunane shi kadai bayan kwana biyu da haka ina cikin dakin nan da nake kwana kamar wata manya a gidan.
Nake dan jiyo hayaniyan su daga falin dake tsakanina dasu wurin kofa na koma ina saurare wanan karon hausa naji anayi don haka na saurara dakyau ko zanci.
Wallahi wallahi kaji tsoron Allah ka guji ranan haduwan ka da Allah ya J ka dauka idan kayiwa mutane wayau zakaiwa Allah wayau ne ?
Ina zaka da alhakin wanan yarinyar da kake cutarwa a rayuwan ka ai gara ka saketa ka zauna kaita aikata sabon Allah ka zaifi ma sauki.
Jamal ni kake fadawa magana haka kai tsaye me kake tunanen ka taka a yanzu naji jamal din na fadin Allah .
Niko ya mamud ya sake hanyar Allah zan fada mashi gaskiya a yanzu balle kai da muke da shakuwa dakai ina zaka kai Alhakin iyayyen mu a kanka ga irin tarbiyan da suka bamu a baya.
Kudi ko ilimi ba hauka bane bazan fadawa kowa wanan abin ba zan dai tayaka addua idan kana da rabo a wurin Allah Allah yasa ka daina wanan harkan daga haka naji ya fita ya gaura kofan falon yafice daga part din.
Da sauri na koma saman gado na dafe bakina don kada sautin hawayena a fito fili sai can naji kamar ana taba kofan dakin Allah yasa ban yarda in kwanta ban sakawa kofan key ba har mai tabawan ya gaji ya daina tabawa.
Washe gari har na fito kamar mai sanda a falo na samu ya jamal a zaune yayi tagumi jin motsin fitowan yasa shi dago kai ya kalli kofan da yaji an taba din.
Mukai arba dashi a dan rikicewa nayi sai naga ya kawar da kanshi daga kallo hakan ya bani daman shigewa dakina dana bude hannuna na rawa kai tsaye na fada ciki.
Sauke numfashi nayi a hankali kamar wata barauniya da aka kama a lokacin nikan na shiga uku na fada a fili .
Ban yarda na fito ba sai wani lokaci dana kwatanci ya jafar ya bar gidan a lokacin na fito na rame sosai don damuwa da nake ciki a yan kwanaki nayi wani irin fari sosai saidan wuyan dan aje.
Yunwa ya fito dani babu kowa a falon duk da nayi mamakin rashin ganin halimatu yau da banyi ba wurin dining na nufa na hada ruwan shayi babu madara don bakina da nake jin shi babu dadi a ranan kamar na kwanta ciwo da dadewa.
Babu abinda nake tunane tun daren ranan sai kakamin ya jamal din ga dan uwan shi ina kuma tambayan kaina wani abune yaya jafar yakeyi boyayye da ba wanda yasan wanan abin.
Kisha tea din kada yai sanyi mana kin zauna kina tunane ke kadai a nan da sauri na dago idanu ina saukewa a kanshi.
A cikin daurewa nake gaidashi da ya jamal ina kwana saida ya zauna yake amsa min da lafiya zainab ya kika tashi ya bakunta kuma lafiya na fada ina dukar da kai kasa.
Zainab kisha kada tean yayi sanyi ya kara fadan hakan gareni da sauri kamar mai jiran umurnin shi na dauki cup din na fara kurba a hankali.
Mama Ramatu ne ta fito daki tana dan dariya halimatu na bayan ta tana fadin wanan yar akwaiki da wayau tsiya wallahi.
Dago kai mukayi muna kallon su har suka karasu inda muke na aje cup din hannuna a hankali tare da zamewa saman kujera ina gaida ita kamar yadda na saba a kullun.
Ta amsa min a cikin fara, a kafin tace dani lafiya kike kuwa yau naga kin rame lokaci guda haka ko wani abinne ya sameki kuma anya kuwa zainab ba shigan ciki ke gareki ba ?
Da sauri ya jamal ya dan kalleni sai kuma ya kawar da kanshi daga kallona sai naji na tsargu da wanan maganan bandai yi magana ba ina zaune na tasa kofin shayina a gaba ina dan wasa da bakin kofin a hankali.
Takon shine ya mayar da hankalinsu ga kofan part din shi yana saye a cikin kananin kaya da suka fitar mai da suran jikin shi har kurciyar shi ya kara baiyana a fili zakace ko dan shekara ashirin zuwa samane a lokacin.
Ya iso gurin tare da fadin mama an tashi lafiya cikin girmamawa a gareta ta amsa mai da fara,a tana fadin yanzu nake zance da matar ka kodai rabo ya shigane bamu sani ba gata sai faman rama takeyi haka a tsaye.
Da wani irin mamaki yace ciki a dan zabure sai kuma ya mike tsaye yana kallona a cikin mamaki yake fadin mama ciki ga zainab din ?
Kana mamakin hakan ne ga macen aure yanzu fa shekara da kusan rabi da aurenku meye abin wani mamakin hakan a nan Allah ya ingatar kawai musha buki wanda ka hanamuyi da aure sai muyi shi a sunan baby.
Kai mama bata dai da lafiya ne tace yanzu take fada min da dan zazzabi ta kwana jiya nace kila gajiyan tafiyane yaja mata hakan.
Amma kuna da abin dariya wallahi wai me kuke mamaki a hakanne gun matar aure har zaku tsaya wani zance ko baka shiryawa haihuwan bane a yanzu kana dabi,an ku na turawa.
Gyara zama yayi yana fadin kai haba mama har guda nawa wanan yarinyar take da zata haihu a yanzu at list dai ta kara yan shekaru nan gaba kafin ta haihu.
A naka tsarin kenan amma aishi Allah ba ai masa dabara idan ya tashi nuna ikon sa akan bawan sa ina cikin ne aimu muna maraba dashi.
Mikewa ya jamal yayi yana fadin zan fita daga can zan leka wurin hjy in dubata duk da yau nasan basa bari a shiga da safe.
Ba zaka jira yayan ka ku tafi tare ba ko akwai motan da zaka shiga ne a wajen yace zan shiga taxi daga nan ai ba nisa da gidan nan.
Barshi ya tafi mama ya jafar ya fada ba tare daya dago kai ya kalli kowa ba a wurin yaci gaba da hada tea din shi da yakeyi.
Wai ko lafiya kake da dan uwan ka kuwa mama ta tambaya tana kalon shi yakecewa lafiya mama me kika gani ?
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.