Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 134 of 139

ZASSALAMU ALAIKUM YA YAN UWA MUSULMAI BARKAN DA GANIN WANAN RANAN NA ALHAMIS UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN.
KADA KI MANTA TASHIN DARE A WANAN RANAN MAI ALBARKA KI YAWAITA ISTIGIFAR GA ALLAH KI NEMAWA KANKI GAFARA ALLAH YA BAMU IKON TASHI YA KUMA KARBA MUNA IBADUN MU AMIN.

TUNI LITTAFIN DAI NA KUDINE BA A YARDA WATA TA KANTASHI BA IDAN BATA BIYA BA.

Yana tsaye a kaina yana kallona ba tare daya sake magana ba duk sun zuba min ido suna kallo na don ganin ban motsa daga yadda nake ba sai hawayen da nakeyi.
Sai ya mamud ne ya mike ya tako har inda nake tsugune ina sake hawayen bakin cikin dake cina abu goma da goma sun taru min a kaina lokaci guda.
Zainab kiyi hakkuri ki tashi ku tafi ya fada a gefena cikin nuna damuwa a gareni jin haka na dago kai da idona daya yayi ja don kukan da nasha ina fadi da kyar.
Tare da girgiza kaina gareshi yaya ba zan koma gidan ya jafar ba kai masa magana yayiwa mahaifiyar shi biyayya kan abinda take so dashi.
Allah ya gani da zuciya daya nake zaune dashi tankar yar uwa ta jini don duk abinda mami take nuna min banta jin kinta a raina ba haka diyan data haifa ina jinku tankar yayyuna ne na jini don yadda kuka rikeni tun farko.
Bada case din ya jafar daya hadani da mami ba wani sabani daya taba shiga tsakanina da mami duk zamana da ita.
Ban yarda na auri ya jafar dan son raina ba sai bisa tursasawan hjy gwaggo dashi kanshi ya jafar din da sukai min barazana a lokacin.
A daidai nan na dago kaina na dan kalleshi ido da ido tare da fadin yaya a wanan maganan meye laifina a cikin hakan ina duk saboda darajan mami na aikata hakan.
Yanzun kuma kaji a gaban kowa shima ya fadi bai aureni don yana sona ko wani abu nawa ba sai dan bukatan kanshi da yake ganin zai fiddashi ga idon jama, a.
Alhamdullahi kuma dukkan su bukatan su ya biya a kaina don Allah kusa ya sake don wanan abin ya kare daga yau din nan yaya ?
Na fada ina kara sake wani itin kuka mai tsuma zuciya lokaci guda daga inda mami take zaune ta zuba min ido take fadin kenan da sanin hjy dama duk hakan ya faru ashe ?
Shiko ya jamal sai cewa yakeyi ai gashi idan za ai magana a fadi gaskiya mami ki hana duk wanan abin da yarinyar nan takeyi ni nasan taimakon ki takeyi wallahi.
Kune dai da baku yarda ba da farko kuke ganin don bukatan kanta take hakan yanzu sai ku sama mata maslaha itama taje ta huta.
Jafar daya juya ya bamu baya yana cika yana batsewa ya juyo a hasale yana fadin wallahi baku isa ba babu mai rabani da matana wallahi .
Sai ko idan bana raye wanan kan na yarda da hakan naji mun yaudare ki din da farko daga ke har hjy data shawo min kanki a lokacin baku san komai ba .
Yanzu da nayi comfessing ina neman gafaran Allah da naku duk wanan din bai maki ba zai ba ya fada yana tsureni da idanun shi da sukai wani ja dasu.
Fine naji ya fada cikin wani irin zabura yana fadin sai ki fadi yanzu me kike son nayi maki don ki hakkura mu tafi ?
Na duka na baki hakkuri ko kudi kike sin na zuba maki fadi iya yawan kudin da kike koda duka dukiyanane zan iya ko mami kike son ta baki hakkuri gata zaune.
Ki fada duk a yanzu ko wanine daga ciki za ai maki a yanzun nan ba sai an jima ba.
Kai kai kai Allah ya rabamu da rashin tarbiya wallahi da tashi a cikin daulan da ba kwabo wadattace ga mutum.
Duk wanan abinda ya fada a yanzu shi a nasa zaton sune abinda zai kwantar min da hankali ko wani abu can.
A hankali na girgiza kai tare da fadin ko daya yaya jafar bana rayun ko daya daga cikin abinda ka lissafo min din a yanzu.
Na farko kana ganin dukawan ka a gareni ka ban hakkuri zai iya dawo min da farin cikin bakin cikin da nasha a wurin ka da mami da yan uwanka dake kina.
Ko kuma kana ganin kana da kudin da zai iya sayen mutucin na da imani na a hakan.
Sai mami gata a zaune mami uwace mafi soyuwa a gareni mafi girma da daukaka a idona ita da innata data kawoni duniya don bayan inna sai mami tayi imin komai a rayuwana ba zan taba manta harcin su ba a gareni.
You see mami kinji, kinji yarinya karama tasan halarci irin wanan, ta yaya ku manya zaku kasa gane hakan ?
Har ma wani dadi zainab ta samu a lokacin da take ta fadan kin mata halarci bayan tauyen ta da akeyi ana mai da ita kamar wata boya a ciki gidan nan kowa ya tashi ko ruwane zainab dai zainab dai ku din nan yau kunji inda akewa mutum alheri ya rama ta wani hanya.
Don ku din nan ba irin wullakancin da bakuyiwa zainab a gidan nan ba yau gashi tafi ku da komai a duniya.
Don ko kafanta ba wanda ya taka a cikin ku kaf din ku ba wanda yayi lilmin zainab a yanzu ya fada yana nuna su da yatsan hannun shi.
Ku rage wullakanta dan Adam don Allah don watarana baku san me Allah zai mai dashi ba jamal ya fada a hasale yana mikewa tsaye.
Ya girgiza kai ya saka hanayen shi cikin aljihun shi yana kokarin barin wurin.
Sautin muryan mami ne dake kuka yaji ya hanashi tafiya a lokacin ya juyo da mamaki yana kallon mami din da kuka takeyi wiwi a lokacin.
Ya mamud da sauri ya karasa wurinta yana fadin haba mami me yai zafi haka wanan ai saiki tada hankalin mutanen gida da wanan kukan naki.
Zuwa lokacin ko har sun karaso don Rufaida datake labe saman bene tana sauraron abinda ke wakana duk da bata ji sosai a lokacin daga inda take labe.
Tadai labe din tana kallo don tasan wani abu ke faruwa a lokacin a yadda taganmu zazaune yasa data hango mami na kuka kuma kaman ana fada ta fito da sauri tana fadin kuzo akwai abindake faruwa a waje da su mami don Allah.
Hakan yasa suka fito a cikin tashin hankali zuwa waje sai dai suna tunkaro wurin suka tsaya duk abinda ake fada a kunnuwan su ne lokaci.
Sai suka fara dan kalon juna a tsakanin su kafin hjy ta karaso tana fadin wai meke faruwa a wurin nan ne haka tun dazun ?
Sai kuma dan yanayin mami ya dauke mata hankali ta kurawa yar nata ido tana binta da kallon a cikin mamaki.
Iyami kin bata wayau ki yau har abin naki yakai ki zaunar da yarinyar nan haka a waje kina ci mata mutunci haka.
Ki duba nan duk yayan kine a nan aure kuma zasuyi suje gidan wasu shin kinsan irin *abifaru
sakamakon hakan zai zo masu ?
Shifa komai ka aikata a duniyan nan kai da kanka zaka girbi abinka da hannun ka shin iyami baki gudun yaran nan su tarar da uwar mijin data dara irin gasawa yar nan da kikeyi ?
Kowa yai shiru a wurin ana sauraron abinda hjy din take fadi sai rufaida ce ta bude baki tace wa tsohuwar kinyi kuskure hjy don mu kan ba zamuyi aure irin wanan na cusa kai haka ba gaskiya.
Ki min shiru Rufaida mami ta fada wa yar nata cikin tsawa a hasale taci gaba da fadin ana nuna maku hanya har kina ci gaba da magana haka.
Fada min yanzu meye laifin yarinyar nan zainab a nan don kawai ta auri yayan ku ko dan ta zauna a cikin mu har abada.
Yanzu na gaji da wanan halin da kukewa yarinyar nan zainab ku barta ta zauna lafiya da mijin ta don ko ta muna komai a rayuwa don ta zauna da dan uwan ku tsakani da Allah ba don wani abuba.
Yau na gaskanta hakan abinda kuke yawan fada min tayi ko kun gani sam abin ba haka yake ba ashe .
Don yanzu a wirin nan na gaskanta hakan na gane gaskiya abin ba hakana bane bawai ta asirce shi bane ko wani abu.
Tayi ne don ta farauta min rai wanda nasan da wuya a nan a samu wace zata iya yin abinda zainab din tayi min.
Kowa wurin sai kallon mami yakeyi don jin furcin ta a kaina taci gaba da fadin ina son ku sani daga yau ba raini ko wullakanci ga yar uwanku kuma matar yayan ku gata a zaune gaban ku zainab.
Ikon Allah hjy da takai zaune ta fada har lokacin tanawa mami din kallon mamaki kafin mami din tace hjy don Allah ki tafi gida dasu in an jima zanzo gidan da mamud da jamal mu sameku a can.
Mamakine ko al,ajabi ya cika min zuciya a lokacin don saukowan mami haka da sauri sai abin ya fara daure min kai na.
Wanda nasan ba ni kadai nashi yin wanan tunanen ba a wanan lokacin kusan duk wanda ke wurin yana mamakin hakan.
Hjy ta kalli jafar tana fadin mu tafi tashi zainab mu koma gida tun lokacin sallah bai shige muna a hanya ba.
Ba yadda na iya haka na dago kafata da kyat na fara ja don barin wurin ba tare dana iya yiwa kowa magana ba na fara tafiya.
Sai Anty Na,imace kewa dani zainab Allah bamu alheri sai munzo maku yawon weekend tunda naji ance kun kusa tafiya.
Dan murmushin yake na gefen fuska na sake ba tare dana bata amsa ba na wuce wirin motan mu kai tsaye.
Driver na ganin hakan ya mike ya taso da sauri ya nufo inda nake ina kokarin bude motar ya bude min na shiga na zauna ina jiran isowan su dan shi ya tsaya yana magana da su ya mamud.
Ita kuma hjy da mami suke tafe a hankali zuwa wurin motan da alaman dai duk maga sukeyi daya shafemu.
Yayin da yan matan suke tsaye suna kallon mamaki na sauyawan mami lokaci guda haka bayan zuwan mu gidan ne koma meye ya faru.
Bayan sun karaso bakin motan mami ta dan leko tana fadin zainab kada ki nuna masa komai don Allah sai nazo anjima din insha Allah.
Da kyat na iya budan bakina ina fadin to mami nagode cikin yanayin damuwa don shi kawai zan iya fada a lokacin.
Yana shigowa ya buga kofan motan da karfi saida na kadu mami take fadin kabi sannu fa kada ka tayarwa kan ka da wani ciwo kuma.
Ok ok don't mind ya fada tare da girgiza kanshi yana amsawa ba tare daya kallo inda take tsaye ba.
Hjy na fadin yama ja din aishi zai wahala shi daya sai kuma matar shi da zai wahalal a banza daga dan maganan fatan baki zai bata rai haka kamar soja a filin daga.
Mami ta daga, daga bakin motan tana fadin Allah ya tsare hjy ta amsa da amin sai kinzo.
Shiru cikin motar ba wanda ke magana sai driver ke faman sharara gudu don umurnin da ya bashi na yai sauri.
Allah ya gyara mun isa lafiya ba wanda yai magana haka muka fita wanan karon bai tsaya jiran hjy ba su jera kamar yadda mukafita a gidan.
Sai nice ba tsaya muka jera tana fadin tana tafiya ikon Allah yar nan nace ko wanan uztazun daya zo ya sauko da uwar taku da sauki haka a kan ku ?
Ai bai isa ya canza ta ba hjy sai Allah din dai da kika fada yanzu tace ai kuwa yar nan .
Tana dafa step din da zai hau da ita shiga cikin gidan take fadin a, to ai tace zata shigo anjima ai Allah ya kaimu, muji dame kuma zata zo din.
Har muka shiga gidan tana magana akan mami din muka shiga ciki ana muna sannu da dawowa sai ita ke amsawa a lokacin..
Har dakin ta na kaita kafi na juya na nufi nawa part din a gajiya ga kasala ga tunane dake cina da yunwa a lokacin.
Wanka ba shiga a gurguje don na makara da ga sallah a lokacin na fito na tayar da sallah din bayan na idar ne na zauna na dan gyara jikina na saka wani simple riga a jikina da zan dan sha isaka a lokacin.
Na koma na haye gado don ina bukatan hutu da kadaicewa ni kadai a dakin lokacin don yin nazarin abun da nake son ganowa kan nadaman da mami ta nuna tayi din a yanzu.
Kofa aka turo a lokacin ban dade da kwanciya ba na dan juyo a hankali ina kallon mai shigowa dakin anty Fadila ce ta shigo tana fadin .
Kun dawo a gajiye abinci na dinning tun dazun an gama sai dai nakaiwa hjy nata yanzun kafin in zo nan.
Nakine dana oga a dinning din yanzu sannuku da aiki nace a hankali sai dai anjima zan fito in danci tace shi oga fa ko za a kai masa nasa ne part din shi ?
No ki barshi idan yana so zaiyi maga ai na fada ina gyara mike kafana tare da bayana dana jingina da gado.
Tace da a debo maki ko ferfesun ki sha zaifi zama ciki ba komai na girgiza kai kafin ta karasa fadan abinda zata fadi din.
Sai kuma ta kara fadin ina ganin fa zuwa friday aikina zai kare daku zan bar gidan nan ke nan a ranan ta fada a cikkn murmushi tana kallona.
Da sauri na juyo gareta ina fadin wanan satin ke nan tace eh insha Allah ranan ne zan kamala komai in tafi a yadda aka tsara min.
Haba dai gaskiya da son samu ne zaifi kyau ki hakkuri har mu tafi idan mun tafi ai kinga shike nan saiki tafi a binki ko ?
Gaskiya hakan da wuya don iya month din da aka ban ke nan kuma na gama hada duk wani bayani da suke so a yanzu .
Gashi ban taba zywa aiki wani gida har wani yasan abinda ya kawoni a gidab sai wanab gidan naku abin kamar sihiri wallahi yadda har kuka gane me ya kawoni gidanku da sauri haka ?
Dan murmushi na sake ina kawar da kai tare da tunanen maganan data fada sai na dauka tana sk jin wani abune daga bakina duk da tasan ba zata taba samun amsanta a wurina ba amma ta gwada sa,an ta ta gani ko zataji din.
Kwanciya na gyara ina fadin tare da hamma kin san shi din mutum ne mai natsuwa da lura da komai.
Tace wanan kan na sani ai shiya ja min wanan dadewan tare daku don na kasa fahintar komai a kanshi duk zama tare daku din .
Ganin da tayi alaman ina son hutawa ta mike tana fadin barin baki wuri ki huta naga kamar a gajiye dai kike yanzu baki jin hira nacs wallahi na gaji gaskiya ta mike ta fita daga dakin tare da rufo min kofana.
Fitan ta daga dakin tun ina tunane har barci ya daukeni ban sani ba ban falka ba sai kusan karfe biyar na tashi ina salati.
Ban samu fitowa falon ba sai dana kamala komai a lokacin na samu fito har shidda ya wuce koda na fito.
Jin hayaniyan tunda na fito dakin hakan ya sanar dani muna da baki a gidan ga yadda naji ana dararaku na dauka wasu bakina sai ina karasowa naga ba wasu baki bane su mami ne da hjy a falon ake wanan dariyan haka.
Kunyan kaina naji a yadda na fito falon tun kan ya watso min irin kallon da yake min na warning na riga na tsargu da hakan.
Hakana na daure na karaso ina gaida su da zuwa ba kunya ko wani dar a idon mami take fadin diyata mun zo mun samu kina barci ai nace kada su tasheki a barki ki huta.
Lah mami ai da an tasheni din nayi sallah na fada ina dan dariyan da bakai ciki ba na kai kasa ina gaida ita kamar yadda na saba take fadi cikkn dakewa ke zo nan bana son in kara ganin kina jin kunya na haka kikaga yan uwan ki suna min.
Na gaisa dasu yaya duk ina zaune suke dan hira kafin mami din ta juyo gareni tana fadin tun dazun fada mukewa mijin ki .
Kina daki don Allah zainab ina son ku kawar da komai daya faru a baya a zukatan ku a zauna lafiya .
Wani zance a yanzu duk a bar tuno da abinda ya riga ya wuce duk da nasan hakan yana da wuya amma dai a daure.
Hjy da bata san zancen ba ta dora da fadin sabani dai suka samu har ya kaisu gareki yau din ai amma kuma zuwan nasu gaban ki kuma yayi rana sosai.
Tunda hakan yasa har tsakanin ke dasu a yanzu kun fahinci juna don ni abunda yafi damuna shine irin yadda kika sake wa yan nan kattan yan matan naki sukewa yarinyar nan iya shege ko a gaban kowa.
Don kawai suna takaman ta taba zama a karkashi su a baya wanan abin yana cimun rai sosao wallahi
Amma yau yadda kikai masu din nan yasa na fara fita kwakwanton da nakeyi na uwayen yaran nan .
Don sai nake zargin idan kuna wani abu dasu kamar ba kai sake suka barki ba Allah.
Budan bakin mami sai cewa tayi nima hjy watarana nakan yi zargin hakan a kan su wallahi don kinga Rufaida halin uwarta sak ta dauko ga hali.
Bata kaunan taga wani yazo ya rabeni a gidanan ko kadan sai naci mata mutunci wani lokaci takan shiga hankalin ta.
Laifi kine iyami yaushe za a zauna da uwayen mata nan dasu wai kuma budurwai duk ki sa su fito da miji ki aurar da yan banza.
Mami tace ai mazan sunki fitowane har yanzu ba mashinshini suna nan min zube cikin gida sai karyan banza wallahi.
Basu rasa mazajen aure ba kawai dai basa son masu son su dinne suna ganin sun fi karfi su auri kalan mazan ne ya mamud din ya fada.
Su koma gida mana idan hakane karatune dai sun samu yanzu ba sai ko wacen su ta koma gidan su ba inji jamal.
Kai a bar cen nan please ayi wanda ya kawo ku don Allah 3ni wa yan nan yan iskan yara ina ga nine zan koresu ranan da wata ta karawa zainab iskanci a gidan nan..
Bama zasu ba a yazu indai ba yaran banza suke ba yadda uwar nan nasu tayi masu dazun da haka har mami ta gaiyaceni zuwa dakina da sunan zatayi sallah .
A can ne muka samu kebewa da ita bayan mun sallame ta kira sunana na dago kai a hankali na kalleta

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.