Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 40 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

ZAINAB IDRIS MAKAWA

3️⃣3️⃣

BARKA DA WARHAKA YAR UWA UBANGIJI YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN.

Tana tafe a fusace don ranta daya riga ya baci da yaranta a dakin hjy data shiga sallama da ita ta samu ya mamud suna zancen da hjynta ta ballashi ta fito da fushi ranta a bace cike da tunane.
Tun kan ta iso bakin motan security din ta suka mike tsaye tare da bude motar suna jiran isowan ta wurin.
Tsayawa tayi gaisawa da masu gadi da wanki da mai kulla da komai dake gudana a gidan massege ne yashigo wayan ta tayi niyar shiga mota ta diba sai kuma ta dakata a yadda take tsaye.
Kafatan daya na a motan yayin da dayan kafan nata yake waje ta dafa motan ta bude sakon da mamakin ko sakon meye ya shigo mata a wanan lokaci.
What ta fada da dan karfi, bayan ta karanta sakon dake a fuskan wayan nata a fusace ta juya zuwa cikin gidan tana shiga a kofa suka hadu da ya mamud.
Gaba daya yanayin fuskanta duk ya sauya ranta ya gama baci tanajin zuciyan ta bakikirin a lokacin.
Wani sakon ne ya sake shigowa a lokacin a hasale take duba sakon take idon ta ya kara kankancewa ga baki daya.
Mamud da suka hadu a lokacin ganin yanayinta mami lafiya ya ya fada a dan razane ?
Wani kallo tayi mai kafinta ce biyoni muje ciki kawai ta fada tana gaba yana biye da ita a baya.
Dakin namu suka shiga wurin hjy da sallama cikin wani irin yanayi hjy dake zaune take fadin lafiya dai ko iyami ?
Hjy yaron nan me yake nufine, me yake tunanen ya taka da har zai rainani ko ince su rainani.
Wai me ke faruwane haka iyami ya mamud daya karasa shigowa yake fadin .
Wai mami wani abune kuma akayi yanzu rufa min baki ta fada a cikin tsawa wallahi ka zama babban banza a gurin kannen ka mamud.
Wani kallon mamaki ya jefowa uwar don baisan dalilin wanan fada ba a sanyayye ya furta a cikin mamaki mami ni kuma me nayi yanzu kuma ?
Hjy wai ki duba yaron nan dan baida wayau kullun shi dan maganan nan danayi yanzun nan yaron nan ya kwashe ya fadawa dan uwansa.
Wai sai gashi jafar ya turo min kudi masu yawa haka har yana fada min ga kudin aikina nan tun lokacin dana dauko zainab a gidan ya biya.
Shike nan ta faru ta kare dan nan ya fashi yarinyar nan a gidan nan yanzun kuma sai ki samo wata.
Hjy me kike fada haka kuma sanda na dauko yarinyar nan nayi shawara da shine ko yasan su waye iyayyen ta?
Wallahi wallahi mami ga hjy nan idan nayi magana da Jafar a yanzu kan na fita dakin nan wurin ta ya mamud ya fada rai bace hankali a tashe.
Hjy tayi wani shu,umin murmushi a fuskanta kafin takai zaune cikin tagumi tana karkada kafan ta a cikin mamaki.
Hannu takai ta cire glass din dake sanye a idon ta na fadin ni jafar zai nunawa yanzu wuyan shi ya isa yanka.
Har zai turo min miliyoyin kudi waishi a dole ya fanshi zeey a hannu na to dashi da kudin nasa duk sun, , , , ,
Kai kai kai iyami karki soma furta wani zance mara dadi ga danki dan yau ne fa ke kuma uwar zamani kinga kuna kamanceceniya a wurin hali.
Ba yadda banyi dake ba a gidan nan tun kan zancen nan ya kainan na baki shawara da ki zuba masu ido ki kyalesu suyi soyayyan su.
Wasan gobe banda Allah iyami Allah kadai yasan meya tsara ga hakan kince ba hakan ba kin tsaya kina jayayya da hukuncin ubangiji.
Iyami ina ji maki tsoron irin abinda zaije ya dawo baya a kan wanan jayayyan da kikeyi a yanzu.
Yaron nan idan dai ba alhakinshi zaki dauka ba a banza wallahi baiyi waya da dan uwansa ba a dakin nan yanzun nan ya fita.
Hjy dan Allah bari lokacin da zai aikata hakan kina ina zai iya tura mai sako.
Mami baki yarda da rantsuwana ba kenan ya fada a dan mairaice yana maijin wani iri a ransa ba dadi duk yana jin mami ta muzantashi a lokacin.
Ya dubi mami fuska a daure yana fadin ki kira jafar din yanzu aji wanda ya fada mai don ni wanan abin gaba daya mami kin jefani a cikin zargi .
Idan bakai bane waye ko yarinyar nan ne zeey gata kuma a kwance tun dazun sai dai idan daga kwancen ta kulla wanan sherin ba abin mamaki bane kuma.
Haba mami ji wanan don Allah bai dace ba meye laifin yarinyar nan a yanzu kuma don Allah ?
Kai ke na ka fadamai saka fito fili kafada sukaji muryan Jafar na fadin hi bro ya akayi ne ka fito ke nan naji duk abinda mami ke fadi a waya dazun so na tura mata da kudin sai tai set din yarinyar free by now.
A samo wata daga yau ta dinga wanan aiki ita kuma tayi facing din karatun ta final.
Eehhee mara kunya beran tankwa nayi shawara da kaine da zan karbo ta yaji muryan mami tana fada a cikin tsawa.
No mami bakiyi ba saidai tunda abin har yakai wanan irin zargin yana shiga tsakanin ku let her set free by now tayi karatunta kawai.
Mami yanzun kin daina zargina a wanan zancen me zaisa na fadawa jafar wanan magana tunda nasan a cikin fushi kika fade shi.
Ni kuma ba zan so inga wani abu na tashi hankali haka ya faruwa a tsakanin kuba ko yaushe Jafar fa dankine mami.
Yau yace ga abinda yake so a rayuwan shi mami ya kamata ki sasauta zuciyan ki don in kin kula jafar yayi nisa a wanan zan, , , ,
Kaga dai yanzu na gane yadda zancen yake don haka katafi kawai kada ka makara a wurin aikin ka ta fada kuma a dan hasale.
Toh mami na gode ni zan tafi ya fada yana mikewa daga bakin gadon da ya zauna da farko a gigice.
Yama manta a kusa dani ya kai zaune a lokavin don haka bai kara waigowa ba ya fice daga dakin.
Idona biyu duk zancen da sukeyi yana a kunne na ina sauraren su ban yarda na motsa ko kadan ba don kar mami ta gane a falke nake duk da bana tantama da tasan a falke din nake a lokacin.
Mami naji ta mike tsaye tana fadin ni zan tafi hjy sai dai idan na dawo shi kuma ai zai dawo gidan nan zamu hadu dashine ai ni zai nunawa kudi har yaushe yai kudin nasa shi .
Ko yau din nan yayi dai ya wuce raini a garesa da kayan sa hjy ta bata amsa murmushin karfin hali mami ta sauke a fuskan nata ta fice daga dakin.
Nasan idon ki biyu yar nan bayan wuya sai dadi insha Allahu wata rana idan an daure sai labari.
Dagowa nayi ido shabe shabe da hawayen wahala ga ciwo ga tashin hankali a lokaci daya ya dameni.
Don ranan gaba daya wanan zancen ya hanani shakat a rayuwana don ko makarantar ban samu zuwa ba a ranan ke nan.
Kamar yadda hjy ta fada na mike tsaye da kyat na nufi bandaki ruwan zafin dana samu a heater na kunna ya dan taru na wasa a jikina.
Na fito na shirya a cikin wani blue din dongon rigan English wear mai adon stonen fari a gaban shi.
Fuskana ya koma fayau a dan lokaci guda bana jin karfin jikina ko kadan zama nagi gaban abincin karyawan dake gaban hjy na zuba ido .
Kici abincin mana ta fada a daidai lokacin na dago fuskana dake zubo hawayen dana kasa tare su a lokacin.
A bazata naji muryan hjy na fadin ki daina kuka nima wanan abin ya fara firgitani a gidan nan ki shiya kayan ki kaf zuwa gobe ki koma gaban iyayyen ki kowa ya huta.
Kada azo matsalan yazo yafi wanan abu ya taru ya rikice a lokaci guda ta yadda ba za a iya gyaran sa ba har idan kina da rana a gareta zata gani nan gaba.
Shi kuma ya tafi ya nemi wace uwarshi ke son ya aura din mu gani yanzu kici abinci ba a ciwo da rashin ci ko kadan ne.
Hakana na daure ba don ina so ba na tsakuri a bincin zuciyana yana cike da damuwa kala kala don a gaskiya naso duk wani cin fuskan su mami gareni in daure in karbi kwalin karatuna.
In yaso daga baya in nuna ni gida nake bukatan komawa gaban iyayyena yafi mun kwanciyan hankali.
Sai dai a yanzu kan banda sauran zabi fiye da barin gidan mami din gara in hakkura da karatun nan tunda abin har yakai ga dafa min sata abinda ban taba yi ba a rayuwana.
Gobe kafarki kafata a garin nan ba zan haifi da da cikina in zauna dashi ba tare da yaji magana ta ba duk ko abinda yazama.
Nabi iyami a sannu ne inga iya gudun ta gareni saida har yanzu shedan yayi shimfida a zuciyar ta ita bata bi magana ta ba ta yaya yayan ta take son subi nata don wani manufa nata can na daban.
Idan anyi magana ta farawa mutane kame kame akan zancen ta mata ita ba haka muka dorata ba ina mahaifin yaran nan da halin shi ta aure shi lokacin shima ba matsiyaci ta sameshi ba ba a cin arziki taci ita a rayuwanta.
Hjy ce ke fadan wanan maganan a cikin bacin rai ban yarda na tsuka mata ba sai faman tunanen da nake a cikin raina a lokacin.
Mikewa tayi don yin sallah walha haka ya ban daman gyara kayana kamar yadda ta umurce ni inyi har ta idan a daidai lokacin dana gama komai duk da yar jakar kayan da aka ban bai isheni hada yan tsumakarana ba don yanzu Alhamdullahi ina da yan waddatatun kayan da Aisha dashi jafar din suka waddatar dani dasu.
Falo ta tursasa min da mu fito ko jikin nawa zai kara ake min a kwance nake na dunkule saman kujera a daidai lokacin da mukaji takon tafiyan mutum yana shigowa falon mami din.
Ban dago kaina don ganin kowaye ba a lokacin ina kwance a yadda nake.
Muryanta ne ya sheda min da Nuriya ce matar ya mamud tana gaida hjy dake zaune saman kujera ban dago don gaishe ta ba don kowa na gidan ina kallon shi a makiyina.
Idan ka debe mazan gidan gaba dayan su da suke nuna min iya kulawan su idan sun shigo.
Tsiyata da dan kauye gadara ke me kika taka da bazaki gaida mutane ba dadin abin dai dan halin bera ke ga mutum bai gani ya kauda idon sa saiya dauka.
To ai sai ya gani yake dauka ko wani ko ai ko bai gani ba dauka yakeyi don abin yanzu ba sai dan kauye ba don har wanda baka zata ba sai kaji ya yaudari mutane mutanen ma mijin shi na sunna don kawai ya tara ya kaiwa tsofin sa gida.
Hjy kina nufin dani kike wanan zancen au kema da wani ke zancen ke nan ke kalleni da kyau banyi maki kama da tsofin banza ba da zaki kawo wa diban albarka ba.
Kin taba aje abu a gidan nan ta daukar maki ko wani naki ko dan gidan abinsa ya taba bata toyo dama shi ya kawo ki shiyan nan takalan magana ko me ?
Girman mahaukaci karamin mai wayau sai ya fishi ke abinda kikeyi a gidan nan ai ko kare baya ja .
Mayafi kayan dake jikin ta ta cire ta mayar a kafadan ta taja wani uban tsuki tare da fadin hjy tsohuwa ba mamaki dai kema an gama dake gun malam na kauye yanzu.
Idan bashi ba yanzu dai magana ta nake a wurin nan ba tare da ambatar sunan kowa ba shine har kike kokarin bata min suna haka ?
Bari shi mamud di ya dawo da uwarsa Inji wanda ya fada maki haka a cikin su don ba zan taba lamuntan wanan zancen ya tafi a banza ba gidan nan.
Allah dai ya dawo dasu din lafiya hjy tace tana nuna bajin tsoro a cikin zancen ta ko kadan tafito mata hjy zainabu Abun tana asali.
Wanan abin ya kara saukar min da hawayen bakin ciki masu dumi da kunan zuciya a lokaci guda sai me kuma ?
Ba hjy sai ta juyo gareni a zafafe ta hauni da fada a cikin takaici tana fadin ke yar da wanan bakin kukan naki dayaki ci yaki cinyewa gareki.
Wa yan nan ba mutuncine dasu ba zai ruwan jikin ki ya kare a banza basu san kina yi ba maza ki gyagije ki shiga tsabganki hankali kwance kamar Allah ya aiko ki.
Shi ai sheri ga dan wani takine babba ga wanda yayi shi ni dai nasan harga Allah ba shedun zurba baki daukan masu kwandala a gidan nan ba in har sun yayada wanan zancen haka suyiwa kansu sheri don min sai ya tambaye su.
Hjy nikan na yafe masu kada Allah ya jarabi kowa a cikin su da wanan abinda nake ji a yanzu don akwai zafi da ciwo a zuciya.
Kaji ya mai hankali nima bawai ina nufin hakan ya samesu bane ai ina dai fadin yadda abin yake ne don idan sheri ko hairan ka kuddurata wa dan uwan ka sai kwantankwancin hakan ya sameka kaima.
Kiran sallah azahar ya tayar damu a gurin sallah muka idar a daidai lokacin da lami ta shigo dauke da kayan abincin hjy dakin na gaida ita da aiki.
Take fadin yar hjy ance yau bakiji dadin jikin naki ba Allah ya karo sauki na amsa da amin kawai don yanayina babu dadi cikin sa ko kadan a lokacin.
Fitar lami dakin yayi daidai da shigowan shi da sallama a dakin kamar daga sama muka ganshi ya fado dakin a wanan lokacin.
Jafari ka dawone ashe yau zaka dawo garin hjy dake zaune saman sallaya tana jan tasbaha ta fada a cikin fara, a da kulawa.
Eh mun dawo hjy mun sameku lafiya ya gida ya tsufa da jinya ya fada fuskan shi a kaina na dukar da kaina gabana na faduwa tunda yayi sallama dakin kamar an aiko min da mutuwa nakeji.
Ya jikin naki ya fada a lokacin daya karaso yana zama a kujera kusa da inda nake zaune daga ni sai ni don na nade hijjabin danayi sallah.
Dagani sai dogon rigan dake jikina a lokacin sai duk na tsargu da kaina don ban so ya sameni hakan ba a daki.
Sannu da dawowa ya na fada can ciki ciki ya kara fadin ya jikin kunje asibitin hjy ya fada yana kallon hjy din don son jin abinda zata fada.
Asibiti ai sai yan gata ita ina taga gatan da iyami zata kaita asibiti yanzu tunda kajawa yar bakin jini ga kowa a gidan nan wai ace wanan zancen yakai har ga kunnen matar mamuda a gidan nan.
Zata zo ta nemi karawa mutane zafi akai ina fama da uwarku sai gata dazun gabanin azahar din nan wai tazo yiwa yar fade tayiwa uwarku sata a gabana don yarinyar nan bata data ido a gabana fa jafari don iyami ta mayar da yarinyar nan sabban gida yanzu.
Murmushin takaici kawai ya sake a fuskan shi tare da mikewa tsaye lokaci guda yana fadin zan shiga ciki hjy in watsa ruwa.
Naso hjy ta barshi ys fice a lokacin amma sai gashi tana ta janshi da fira daga tsayen da yake yana amsa mata da eh ko a, a da kuma Allah sarki.
Har ya samu ya fita bansan lokacin dana sauke wani irin gwarou nufashi da har ya fito fili ba a lokacin.
Ki daina tsoron shi kwana nawa ne kun zama daya yar nan ki duba saboda ke ya bar abinda yakeyi ya dawo garin nan yanzu bana ko tantama donke ya dawo a wanan lokaci.
Hjy don ni kuma na fada a cikin yar murya da mutum zai dauka a shagwabe nake magana na tace.
Don ke mana yar nan ya kamata ki fara nuna mashi yadda ake nuna mai yadda yake nuna maki kulawa haka nan.
Munci abincin na kwashe kaya don mayarwa kitchen din a can su kande suka tsareni da tambayan meya hada hjy tsohuwa da matar mamud dazun ?
Ke fadin ina barci ban san meya hadasu ba mama bata da kunya bata data ido sam wanan yar kowa sai kokarin takashi take a gidan nan haka take muna sai bayan mun karasa hada mata abinci tasa a dawo muna dashi wai baiyi ba.
Nidai ban tofa ba na bar kitchen din ina jin daci da kunci a tare dani dakin na dawo na kwanta a gefen hjy don jinta nake kamar kakata data haifeni da kanta.
A dakin shi bayan ya fito daga wanka yayi sallah har la,asar yakai zaune a inda yake bai daga daga kasan ba sai murzan kai da goshin shi da yake yana ji yanayin da yake wani iri.
Baison yayi komai a lokacin don yana jiran dawowan mami ne a lokacin yasan zasu hau sama da ita a yadda ta hasala dashi din a waya.
Don kawai yace ta yi set din yarinyar free shi bai dauka hakan ai lefi bane a gurin shi tunda ya biya abinda mami ke tunanen ta kashe wa yarinyar.
Waya ya karba hakan ne ya dauke mai hankali don suna neman shi kan wani ma,aikata da za a gina suna bukatan shi ya tsara masu wasu na,urori a cikin tsarin ginan wanda saishi ne yasan yadda abin zaiyi daidai yadda suke son shi a ginan don bayanin da yakewa sauran ma,aikatar su basu gamsu dashi ba.
Wanan dalilin yasa shi dole ya koma a bakin aikin shi sai dai zaiso kafin ya koma maganan shi da yarinyar nan ya tsaya kada ya bar baya da kura idan ya tafi.
Anyi magariba duk bai fito ba mami kuma tasan ya dawo yana gidan bata nemeshi yadda ta saba ba idan yai hakan.
Ba wai baison fitowa bane gurinta saidai abinda zai faru a tsakanin sune nai shirya mai ba alokacin.
Mami da ta gama fusata da lanarin da hjy ta bata tsakanin ta da Nuriya yasa ranta baci don abinda tayiwa mahaifiyar nata din don bata kaunar abinda zai taba mutuncin hjyn balle ta bangaren ta.
Sallama yayi kofan mami ya shiga dakin kai tsaye tana zaune a bakin gado a cikin rigar bacin ta sai farin tabarau da zai kare mata haske a idon ta na karatu ta duban wani takarda a hannunnta.
Ba tare data dago ta kalleshi ba ta amsa mai sallama a ciki ciki tana mai cigaba da kallon takardan.
Gefen ta yakai zaune yana fadi a dan shagwabe mami iam tearyed ubana ka dawo ta fada ya riko hannun ta yana fadin kasan nan akwai matsala mami.
Bazan iya abinda suke son nayi masu ba don ba zasu iya fitar da kudi ayi aikin kwarai ba mami nasan ba zaka iya dasu ba dama kada dai suga sun gaiyace ka baka amsa su bane kawai.
Duk maganan da take bata dago ido ta kalleshi ba taci gaba da fadin dana san haka zai faru da zuwan ka garin nan da ban bari ka tafi ba.
Dasun baffan ku ya kara kirana kan zancen ka har yana ikirarin ya baka wata daya ka fitar d mata a cikin yan uwan ka daga Rufaida Nazifa da su Rubby.
What mami me zanyi da yaran nan godforbid mami wanan meye a cikin su banda zalla rashin kunya a tare dasu.
Wa yaja kansa da har ya samu kafan wanan maganan dama ai na dade da sani nufin su kanka ko su jalal niko yarana ba wanda zanwa aure a gida .
Mami ku fitar dani a wanan zancen don wanan shirme na dauke shi gareni na riga dana fada maku matata don haka yanzu ku nake saurare.
Zaka fadi haka jafar tunda ka sayeta a hannuna kake gani kana da kudin da kai zaka ban ni maryam har zaka turowa kudi jafar ?
No mami ba haka nake nufi ba don Allah ina son tayi facing din studies din ta a yanzu ne idan haka ya bata maki rai kiyi hakkuri mami ki nemi wata.
Bazan nema ba ta fada tana juyowa gareshi kaje gaka ga yarinyar nan sai dai kasan inda zaka kaita yanzu kuma baida ma matsala hakan mami ya fada tare da mikewa ya bar dakin.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.