Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 93 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWALITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KAFIN KI KARANTA DA GUJEWA DAUKAN HAKKIN WANI, , , ,
Duk wanda ke gidan yasan akwai rikici a tsakanin sai dai ba wanda zaice ga dalilin daya faru a tsakanin su ba.
Sai hakan ya jefa kowa a cikin duhu akabar su da wasi wasin a zuciyar su don suna son sanin meke faruwa haka a gidan.
Sai dai sunfi karkata zuciyar su akan rashin kaunar da mami batayiwa auren mune ta tayar da wanan fitinan a tsakanin mu .
Har hakan ya jawo wani fitina da akeyi a lokacin wanda ya dagawa kowa hankali a cikin mu.
Nuriya har zancen ta tsare ya mamud dashi a dakin su ya hauta da fada yana fadin shi sam bai sam ma wani abu yana faruwa a gidan ba in ba data fadi hakan ba yanzu a gaban shi.
Bata gane komai ba dole ta bar zancen ga gulma kuma yana cinta akan sanin ko rikicin me akeyi a tsakanin su.
Gashi mami ta fada masu su shirya zasu koma gida tun lokacin tafiyan da suka debo baiyi ba na komawan su gida.
Da safene ina daki zaune wayana yai kara na dauka layin ya jafar ne ke kirana a take mamakin hakan ya kamani.
Saida naja aji na daga wayan da sallama a bakina naji muryan shi kasa kasa yana fadin kizo dakina ki sameni yanzu.
Ya kashe wayan nabi wayan da kallon mamaki a raina don mawuyacin abune zaisa ya nemeni a part din shi haka kai tsaye don ni har na saba da hakan.
Saida na dan dauki lokaci na mike na fito tare da rufo kofana na nufi part din nasa don ba nisa ke garemu sosai ba.
Dama kuma zamu bar wanan gidan mu koma wani unguwa dake can nisa da inda muke a yanzu .
Sanin hakan ranan yake waya a gaban mu muke jin yace wurin sabon gidan shi da zai koma da family din shi za a kai wanan dalilin yasa muka san zamu tashi a gidan.
Na dauka yana falon shi saidai ban sameshi a falon ba haka yasa na nufi dakin kwanan shi kai tsaye.
Saida na danyi nocking din kofan kafin in tura in shiga bawai zanji amsawan shi bane in har ya amsa din ma.
Can na hango tsaye a gaban widow dakin yana kallon haraban gidan na tako a hankali har zuwa inda yake tare da fadin gani yaya.
Ya juyo lokaci guda tare da dan kura min ido na dan lokaci kafin yace dani rufo kofa magana zamuyi dake.
Na juya zuwa kofan na rufo koda na juyo a lokacin ya dawo saman gado ya zauna wuri ya nuna min na samu a kusa dashi na dan zauna a cikin tsarguwa.
Zainab me kika fadawa mahaifiyata da yan uwana game dani ya fada ba tare da ya dago kai ba har lokacin kanshi na a duke ya harde hannayen shi biyu saman gwiwan kafan shi.
Da sauri na dan kallo shi don nima fuskana yana kallon kasan dakin dama a cikin mamaki karara a fuskana nake kallon shi.
Ya dago kai ya dan kalleni sai lokacin naga yadda idanuwan shi suka sauya sun rikede kamar ba nasa ba lokaci guda.
Nace mena fada masu ko sun fada ma na fada masu wani abu a game da kai zuwan su ?
Duk da nake yarinya ai nasan mutuncin kai na da kuma darajan aurena don haka bana cikin irin matan dake fallasa sirin gidan su.
Ido ya kura min kamar yana nazarina kafin ya sauke ajiyan zuciya yace idan bake kika fada masu ga yadda nake ba banyi zaton akwai wani wanda zai fadi hakan ba garesu.
Amma ai abinka ba a boye yake ba kowa ya sani idan ka boyewa wa mutane ai ba zaka boyewa Allah ba dole wata rana asan ko kai waye .
Saidai ranan ai mami ta shigo dakin kuma ta ganka tare da wanan abokin fasadin naka koka manta da hakan ne ?
Don ni ban san a yanayin data riskeka a ciki ba nadai ganta tayi baya acikin tashin hankali wanda hakan yai dadai da zuwana wurin na tareta zuwa dakina.
Bayan haka kuma ta wayi gari a cikin ciwon da har ta kwanta asibiti don haka ba ni zance da kawai na sani ke nan a gidan nan.
Humm kada ki mayar dani karamin yaro zainab idan baki fada masu ba abinda ke shiga tsakanina dake ba a matsayin mu na miji da mata yaya za ayi su san hakan su ?
Wanan ni ba matsala bane tunda zaman hakan bai dameni idan kana son jin komai ai zaka iya zuwa ka tuntubesu su fada ma wanda ya fada masu hakan.
Don ni ba a wurin mutum zan kai kukana ba sai wurin mahalicina don shine mai maganin kowa ba wani ba don haka meye amfanin fada masu komai.
Rashin kunyar nawa ai baikai in fada masu ga yadda muke zama dakai ba don na matsu ko me zaisa har in fadi hakan.
Na fahince ki zainab kina kokarin nuna min yanzu kinsan komai na dade da kula da hakan gareki don hakane kike son a rabaki dani yanzu ko ?
Idan anyi hakan an taimakeni ne yaya don ko ba a rabamu yanzu ba nan gaba dole a rabani dakai ai.
Kamar yadda nasan ka a dan musulmai a asali haka nima nake diyar musulmai a zahiri don haka ba zan zauna na yarda mu kone tare da kai ba tunda ka sani kake take sanin ka .
Tunda nakan fada mai magana ban taba gasa mai mai zafi irin wanan ba don haka hakkurin shi a ranan ya kai karshe dani.
A harzuke sai dana razana daya daka min wani tsawa ke enough kada ki daukeni mara hankali ko rashin wayau.
Naji mami na fadin zata wuce dake Nigeria bari kiji idan ma ke kika hada wanan zancen ki koma ki fada mata kin fasa tafiya don hakan zaifi maki sauki.
Don kafi ki tafi sai na halaki a kasan nan idan kin kafe akan zaki bisu ba tsoro duk da na tsorata da maganan nace.
Nasan zaka iya don imanin ka nada rauni ba Allah ka sani ba ai da baka kwana da dan uwanka namiji ba kabar , , ,
Marin daya daukeni dashi yasa naga wani irin duhu ya gitta min har na manta da abida zan fada lokacin.
Dafe wurin nayi na dan lokaci kafin na mike cikin karfin hali ina fadin ka mareni yaya ?
An mareki kada ki manta tun farko saidana fada maki auren mu na taimakon junane nida ke.
Don me yanzu zaki bijiro da wani zancen saki a baya ko kin dauka kinfi karfinane da kike min abinda kikaga dama ina kyaleki.
Akwai abinda nake duba nake raga maki sosai kada ki dauka hakan ba yana damuna bane don kawai banda abinda zanyi dake.
Wani kallo nayi mai wanda ban taba mai itin sa ba na raini na juya na fara tafiya don barin dakin.
Zaka san ka mareni don wanda bai sani ba yanzu zai sani bazan zauna da fasiki mai aikata fasadin mafi muni ba a duniya na fada dana kai kofan dakin.
Ya bini da kallo yana jin kansa kamar ya hade ranshi don wani irin takaicin da yake ji a zuciyar shi yana fadin.
Shi yarinyar nan zatayiwa tonon asiri irin haka duk ingata mata rayuwan danayi kada takai zuciyar ta ga hakan ?
Kafin wani lokaci wurin ya nuna alaman yatsun hannun shi don ya fito radau a fuskana abu ga farin mutum sai idanuwa na duk suka rikede sukai ja.
Kin fita nayi ina daki a kwance don ban gaida kowa na gidan ba da kwana a ranan haka yasa hjy aiko sadiya ta dubani ta same a wanan halin.
Komawa tayi ta fada mata ta samu kamar banda lafiyane ina kwance.
Sai ga hjy ta taso da kyar zuwa dakin take tambayan meya sameni ina kokarin boye mata take tambayana.
Wanan kamar shedan mari a fuskan ki nayi kasa da kaina ina hawaye jafiri ne ko shi yai maki wanan haka ?
A garin yaya haka ya faru ko uwar tasa tasa ya dokeki haka har tsanan yakai tasa dan ta gaba yai maki haka ?
Na samu na bude baki da kyar ina fadin hjy ki taimakeni ki rabani da ya jafar don ba cikkaken musulmi bane shi.
Innalillahi take fada tana taba hannayen ta a cikin mamaki kafin tace sallah ne baya cikawa ko azumine bayayi ?
Kaina girgiza mata a hankali ina maijin yadda zan bude bakina nayi maganan da ita a lokacin.
Saiga fadila ta turo kofan ta shigo dauke da abinci a hannun ta don tana da wanan dabi,an na kula dani idan ta fahinci bana cikin dadin rai.
Yanzu sadiya ke fada min bakya jin dadin jikin ki ta fada tana aje abincin tana kallona idon ta yi arba da shartin yatsun shi a fuskana .
Da sauri ta dago tana fadin subbahanallahi meya faru kuma haka madam wa yai maki wanan aikin haka ?
Wa zai mata banda mijinta mara tunane koma me tayima ai sai kayi hakkuri tunda baku kadai bane yanzu a gidan nan.
Wanan ai sai kabar mata abin fade idan yana dukanta bama kusa yanzu ma da muke nan akace ya duketa don bai san ciwon kansa ba.
Ina jafari ina dukan wanan yarinyar haka tunda ba karfin su daya ba wanan me zubin samudawa ina wanan yar zata dauki dukan shi haka ?
Hjy tunda nake zaune dasu a nan ko fada basa yi gaskiya a tsakanin su don zainab yarinya ce mai biyayya .
Yau daine hakan ya faru tsakanin su har abin yai muni to idan uwarshi tasa ya dukeki ai ya daki auren shi ke nan a gidan nan.
Jin haka na kara marairaicewa ina fadin don Allah hjy ki ceci rayuwana ban iya zama da yaya jafar a maysayin miji don ba dukiya nake aure ba.
Shiru sukayi suna kallo na kafin fadila tayi karfin halin fadin haba zainab ai addu,a bai bar komai ba ki dinga masa adduan nan dai da kika saba har Allah yasa ya daina wanan abubuwan da yakeyi din.
Amma zancen a rabaku wanan wani sabin tonon asirine a tsakanin ku zai taso maku har duniya ta jiku.
Bayan ana ganin ke din mai sa,a ce da kika samu miji da gidan hutu irin wanan kinga mutane basu gane halinda kike ciki ai.
Dakata yar nan kuna makana kun nuke ni ta baibai kun barni a duhu kai zancen ku yana nuna akwai mumunan zama a tsakanin auren nan da bamu sani ba.
Wallahi hjy a kwaishi kan sai dai tayi hakkuri data saba amma zainab tayi kankanta da irin wanan rayuwan haka da takeyi a gidan nan tunda da kurciyar ta.
Ace miji ba ruwan sa dakai ba zaya kalleka da sunan mata ba a idon sa saidai ayi ta labta ma kayan alatu kana hasaka gari ?
Tsohuwar ta gyara zama a rude tana fadin nikan kun barni a cikin duhu har yanzu don na kasa fahintar inda kuka dosa.
Sai ta mike tsaye wanan zancen bana kyalewa bane barin samu uwar nasa idan itace me sakashi cutawa yar nan haka a zaman su.
Duk kiran da fadila kewa hjy ta fice bata juyo ba gashi da kyat take tafiya yanzu ajiyan zuciya na sauke don nasan ko banza yanzu za ayita ta kare tunda har hjy taji wanan zancen duk da bataji duka ba ma.
Fadila ke fadin banso tsohuwar nan tafita haka a cikin fushi ba don yanzu komai zai iya faruwa har wa yan nan yaran su ji.
Dakin da mami ke ciki hjy ta dosa suka hade da ya jamal a kofa ta wuce shi tana fada haka kawai ka tasa yar mutane a gaba da duka .
Gara dai a kashe wanan auren kamar yadda iyami ke so tun farko kowa ma ya huta da wanan alkakan hakana.
Aure ba haihu bada ba jika amma fitinan shi har yau yaki karewa mutane a rayuwa gara akashe kowa ya huta.
Jin hakan yabi bayan ta zuwa dakin kusan a tare suka shiga mami na zaune ta jingina bayan ta da gado kafafuwan ta a mike da gani ba sai an tambaya ba tana cikin damuwa ko tashin hankali walau ciwo kuma.
Yau dai ayita ta kare a gidan nan ku sakarwa yar mutane mara ta huta mami ta dago kai da sauri tana fadin hjy kedawa kuma ?
Ni da dan nan naki jafari ya kama yar mutane da duka haka duk ya bata mata fuska da shartin yatsun shi ina yar nan ina daukan dukan bawan Allah nan.
Ko ya fara shaye shaye ni kan don sai magana take min bayani a dunkule mai nuna ABU A CIKIN DUHU SIRINE.
Mu muna mata kallon ta samu gida tana yadda ranta keso jiya jiyan nan na gama ji yaran nan wanda basu da aiki sai hassada da kyashi suna fadan haka da kunnuwana naji su sai gashi yau Allah ya nuna muna sirin dake boye.
To gara dai kisa ya sallami yar nan tunda abin ya kai ga duka haka tun muna nan ke nan inaga bama nan Allah kadai yasan ukuban da yake nuna mata tunda kin riga da kin masa huduban shedan ya dauka gara dai kowa ya huta da wanan auren itama ta kama gaban ta taje ta samu daidai da ita a can.
Saida ta kai aya ta dago kai don duban mami data kyaleta tana ta zuba haka sai taga mami din na hawaye mawuyacin abu ga mami din duk yadda ranta yakai ga baci kuwa.
Cikin muryan kuka mami ke fadin hjy jafar kasheni yake son yi ya huta a yanzu ina dana sanin ma haihuwan jafar a duniyan nan .
Hjy tayi tsaye sororo tana kallon mami din cikin mamaki don ganin yanayin ta dakuma abinda take fadi din don yadda tasan tana son dan nata fiye da duk yan uwan shi.
Haba mami ki daina fadan haka ki masa addua jamal ya fada daga bayan hjy inda yake tsaye a kofa ranshi bace.
Jamal dole in fada don jafar so yake ya konani a duniya bayan ya kona kansa saboda rudin duniya.
Fita yayi zuwa waje ashe ya mamud zai kira a waya ya kirashi ba a jima ba sai gashi yazo da saurin sa suka shigo tare.
Har lokacin mami kuka takeyi sosai itama hjy sai ta kama kuka duk da bata san abinda ya saka mami din kuka ba haka ?
Da sauri ya turo kofan ya shigo jamal na bayan shi ya maida kofan ya rufe don ma ginan su irin na kasan da wani bsijin wani da dole sauran mutanen gidan hankalin su ya dauku garesu.
Wai me kuma ya faru ni wanan abin gara mu koma gida zaifi mami fon wallahi hankalin kowa dai a tashe yake da wanan maganan.
Shi kanshi jafar din ai in kin kula baya cikin kwanciyan hankali duk tsiyat shi yanzu da yasan an gane me yakeyi ana nuna mai kyama.
Haka yasa ya tozarta ga baki daya baya cikin walwala duk da karfin halin shi kuwa wanan karon ya sare don bai zaci haka abin zaizo mai lokaci guda ba tunda ya maida mutane wawaye,
Yanzu ba wanan ba ya mamud zainab ya kama ya doka waya sani ko yayi shaye shayen nasa ne kuma ko ta kamashi yana harkan banza.
Sam ya manta da hjy tana dakin don idon shi ya rufe a lokacin yake faman dake maganan da ba a son taji din taji sai ji sukayi ta fadi saman gado Allah ya taimaka a zaune take lokacin.
Ihun kiran sunan ta da sukeyi yasa hankalin a gidan ya koma kansu da gudu aka nufo dakin mami din.
Gaba daya dakin suke shiga dan ihun da mami din keyi ina daki ban leko inda suke ba don hutun nasu ya zama muna tashin hankali ga baki dayan mu daga mu harsu a yanzu.
Ya mamud ya kira jafar a waya yana fadin kana inane kazo ga hjy ta some muna bata numfashi.
What hjy din meya same ta kuma yanzu muka gaisa da ita na fita to kazo dai yanzu ya fada ya kashe wayan.
Shike nan kun kashe min uwa kun huta saura ni ku kasheni mami ta fada a cikin kuka goran ruwa mai sanyi jalal ya dauko a fridge ya bulbula ma tsohuwan ta sauke ajiyan zuciya saidai bata bude ido ba.
Lokacin ne jafar ya shigo gidan a rude yana fadin ku dauko ta ga motab asibiti nan waje yanzu zasu karaso .
Yana kokarin daukan tsohuwan kakan tasu uwar ta daka mai tsawa da fadin kada ka taba min tsohuwa.
Tsayawa yayi cak bashi ba da wanan zancen ya daki zuciyar shi duk wanda ke wurin saida zancen ya taba mai zuciya.
Ya mamud ne ya matso ya sukuci tsohuwan dake kwance zuwa waje sauran suka mara mashi baya a cikin sanyi jiki.
Allah ya gyara daga Nuriya har yaran ta babu kowa a wurin lokacin suna part din su sun kulle don har yanzu bata bari yaran su sake jiki a cikin yan uwa.
Muna daki bamu san wainar da ake toyawa a gidan ba fadila tana ban hakkuri har muka koma hiran hjy da take nuna min kauna kamar ni din jinin tace.
Na,imace ta shigo part dina tana fadin hjy fa ba lafiya an tafi da ita salati muka saka fadila na fadin yanzu fa muke nan tare da ita.
Falon muka fito muka samesu zaune zugun zugun anan suke labarta muna dan abinda ya faru muna jimame tare da tamtaman hakan.
Allah ya taimaka ba a kwantar da ita ba bayan yan aune da sukai mata suka bata magani da sallama.
Bayan sun dawone kula da hjy ya dawo kaina nake kula da ita da komai dani da fadila yayin da shi kuma bai zama gidan sai dare sosai yake dawowa.
Ranan naji yaya mamud na fadawa hjy zasu koma Nigeria jibi jin hakan danayi yasa nima na fara shirya muna tafiya.
Fadila ta fahinci hakan ta sameshi ta fada mai don kada tayi laifi a wurin shi bai iya min magana ba don abinda ya faru mami ta kara daukan fushi dashi sosai da bai taba tsamani ba don ko ya gaida ita yakai bata karbawa yanzu ko gaban waye.
Don haka yaje ya samu yaya mamud don yai min magana ina daki zaune sai ga ya mamud din yazo nan dai yake ban hakkuri yana fadin.
Tunda yace da zaran na gama karatu zai zo damu Nageria don haka nayi hakkuri idona ya kawo hawaye nake fadin ya mamud kasan ya dai fada ne kawai .
Sau nawa yake zuwa gida bai je damu ba sai ya dawo muke sanin gida ya tafi ai dolen shi yazo gida don mami dake fushi dashi yace .
Muddin yana son albarka ya gama da duniyan nan lafiya dole yazo su shirya da mami din.
Dole ba don na yarda ba na bar zancen tafiyan muna kallo suka kwasa suka koma bayan ya cika yan uwan shi da abin arziki kaf da suka zo sai mami da jamal ne sukaki karban komai nasa.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.