Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 106 of 139

LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON SAYA SAIKI KIRA WANAN LAYIN 08036959257 KO 09026931792 DARI UKUNE KAWAI KUDIN SA ALLAH YA BADA IKON BIYA YAR UWA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA YARDAN UBANGIJI, , , ,

Rayuwa haka ya kasan ce ba tabbas a tsakani da yaya akan cewa ya daina duk wani halaiya nasa mara kyau a yanzu.
Ni dai tunda yace yace ya daina na dauka din ya daina ko ya rage don ba yarda nayi da hakan har kasan zuciyana ba.
Sai dai ba wanan zancen a tsakanin mu ban sani ba ashe yaya yana nan yana shirin tafiyan mu zuwa Nigeria a asrince.
Don daga gyaran gidan da zamu zauna har suturo da duk wani abinda zamuci ko amfani dashi an gama hada komai a can Nigeria din ya tura wasu daga nan wasu kuma an saye a wani kasan an tura can Nigeria din.
Ko mami bata san da wanan shirin nasa ba balle wani dan uwansa ya sani dama dai jamal ne wanda nasu yazo daya da jafar din .
Yanzu ko sun raba gari a tsakanin su do ma mahaifiyar su na tsaye a kansu ne yasa basu kai inda ba,a so ba a tsakanin su din.
Don shi jamal din ga baki daya ya tsani jafar gaba daya a rayuwan shi ya tsani duk wani abinda ma ya fito daga hannun jafar din.
Tun yana iya boye hakan a zuciyar shi har yakai mami ta kai ga fahintar hakan duk abinda ya fito daga jafar din shi jamal baya amsa baya ko kallon abin.
Ranan a gaban kowa mami ke masa fadan hakan sam ta manta da cewa sauran yaran basu san halin da dan uwan nasu ke ciki ba a lokacin.
Take fadin Jamal ina kula da take taken ka kan dan uwanka kana nuna kyama da tsana akan komai nasa.
Duk halin da jafar ke ciki a yau ko ma ya zama abin kyama ne a gun wasu banyi tsammanin ku zaku iya guje masa ba ai.
Tsit sukayi falon kowa na kallon su kafin shi jamal din yace mami nifa ba tsanan shi nayi ba ina dai koyi ga abinda sunna ya koyar da mune ga masu wanan halin kawai.
Hali wani hali kuma kega ya J da har zai fadi haka mami kawai kila hassada ya jamal ya fara a kan dan uwan shi .
Amma meye matsalan da har zai fadwa dan uwan shi haka ni dai a gareni banga wani abin kushewa gun ya j din ba sai dai wanan bakauyiyar yarinyar da yake aure kawai wace bata san kanta ba balle na wasu .
I realy totally hate dis zainab yanzu wallahi ji irin dukiyar da shegiya ke ciki amma bata san yadda zata juyashi ba dan gidadancin dake damun yar iska.
Wani kallo jamal din ya watsa mata tare da fadin dan Allah gafara can ki rufawa mutane baki gada na balla ki a wurin nan.
Tunda bakya son ta ba sai ki kasheta ba ko ki fitar da ita cikin daulan da kike kyashin zaman ta din a yanzu.
Zainab da kike gani tafiki hankali da wayau sau dubu dan ita tasan ya kamata ba wai daula ko arzikin shi ke gaban ta ba ita.
A,a,a ke Aisha ki kyale bakin ki fa akan zainab don bata taba laifi a gaban bros tun asali kin sani .
Ta sani mana tunda yafi son ta sama ga dan uwan shi tunda ta iya makirci har ta gaji a rayuwa har yana wani son ririta ta yanzu a gaban kowa.
Mikewa yayi tsaye don fita daga falon yana fadin gaskiyane dai baki so mami amma yarinyar nan ai bata cancanci irin wanan ba a wurin ku yanzu tunda kunsan zaman da takeyi dashi itama.
Sakarai kawai mara hankali zanga yaushe zakayi hankali ka daina wanan halin wai kai mai ra,ayin rikau hakan.
Fita yayi bai juyo ba yana fita jalal ke fadin mami wai me ya J yakeyi ne da kullun jamal ke nuna baya son shi haka ?
Kyale mara hankali da baisan me yakeyi ba dan kawai dan uwanka na wani hali mara kyau zaka nuna masa tsana haka ?
Ni dana haifeshi ince me yanzu don yanzu dani duniya zatayi kwatancen shi idan an tashi fada ai.
Wani irin kallo yaran kewa uwar cikin rashin fahintar inda maganan nasu ya dosa a lokacin kafin Aisha tace wai mami nafa kula kamar akwai wani hali da ya J din keyi wanda ba a son mu sani.
Wata kila dai mata yake nema ko tunda naji jamal na fadin ko zainab na hakkuri dashi ai.
No kai ina ba dai ya J ba kan akan mata don da munga alaman hakan tuni a gareshi ba wanan bane mami basa son muji daine nake gani.
Dan Allah ku rufa min baki koma me yakeyi ku tayashi addu,a Allah yasa ya daina ta fada a cikin bacin rai tana kawar da kai a garesu baki daya.
Ranan wanan zancen da yaran sukayi ya hana mami din shakat a rayuwan ta dashi ta kwanta can dare kamar yadda ta saba tashi a cikin dare tayi nafila hakama ranan ta tashi tana mika kukan ta ga Allah.
Tun tana yi a cikin zuciyar ta har yakai ta fashe da kuka a fili tana rokanwa dan nata sauki a wurin Allah.
Tare da kaskantar da kanta ga Allah ta daga hannayen ta sama duka biyu tana hawaye tana addu,a tare da mika kukanta a kaskance wurin ubangiji.

Zaune nake ina bitan kur,anina da yanzu na koma gare shi sosai fiye da komai da nakeyi don ina son na kara saukewa duk da banda wanda zai karani a lokacin.
Sadiya ta fito daga dakinta tana saye a cikin dan wando pink daya tsaya mata iya gwaiwan kafanta sai yan aninaiya biyu da akaiwa wandon ado dashi sama rigace fara mai shaka shaka da rigan ta fito dashi a jikin ta.
Zama tayi kusa dani tana kokarin lalaban wayana dake gefena ajiye sai lokacin na dago kai na kalleta na tsayar da karatun da nake ina fadin .
Amma dai kinga abinda nake zaki zo min kai babu hula ko dan kwali ki zauna a kusa dani haka ?
Ba zama zanyi ba ai waya nake son dauka dama ta fada a cikin harshen turancin da yanzu dashi take iya magana ko a gida sosai.
Kallon ta nayi mai kama da harara ina kawar da kaina gefe ta gane may nake nufi yasa ta juya ta koma dakin.
Naci gaba da abinda nakeyi ban tsaya bin ta kanta ba sai can ta fito saye da hula a kanta ta zauna nisa dani tana kumbure kumbure na fita batun ta.
Shine ya shigo part din saye da farar jallabiya zakace balarabe ne shi din yadda rigan ya karbi jikin shi kusa dani ya zauna daya shigo .
Sai dai hankalin shi yana gun sadiya yake fadin Sady ya na ganki a haka kamar an bata maki rai ko ?
Shafawa nayi tare da dago kai ina fadin fushin banza takeyi tunda bata son a fada mata gaskiya don tana kokarin kwasan dabi,an nasara ta dorawa kanta yanzu niko ba yarda zanyi da hakan ba.
Me tayi ya fada yana kallon sadiya din ai gatanan ta fada da bakin ta ina mikewa don dauko mai ruwa don nasan ko ban dauko ba zai tambaya idan zai tsshi.
Ina zaki ya tambayeni ruwa zan dauko ma a fridge na fada naci gaba da tafiya na dan dade a kicin din don adduan dana tsaya yi a cikin ruwan ba wani addu,a bane sai fatiha dana tsiri karanta mai kafa goma sha daya a ruwan wanda kafin nasa nakan karanta na aje mai ya danyi sanyi daya tambaya na dauko mai shi.
Sai ranan na manta ban karanta masa ba har ya shigo part din namu haka yasa na dan tsaya ina karantawa har na bata lokaci a karamin kitchen din namu na part din.
Wai ke zainab tunda yarinyar nan tana son waya don me baki bata wayan can dana ce ki bata ba tun farko.
Tiren Ruwan da cup na aje a gaban shi cikin ladabi ina kokarin budewa yace min barshi sai na tashi zansha a cikin muryan shin nan me kamar na rowa ga mutum idan bashi yaso magana ba.
Wayar tana inane tunda kin hana mata naki ya sake maimaitawa nace tana nan aje wanan ma ai ya ishe mu amfani banda mutanen gida wa muke kira dashi.
Naki ma ai wani za a saya tunda ba zaki gida da wayar data sha hannu ba sai ki bata ta ci gaba da gamen dinta a zauna lafiya ko gimbiyar game ?
Sai lokacin tayi murmushi a fuskanta jin abinda ya fada din yace to koke fa sadiya kin zauna kin hade rai haka kamar wata matar soja can dake ?
Ni da naga sa,adatu hade fuskanta ai baiban tsoro na fada ina zama a inda na tashi muryan shine ya sake fadin akwai wani abinda kuke son sayane zaku tafi dashi gida duk da dai ba dadewa zamuyi ba zamu dawo ?
Don hutun nasu na tambaya baida yawa kwarai akace wanan karon saboda sadiya sai mu dawo da wuri yaya nikan sai na gama koda zan dawo na bashi amsa.
Tunda kece mai shirya tafiyan ya fada a dan hasale amma yaya kasan dai mun dade rabo mu da gida ai na fada ina kallom shi.
To idan hakane sai a fasa tafiyan in hakan bai maki ba wata daya na yanke zamuyi a can zuwa lokacin nasan kin gama dai abinda ya kaiki ai.
Duk da naji dadin zancen a raina amma a fili cewa nayi wata daya kuma yaya ina laifin dai wata biyu zuwa uku haka ?
Karatun nata fa wai zainab bana son wasa da abinda ya shafi karatun ku ga baki daya kema na saya maki form da mun dawo zaki koma karatu ne nan gaba.
Ko hakan bai maki bane zaki tsaya batawa kanki lokaci zanso ace kin hada karatun ki kaf a nan kafin mu tattara mu koma Nigeria gaba daya da zama can don hakan nake planning nan gaba don mami ta fara fadin mu koma gida hakana.
Mami tana da gaskiya yaya zama acan kusa da yan uwa zaifi ma tana ganin ka a kusa da ita hankali zaifi kwanciya ai balle ni wa yanan abokan naka yaya basu min ba sam.
Zainab yaushe kika san abokaina da har kika san basuyi maki ba ya tambaya da mamaki yana kallona .
Nasan su tunda sune mahalakan ka a yanzu na fada a hankali sai naji ya sake dan murmushi kawai yana kada kai .
Can yace zainab da kinfi haka bansan inda wayau ki zai tsaya min ba don kallon da nake maki kin wuce haka a wurina.
Abi ma dariya ya bani na kai bayana saman kujera ina dan murmusawa tare da fadin ni di kuma yaya sadiya karya na fada matar da take zaune a gida take fadin abokaina.
Yanzu da nayi magana yayan mu laifina zata gani yaya ta fada tana nokewa ga maganan ruwan dake gaban sa ya bude ya zuba a cup din tare da dan kurba a hankali yana kada kai kafin yace ina ganin ranan Friday mai zuwa muna Nigeria.
Don haka idan akwai abinda kowan ku keso sai ya fada ko ku fita ku sayo da kanku zaifi min sauki saidai bana son kaya masu nauyi da yawa kin sani ga tafiya.
Duk iya abinda zan rika yaya tufafine ko dan wani abin amfanin mu na bashi amsa ina cikin farin ciki da jin zamu wuce gida dabai fi an kwanaki ba a lokacin ashe .
Tu wanan ranan sosai muke busy yawon fita sayayya duk ban san cewa ya riga da yai muna sayayyan da ban taba zato ba don wanan tafiyan.
Kafin ranan duk mun gama wani shiri na tafiyan mu inda nikan shiri nakeyi sosai na barin kasan gaba daya a raina don haka duk wani abunda zan tuna nayi dana sani bukatan shi a can na tanada don komawa dashi gida duk ya yaya yace baya son muyi tarkacen kaya da yawa ga tafiyan.
Ranan daya bukaci mu fitar a tafi da kayan airport yasha mamakina sosai don bai iya boye bacin ranshi a zuciyar shi ba don ganin yawan kayan da yayi dana fitar.
Haka ya daure akai muna packed din shi zuwa airport inda kayan da alaman zasu rigamu isa ga nawa tunanen.
Shiri sosai mukayi daga gyaran jiki zuwa duk wani abinda ya kamata ace munyi don ban yarda na bar kasan ba saida naje har kauyen su maya mukai sallama da ita da iyayyen ta kan na tafi na tafi ke nan ba zamu sake haduwa da suba idan na tafi.
Kamar yadda duk wani sabo yake udan za a rabu haka muka rabu da maya da yan uwan ta kakarta bata barni haka ba saida ta ban wasu abunuwa datace na zanka amfani dasu har yayana nan gaba muka rabu cikin kewa da juna ina kuka maya ma tanayi.
Washe gari da daren ranan muka bar kasan chaina zuwa Nigeria sai dai naji haushin tsayawan mu a kasan Dubai da muka kanceqa da yayi wani aiki ya taso mashi a can da zai tsaya ya dan yi.
Ba laifi mun tsaya a Dubai mun kuma sha dadi sosai duk da shikan baida lokacin mu kullun sai dare yake dawowa masaukin da muka sauka wani lokacin ma kafin ya dawo zai samu munyi barci ko.
Wasa wasa kwanan mu biyar a dubai din wanda ni dai nayisu ba a cikkn dadin rai bane do na matsu na bufe ido na ganni a kasata Nigeria a lokacin.
Shiko hakan ko a jikin shi don ba abinda ya dameshi a zamanu din sai ranan da yake fadin gobe zamu bar kasan ya danga walwalana kadan.
Alhamdullahi mun sauka Nigeria da dare amma ta kano ba kamar ta Abuja ba kamar yadda ya tsara muna.
Nasan maganan hauka zanyi idan nace ya barmu mu fara zuwa gida don gamu a kano don yafi muna kusa da gida a lokacin.
Amma nasan zuciyana hauka take ban don ba zai taba yarda da hakan ba sai idan mun danganta da wurin mami da yanzu zaman ta ya koma garin Abujane kamcankan duk da an sauke su a lokacin.
Don lokacin har waya tayo min kan wai ban kirata na mata jajen saukan su a mulki ba ta fada don takanas ta kirani a waya ta balbaleni ni dai sai hakkurin dana bata kawai a lokacin.
Duk da an sauke su bata kwaso ta dawo kadana da zama ba sai suka zauna can ga baki daya tunda dama gidan su na kansu suke zaune a cikin sa yanzu ba na gwaunati ba.
Duk wani gyaran gidan da aka kara yi yaya J ne ya kara gyara masu shi suke zaune a cikin sa yanzu.
Karfe goman safe duk muna Abuja ba zance ga unguwar da muke shiga ba don garin gaba daya ya kara sauya min ga dan sanin danayi mai a baya.
Duk da rudewan sauyawan wurin hakan bai hanani gane ba wancan gidan da muka zauna a farkon aurena dashi bane kafin mu wuce zuwa chaina.
Wanan gidan na yanzu yaci uban wancan sosai ga fasali da keruwa komai na gidan sabone ba sai an fadawa mutum haka ba.
Motocine a haraban gidan gasunan birjit a cikin rigunan su rurufe sai shuke shuke da zai tarbe ka.
Tun saukan mu kano ya sauya layin wayan shi naga ya aje wancan wayan da mukai tafiya dashi haka kuma ya miko min nima waya sabuwa a kwalin ta kiran samsung full ita kuma sadiya iphone karama mai kyau da su.
Zakace duk biyun ba zaka gane bambancin su ba don kyau godiya nayi a fili a zuciyana kuma fadi nake kyautan karshe ke nan tsakanina dakai baka sani ba.
Don yanzu sai lalabashi kawai nakeyi in samu naga mun sauka ya mika mu gida lokacin zan tayar da balli na a garesu.
Don duk wani rudi da abin duniya da yake min yanzu ni bashine a gabana ba kaina kawai nake son na kwata a garesu naga na fita hannun shi baki alaikum ba tare da duniya ta zargi komai a hakan ba.
Kinga gidan ki na abuja ke nan da fatan tsarin ginan yayi maki kyau sosai ya fada kamar mai rada a lokacin.
Don naga kina da sha,awan ruwa wancan kuma babu swimming poll a cikin sa yasa na fadada wanan din aka gyara makushi sosai.
Dan murmushi yake na sake tare da fadin gidan yayi kyau sosai wallahi ballw ni yar tallaka ina ni ina wani zabem gida mai kyau gareni.
Bana son kina kiran kanki da hakan don yanzu a matata kike a idon kowa don haka wanan kallaman ya fita a bakin ki.
Donke din matar jafar kankia ce ba yar anchau ne ko meye sunan garin naku ba na manta ya fada yana kawar da kanshi don motar data tsaya gab da kofan shiga gidan.
Innalillahi zakace wasu basu tunanen lahira idan suna hada duniyan su kamar ba zasu barshi ba don tsarin gidan kamar ba gobe.
Haka muka fito muna bin gidan da kallon mamaki zuwa cikin gidan saidai duk hakan bai hanani addua a bakina duk da na rude da ganin wanan gidan haka.
Sai tambayan kaina nake wai ya jafar ne mai mahaukacin kudin nan haka kamar wani mai shekaru a duniyan nan daya tara kudi irin haka.
Oyyoyo da uwar dakina muryan fadilace ya daki kunnena lokaci guda sun fito tare da wasu daga cikin gidan.
You again muryan sadiya ta fada da dan karfi ta nufi wurin ta da gudu don murnan ganin ta a lokacin.
A hankali nake takowa cikin dan murmushi zuwa gareta ta hadamu ta rugume ga baki daya kafin sauran mata su shiga gaida mu suna muna sannu da zuwa cikin nuna kulawa a gare mu.
Na dago ina fadin mun sameku lafiya suka amsa a cikin fara,a da murna kamar sun taba sani mu da farko.
Shine ke waya da bansan wanda yake wayan dashi ba a bayan mu yake fadin mun iso a kawo mai abinda yace azo dashi din.
A raina nace giya ke nan ko wani katon tun da naji ya fadi hakan yayin da matan suka shiga gaidashi da zuwa da sauran yan aikin gidan.
Muna shiga wani katon hoton mu da muka dauka a chaina dashi ranan sallah ne ya tareni don nasha kwaliya a photon zakace ko balarabiyace ta asili yadda na fito a photon.
Da murmushi na sake tare da tambayan kaina yaushe har ya yi wanan aikin haka kai yaya ya iya duk wani abinda zai kawar da zargi a zukatan mutane shikan .
Ai wanan photon sai a dauka ni din matarshice ta gaskiya yadda photon ya karbi falom kamar kai magana damu mu amsa ma a fili.
A falo muka zauna aka shiga gaisawa da masu aiki sai kuma wasu biyu da ban sani ba na dai ga suna zirga zirga a gidan kamar yan uwan shi.
Kafin shi ya fara mikewa a daidai lokacin da Fadila ke fadin ai maza a kara gyara table din abincin don muna da gajiya kafim mu shige ciki mu huta.
No saidai su nikan zan shiga na watsa ruwa ya bada amsa yana kallon agogon hannun shi kafin ya juyo yana fadin mami bata san da zuwan mu na fa nasan zaku kwasa da ita karshe.
Da nayi laifin me tunda tasan bani bace mai tafiyan a raina kuma fadi nayi saidai tayi da wanda ta gani don ni goben nan zan bar gidan nan idan ma ba kasani ba ka sani.
Don a kage nake ko zuwa abujan duk bat da saune kawai nayi mai kada mu raba hali tun a hanya shiko sai wani nuna jiji damu da yakeyi a gaban kowa yadda kasan auren gaskiya muke a tsakani mu dashi.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.