Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 57 of 139
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4ï¸Â⃣8ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERIN GAREKU TARE DA BAN HAKKURI RASHIN SAMUN UPDATE KO DA YAUSHE DA FATAN ZAKUYI MI AFUWAN HAKAN YAN UWA, , , , , , ,
Ina kwance tun safe kamar yadda ta umurceni da yi hakan din sai dai tunane ya addabi rayuwana yadda wanan wasan da take shiryawa zai kaya muna.
A gogon dakin na bango na duba da karfe sha daya saura na safe tun bayan sallah asuba nake kwance ni ba barci na koma ba don tunane ina kwance a falke ina faman dakon tunane a zuciyana.
Wayana dake gefen gado wanda tun daren jiya na ajeshi da zamu kwanta ban kara bi ta kansa ba ya dauki kiran agaji.
Hannu na mika daga inda nake kwance din na dauko wayan da zuman ganin wanda ke kira layin don ban taba zaton kiranshi bane a lokacin.
Lanba ce ta kasan waje aka kira layin dashi na kurawa kiran ido ban daga ba ina nazari a raina har kiran ya gaji ya katse lokaci guda .
Wani kiran ne ya sake shigowa lokaci guda ina kallon wayan na fitar da sautin kida na kasa dagawa don na farko ban sheda ko lamban waye ba a lokacin.
Na biyu kuma idan na dauka shine mai kirana me zan fada mai don bamu riga da mu aje magana abinda zan fada mai ba.
Jikina gaba daya yayi sanyi a lokacin a cikin daurewa kiran na gaf da tsukewa na kai hannu na danna dauka.
A hankali na kara wayan a kunne na lokaci guda ina sauren mai kiran nawa hello din daya fada a gadarance yasa na fahinci ko waye a layin shidin dai ne ya kira wayan a lokacin.
Ya kara fadin hhy ya kuke me faru dakene dazun fadila ke fada min baki da lafiya tun jiya ko fita daga daki bakyayi.
Saida na tattaro wani karfin hali a tare dani kafin in iya budan bakina nace a hankali cikin yanayin wanda ciwo yake damun sa na furta banda lafiya ne da kyar.
Baki sa lafiya ita fadila me take jira dake a gida bata kaiki asibiti ba ko bata san aikin ta bane wai ?
A hankali na lumshe idona tare da fadi a marairaice cikin sanyin murya ta sani ita dince ma take kula dani yanzun haka na basa amsa.
Ta kaiki asibiti ya kara tambaya ta kaini jiya da yamma na samu kaina da fadin hakan duk da nasan komai karyane shirin hakan mukai masa.
Zan turi maku da sako idan wanan bai isa ba aimin magana ya fada kamar a kage yake da ya kashe wayan shi a lokacin.
Yaci gaba da fadin idan har kuna da matsala da ita zan iya canza wata a samo wace zata kula dake fiye da ita.
Ban san lokaci danace a rude laifin me tayi koda mahaifiyata ce ita ai iya kar taimakon da zatayi min ke nan .
Naji ya saki ajiyan zucuya tare da fadin ta kyautawa kanta don bana son wasa da aiki a rayuwana.
Idan ma laifi ne ai ba ita bace mai laifin don ba itace ta rabani da uwata ba na fada can kasan makoshi na a hankali na dauka ba zaijini ba.
What me kike fada ?
Shiru nayi tsayin lokaci babu amsa daga bakina bai kuma kashe wayan nasa ba a hankali na runtse idona ina sauke numfashi da kyar don gabana sai faduwa yake daurewa kawai nayi a hakan.
Ba zaki magana ba naji ya fada a cikin dan daga murya nace to ai kaine ka rabani da mami kuma ka , , , ,
Look ina wasa dake ne zainab yaushe har raini ya shiga tsakanin mu haka dake ko so kike na bar aikina nan na dawo na zauna Nigeria daku ?
Kit na kashe wayan tare da maida nufashin dake sauka min na tsoro da sauri don ban zaci zan iya fadan hakan ba ni kaina.
Aje wayan yayi daidai da shigowan anty fadila dakin cikin sauri na dago kai a firgice ina fadin anty wallahi shine ya kirani yanzu din na fada ina kallon ta kamar mara gaskiya.
Na sani ta fada tana zama a gefen gadon da nake kwance nima mikewa nayi ganin ta zauna din a dakin.
A haka zamu kamo shi sannu a hankali har hankalin shi ya karkato zuwa gare ki don maza a yanzu sai da kisa da iya zama dasu a cikin dabara.
Na bude baki da zuman magana ke nan aka turo kofan inda nayi shiru maizubd ce ta shigo tana fadin wai nikan jikin ne yau ta hanaki leko waje yar nan ?
Fadila tace jikin ne nima yanzu naji shirun yai yawa na leko ta na same ta a kwance sannu ta fada tana kallona a cikin damuwa da nuna kulawa a gareni.
Na amsa a cikkn daurewa ina kokarin yaye bargon dake saman jikkna wanda ya dameni a lokacin don dole nake kwance dashi.
Ki tashi ki karya fadila ta fada a cikkn kulawa nace zan watsa ruwa kafin na fita yasa suka bar dakin don na samu kintsawa hankali kwance.
Dogon riga mai laushi green mai adon dawisu a gaban rigan zuwa kasan shi na saka a jikina sai gyalen shi danayi dan kwanlin dashi a kaina.
A falo na same su zaune suna kallo na fito daga yanayi tafiyana ya nuna ban cikin dadin rai a tare dani.
Dining na nufa kai tsaye abinci na nan a gurin na diba kuma sai na kasa cin komai don hankalina yana gun yadda mukayi a waya dashi.
Da ido Fadila ke warning dina a yadda nake cin abincin da sauri na gyara sallon cakulan abincin a hankali cikin yanayin yauki da yanga kamar yadda ta koyar dani.
Muna falon har lokacin da halimatu ta dawo daga school tashigo da murnan ta tana kokarin fada min ajiki.
Anty fadila ta daka mata tsawa tana fadin kada ki fada mata yinin yau bata da lafiya gaba daya da sauri ta juinda inda nake zaune ta dan langabe kanta tana fadin.
Yayan mu sannu ya jikin na dan gyada mata kai alaman amsawa gareta ta zauna gefena tana fadin kinga yau tare da yaran gidan hjy din nan muka yi yawo a school.
Wanan akwai ki da iyayi har sai kin daukowa mutane zance a garin nan yaushe har kika sansu da kike kokarin cusa kanki garesu maizube ta fada.
To ba saboda yayan mu nake kula suba ta fada tana turo baki gaba alaman zancen da maizube tayi bai mata dadi ba.
Halimatu tashi ki shiga ki cire kayan ki na fada cikin bata umurni ta mike da sauri zuwa dakin kamar yadda na umurce ta tayi.
Alwala na dauro na gabatar da sallah tare da mika kukana ga sarki Allah wanda yafi kowa sanin dumbin damuwan dake tattare dani a rayuwana.
Kafin na mike na koma na kwanta dan banjin fita falon da ya zame muna wurin fita kawai a gidan don ko haraban gidan bama fita idan ba fita ya kama yi ba.
Amma kuma sai barci ya gagareni a lokacin sunayen Allah mai girma na dinga kira don na samu natsuwa har barci ya daukeni a hakana.
A cikin barcin nake mafalki da ya jafar yana tsaye ya harde hannayen shi yana kallona na tun karo inda yake tsaye.
Saiga wani yazo ya tsaya a tsakanin mu ya bani baya don haka ban samu ganin fuskan maishi ba .
A haka ina kalon su ban samu karasowa inda suke tsaye din ba ina kallo wanan mutumin ya jayeshi gareni ya tafi yana waigena a inda nake tsaye.
Sunan shi na kira da karfi wanda hakan yai daidai da bude idanuwana daga barcin da nakeyi din na falka a razane na gannin a cikin gumi.
Zainab wanan ihun fa Anty fadila ta fada daga kofan tana tsaye kai na dago ina kallon ta a tsorace take fadin nazo zan wuce naji kamar kina ihu na shigo.
Anty mafalki nayi na bata amsa take fadin barci a wanan lokacin baida kyau gashi har biyar na yamma yayi yanzu kina kwance.
Dago kai nayi na kalli lokaci sai na tuna da zancen sallah na mike don zuwa nayi alwala bayan fitan ta na samu fashin sallah yazo min a lokacin don haka na tsaye kawai na gyara jikina na fito daga bayin.
Naso na manta da zancen mafalkin nan danayi saidai abin ya tsaya min a raina sosai har yakai ina ganin abin kamar a zahiri a idona don irin kallon da yake min a lokacin.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.