Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 26 of 139
Mami tunda yaya mamud ke fada mata ai Jackson ya koma kaduna taji rayuwanta ya baci dashi sosai don me zai nuna bai iya zama a mahaifan ta.
Ko kuma yayi hakane don gujewa zancen auren data tasa shi gaba dashi don ko a daren jiya saida sukai mai tas itada yan uwanta da mahaifiyar su.
Wanan zance ne na sama sunayi da anth Aisha ta aikoni daukan mata charger ashe a dakin tsohuwar da dare.
Mami uwar zamanice don haka ba tare data furtawa kowa bacin ran da take ji a ranta ba ta nasa zata kyaleshi taga iya gudun shi yanzu.
Don haka ta daure taci gaba da tsabgoginta ba tare da nunawa kowa komai ba kamar ranta bai baci ba.
Haka kuma tasa a ranta wanan karon ba zata kirashi taji dalilin yin hakan dayayi ya barsu can ba tare data sani ba.
Karshe ma shigewa tayi da sunan zatayi wanka harta shiga dakin ta juyo ta fito zuwa dakin mu ta sameni kwance na rufe idanuwa na sai jin muryan ta nayi a kaina.
Da sauri na bude idanuwana cikin laushin murya nake gaida ita take fadin ya jikin naki yanzu ?
Naci sauki na fada a yar siririyar murya ina kokarin mikewa zaune ta sake fadin badai inda kike ji a jikin naki yanzu don in sani tun dare baiyi ba.
Zama tayi a gefen gafon dakin tana dan kale kale a dakin kamar tana nazarin dakin ne ko kuma wani tunane.
Na dago kai a hankali sai naga tana kallona can take ce min ko dai zancen karatun kine kika saka a rai haka zeey har yaja maki ciwon kai ?
Nace lah mami wallahi bashi bane mami dazun daine kan nawa ya fara ciwo kuma ai nasha magani yanzu naji sauki.
Tana mikewa take fadin to shike nan ina ganin zan karbar maki transfer tunda yanzu zaman mu zaifi yawa a can.
Don ba zan barki ba inda bana don ke din kamar amana kike ga hannu na ai.
Mami duk yadda kika zantar a kaina daidaine tunda kece uwana yanzu ai mami banda wata uwar dana sani kuma.
Tace to babu laifi na gode ga yadda kike nuna min nima sai dai ina tsoron watarana kar asabe ta rabani dake.
Asabe yamzu bata da iko kamar yadda kike dashi a wurina mami don ba tare nake zaune dasu ba kuma.
Sai tayi murmushi tana fadin kafin dai ki kwanta ki kara shan maganin da aboki ya sayo maki dazun don ina ganin har da gajiyan aiki din a ciki.
ZAINAN IDRIS MAKAAA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2ï¸Â⃣0ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA JUMMA,AT MUBARAK FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA KARBA IBADUN MU YA SADAMU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN YA GAFARTAWA MAGABATAN MUSULMI BAKI DAYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , ,
YAU MA DAI INA MAKI TUNI AKAN HAKKI DA KWABON KU MUKE SAMUN CIGABAN RUBUTUN MU A DAURE A BADA HAKKI DON SAUKE NAYI A KAI, , , ,
Sai faman shiyawa muke tun dare ake shirin dawowan mu kaduna taaraba mai yawa aka hadawa mami irin abinda zata bukata a birni wanda babu shi sai a irin wanan gari.
Gashi tare da wanan tsohuwar zamu koma don mami ta shawo kanta da kyar ta bari a kaita asibiti a dubata ta dan kwana mata biyu ta dawo koshi sai da wanan mami ya sa baki ta yarda da hakan.
Tun a can mami ke fadin wanan bakuntar zeey ce da Aisha ce don dai nasan hjy ba shiryawa zatayi da sauran yaran nan ba cewa su anty salma dake gida.
Bamu bar garin Samu,naka ba sai misalin sha dayan rana tafiyace maidan jayawa tsakanin kaduna da garin sai dai a gurin su yake haka nikan a wurina kamar unguwane hakan ai.
Don ko banza naga gari da kauyokan da nake jin sunan su a bakin mutane a da can da nake gida.
Allah ya kawo mu lafiya don wanan karon da motoci biyu muka juyo don mai tarin motocin ya juyo abinshi ya barmu can.
Duk da nasan mami tana wayencewa kan barin ta can da yayi don kamar rashin da,a ya nuna mata ga hakan don naji suna magana da anty Aisha a dakin da muka sauka kan hakan.
Aisha tana bata hakkuri da cewa mami ki dai bincika wata kila yana da wani uzurine yai haka don kinga ai daga baya jiya ya turo da sako a rabawa mutanen nan din.
Mun samu su mama Kande sun gyara gida tsab suna koma kan aikin girkin da za a ci idan an iso, da yake aikin nada yawa yasa basu kare ba kafin isowan mu garin.
Sun fito sun tari kowa da murna da farin ciki ina tsaye wurin mota babu wanda ya kulani a wurin nikan driver na fara fitar da kaya na fara dauka na shiga dashi cikin gidan da nakw ji yanzu kamar gidan mune.
Tsohuwarce tafe a hankali tana saye da glass din ido a fuskan ta sai farin gyale kwato dage yafe a jikinta dake saye da atamfan super mai ruwan haki da dorawa a jikin shi da manyan zane.
Da sauri na karasa ina kokarin karban ledan maganin data rike a hannun ta zata shigo gidan ga su Rufaida suna gefe suna mata tsiya.
A cikin ladabi na mika hannu ina karban ledan tace ba kaji ba yar albarka kedai kinfi wa yan nan kirki da hankali.
Barshi kinji ba wani kayan nauyi bane a cikin sa ai, aiko sukayo min caaaa a kai Rufaida na fadin wanan ai bakin iya yi ne da ita ga kowa saita nuna ita yar munafukaine ai.
Kai haba wanan zagin haka kuma fa ku daina wanan dabi,an bai da kyau ko kadan zagi harda iyayye.
Rufaida ta hasala ta watsa min harara nidai duk da tace baida nauyi bai hana in karbi ledan a hannunta ba.
Zama tayi a falo bayan ta iso da kyar don yanayin tafiyan nata yadda take yinshi a hankali ga tsufa ga ciwo dake damunta a jiki.
Nan falo gaba daya suka zube sai nuna kauna ga juna sukeyi ni dai ina tsaye da ledan nama shagala ban sani ba.
Banji fitowan shi ba sai kamshin shi daya doki hancina lokaci daya tare da muryan shi yana fadin watau nan ma kin biyoni ke nan ko ?
Na gudo na barki can bai maki ba saida kika biyosu kuka dawo tare yana magana tare da daure fuskan shi kamar gaske .
Ja,iri to baka tsira ba ai don gani ko na biyo ka din don ba fasawa zanyi ba da magana ta sai kagaji kayi zuciya ka fito muna da mata mun gani idan shika guduwa dama.
Mami yaya akayi kika zo muna da wanan yar matsalan tsohuwar gida yana magana yana kallon mami din data daure fuskanta tun fitowan shi kamar ba ita bace ke dariya yanzu .
Saidai jin ya ambaci sunan ta fake fadin cikin daga mai hannu please live me alone don't metion my name again cikin kara daure fuskanta gare shi.
Oh mami rely iam sorry for what i have done wanan tsohuwar ne ta dameni kuma nasan ba bari zakiyi in dawo ba idan na fada maki kai tsaye zanzo inyi wani abu a nan a ranan nima tafiyan ai da niyar in komane idan na gama sai gashi ban samu komawa ba.
O hjy ce ma ta dameka har kana fadi a gabana forgive me mami iam sorry wlh wani abu nazo yi garin nan na lake a cikin sa.
Alhalin tunda yazo yana gida bai fita ba yana daki yana ragewa kanshi zafi abindake tsunkularshi kwana da kwanaki.
Is your on business koma meya baro ka da garin mu dai ai ba zaka hanamu yin kwanakin da mukai niyar yi ba a can.
Ya dan laso bakinshi yana shafan kai don ya fahinci mami ta hau sosai dashi kan abinda yayi din na barin su can ya dawo nan shi kadai.
Ke wai lafiya kin tsawa mutane saman kai haka kina bin mutane da kallo don rainin wayau Rufaida ke fadi a hasale.
Keko gulma mana tana bin bakin kowa da kallon abinda ake fada kamar ba yar aiki ba ta dinga shiga cikin mutane tana kutsa kanta.
Ikon Allah da alama yar nan dai bata jin dadi a wurin ku meye matsalanta don ta tsaya a cikin mu ita din ba mutum bace kamar ku ai dan mutum daraja gare shi tsohuwar ke fada tana kallo.
Zo ki zauna a nan gaki tsaye kinyo tafiya baki zauna ba take fada tare da kallona tana nuna mi wurin zama.
Nace dama ledan nan ne ban san dakin da zan kai maki ba shine na tsaya na fada a dan marairaice.
To kuma ji da abinda ya tsayar da ita a gurin ba tsayin banza tayi ba ta mika hannu in miko mata ledan dake hannuna.
Mami tace na rasa me yarinyar nan ta tare masu a gidan nan da basu bata salama sai hattara da tsana.
A,a in kinga hakan wata kila dai sun hango wani abune a gareta sukewa kyashin sa ko don yanzu ta karbe masu fada gurin ki.
Su dai daina haka don ban so banyi sharawa da kowa ba da zan kawo ta gidan nan do haka ba zan dauki hakan ba gareta tunda ban bari uta ta raina ku ba.
Gaban mami bazo na tsuguna ina fadin mami bani key in bude daki zan gyara ne kafin ki shigo.
Ga dai key din gyara ki bari sai anjima yanzu dai ki kwashe kayan mu kikai min daki hjy kuma nata dakin ki kai mata sai ki koma dakin Aisha da zama ke .
A, a barmu mu zauna dakin ta a tare dama kawatace ki n ga ai ko tausa tayi min a dakin idan ina so naji kuma dumin mutum a kusa dani ai?
Ko ba zaki zauna tare dani ba kawata tana tambayana cikin dan dariya tana kallon fuskana.
Murmushi na sake wanda yasa fararen hakora dan baiya diple dina ya dan lutsa daga gefen fuskana ina fadin ina so sosai hjy .
Ya daifi ni dama ba zan zauna da kowa a dakina ba Aisha ta fada tana mikewa tsaye mami tace hakan baidai taso bane .
A nan na barsu ashe baya barina wurin Rufaida tayi fushi ta mike ta koma daki su waya ta jawo tana fadawa uwarta wai mami tana disgata kan yar aiki ita gida zata dawo don hakan da ake mata yana ci mata rai.
Duk da mami tace kada na gyara dakin ba yarda na barshi hakan ba don sai dana kara gyarashi tas na dawo dakina na gyarawa hjy yadda ya dace na dauko wani zanin gado dakin mami mai kyau na shimfida mata.
Falon na dawo inda na samu sun fara cin abinci har lokacin mami na zaune tare da yaran ta gaba dayan su a wurin sai salma da hjy ma kakarta ce don itace ta haifi uwarta a gurin tana nuna jin dadin ganinta.
Yau zee kici abinci ki dauko zanin gado a daki ki shimfidawa hjycdakin ki .
Nace na dauko na shimfida mami tun dazun ai tace kai zee na gode sa wanan karama hjy din da kike yi yamafi min ku zauna tare da zamanta da wanan mara moriya din tana nuna Aishan ta.
Mami nice banda moriya bari ki gani har wanka zan dingawa hjy har ta bar gidan nan kuwa hannu mami ta watsowa Aisha tana fadin karbi naki nan ko uwarki Ramatu tayi kadan tayiwa hjy wanka yanzu ai.
Abinci na diba na koma can gefe guda ina dan duban inda zan zauna mami ke fadin wanan abinci zai ishe ki ke nan zeey ?
Ya isa mami na fada ina nufar can nisa dasu don in zauna tsohuwar take fadin wanan ya da dadin zama take wallahi.
Wanan ba irin yarwa bace a cikin ahali yarinyar ta samu tarbiya a gun uwarta kada ki bar wa yan nan marasa ta ido su kore maki ita gidan nan.
Ai ba zan barsu ba mami ta fada duk wanda bai iya zama da abindanake so yayi gaba hanya a bude yake mai ai.
Baidai kai can ba kowa ya tsaya a matsayin sa tsohuwar ta fada mami ta nuna salma tana fadin sune ai marasa hankalin yarinya ta girmamasu sai sun zubar da mutuncin su gareta zasuji dadi.
No mami ba salma a ciki zancen nan don da kanta zeey ke fada min tana jin dadin zama da anty salma sosai idan muna hira da ita.
Salma tace mami ni ina ruwana da harkanta gidan nan tunda bata tare min komai ba ga kowa.
Shine daidai hakan ai kinji itama tana yabon ki a bayan ki gashi yanzu yar uwan ki tana fadi kuwa kafin ta juya wurin yaya jafar tana fadin.
Kai gwauro ba zakaci abincin bane kai ko sai yayi sanyi ka tsikara ka tashi tunda baka aje ba balle a dumama shi.
Zaki fara tsokanarshi ko hjy yaya mamud ya fada yana mikewa sai tsohuwar tace gashi ko yanzu ya iya yaji saboda korafina ba kuma zan fasa ba idan baiyi abinda nake son yayi ba.
Ya dago kai yana fadin me kike ci na baka na zuba hjy kwana zan fitar da mata kowa ya huta ina shike nan.
Shike nan kuwa kaga an wuce wurin haba ko kai fa mutum kamar me jin warin mata a tare dashi.
Barshi hjy rainawa mutane yake son yi wanan karin ko ba zan saurara mashi ba don naga wasa ya dauki zancen nan.
Mami ai na fada maki kwanan zan fitar kowama ya huta sai mami take fadin yar gidan wanene yarinyar da zaka fitar din ?
Mami ai ko yar waye zaki gani idan Allah ya kaimu ranan dinan ki sai naba kowa mamaki a gidan nan sosai.
Mami ai kin san sai yar gwauna ko wani seneter don irin su yaya Jackson sai diyan manya a kasan nan ai Aisha ta fada tana kallon shi tana dariya.
Shima murmushi yayiwa zancen Aisha din yace kedai bari zan yi surprise din kowa idan na tashi sai hjy tace kada dai kaiwa mutane zaben tumun dare garin ruwa idon kan nan.
Ni makoho ne aka fada maki ai kece mai bani shawara ki bari ki gani idan ban zabo da kyau ba sai ki fadi hakan.
Wayan shi da yai kara ya dauka yana duba kafin ya mike ya bar wurin yana wani magana kamar yare sai hjy ke fadin.
Itace ta kiraka kake gudu kar muji me kuke fada dama ka zauna da wanan yaren naku baji muke ba mu.
Daga inda nake ina dan murmushi wani tunane yazo min nake fadin a raina zanso nima inga wanan zabin na yaya jafar yadda yarinyar zata kasance.
Nasan badai kyau da kudi ba kan kamar yadda yake da kyau din nan ga ilimi ga wayewa dole wace zai aura din itama ta kasance kamar ai.
Ni daya ke faman tunane har naji abincin ma ya fita a raina ina tuna sukan sunji dadin su uwa kudi uba kudi haka.
Suma gasu kudi wai ina mutanen nan zasu da wanan dukiya hakane idan da nice su ai ba zan nemi wani kudi ba zan zauna in hutane kwai inta jin dadi na a gida.
Zeey zoki kwashe wanan kayan abincin nan wurin nan ki dawo ki kai hjy daki tayi sallah ta dan huta.
Firgigit na dago kai tare da fadin to mami ina kokarin mikewa a inda nake zaune din.
Sai dana gyara komai mami na zaune gurin tana waya da yayan ta da muka baro dazun garin su.
Hjy muje in kaiki dakin azahar yayi tun dazun na fada a cikin ladabi ina kokarin daukan kayan ta gyale da ledan maganin ta dake gefenta aje.
To yar nan har na fara gyangyadi ko a wurin ba tare dana sani ba tana mikewa tare da kokatin tattaro gyalen ta dake gefe.
A hankali muke tafiya zuwa dakin har muka kai dakin yayi dan dumi sai kamshi ke tashi a cikin sa ledan na aje a gefen gadon kafin in nufi kofan ban dakin in bude mata shi.
A, a kagani ba nan yayi min gara in zauna dake da in zauna da wanan mara moriyar Aisha wace ko kara ba zata iya kawar wa kanta ba balle wani.
Bayan mun idar da sallah dukkan mu a nan kasan muka kwanta nabawa hjy filo tayi matashin kai dashi niko ko filon ban samu matashi dashi ba sai barci.
Ban falka ba sai da hjy ta tashini don inyi sallah la,asar nasan yamma yayi saboda dadin barcin da nayi.
Na idar na mike zuwa dakin mami bata dakin yasa na samu daman kara gyara dakin da yake ba wani datti a ciki dakin
A falo mamice da yaya mamud suke magana haka yasa na juyo zan koma dakin mu indan gyara don ko ba komai da zan wa dakin ban dakin yana bukatan wanki koda yaushe.
Na wanke na fito ina daukan filon data kwanta a kasa take fadin yar nan idan kin rage sai ki kaini falo in zauna don yamma tayi yanzu.
Na amsa da to hjy muje mami ma tana falon zaune tare da yaya mamud .
Wai ni iyalin shi mamud din suna inane don banji duriyan su ba tun dazun ina a nan gidan suke zaune ne suma.
Suna Abuja an barsu a can da zamu dawo kaduna yar ta kifen tana nan dai da halin ta har yanzu bata canza zani ba ko ?
Dan dariya mai sauti nayi ba tare da nayi magana ba don ban san abinda zance da ita ba.
Falin muka fito tafiyan minti daya daga dakin mu zuwa falin saida muka biyar muna lalabawa kafin mukai saman kujeran ta zauna a hankali.
Mami na fadin kun lalabo kun fitone hjy take fadin yar nannta lalabo dani ina dan jin dadin hakan yarnan akwai kirki sosai.
Allah yasa kiga aurenta hjy amin ta juya tana fadin kada ki tsaya dogon bokon nan na zamanun nan dake batawa mutum lokaci sai a dauki lokaci yaro na zubar da irin sa duk wata.
Yaran nan da kun gane ai da ku aurar da su don har sun wuce munzali aure a yanzu .
Hjy kin san ai aure dan lokaci idan lokacin sa yayi koda shiri ko ba shiri sai ayishi a lokacin.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.