Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 128 of 139
Don Allah ayi hakkuri da wanan din ba yawa sosai yar uwa dare yayi sosai ba zan samu karasa shafin nan ba yau.
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA MARASA LAFIYAN MU ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYA ALLAH YA KARA MASU LAFIYA .
YAN UWA MUSULMI DA SUKA RIGAMU GIDAN GASKIYA UBANGIJI ALLAH YAI MASU RAHAMA ALBARKACIN KALMAN LA, ILLAH HA,ILLAH MUHAMMADUN RASULILLAH ALLAHUMA AMIN.
NOVEL DIN KUDINE NA FADA BA HAKKI A TSAKSNINA DAKE RANAN TAMBAYA NAGODE ALLAH BADA IKON BIYA A KATANTA LAFIYA, , , ,
Zaman hjy a gidan mu zance kamar alherine a garemu baki daya don tsohuwar duk da tsufa da yai mata yawa a yanzu haka baisa ta barkace ba ga komai.
Wanan shi ake kira da tsufan mutunci zakaga tsofo a kamile komai nasa a cikin mutumci da addine yakeyin sa ubangiji Allah kabamu irin tsufan nan idan tamu tazo Allahuma amin.
Yau ma ina fitowa mukai kicibis da mama Ramatu da tafito kitchen yiwa mai aiki magana ta kawowa hjy ruwan zafi tasha shayi kafin tasha maganin ta.
Tana dawowa ina bude kofan yaya jafar din zan fito a lokacin mukai kicibis da ita jin karan kofan yasa ta dago ta kalli part din .
Nice ina rufe kofan ta dan sake dan murmushi a fuskanta daga can nisa inda take tana fadin har kin tashi ashe.
Ban iya bata amsa ba don nauyi da kunyan hakan a gareni ashe shigan ta take cewa hjy din ikon Allah koda ake cewa yaran nan basu damu da junan su ba auren nasu na gashi nayi kane sukayi ashe zancen ba haka yake ba hjy.
Nikan nasan cewa lokacin haihuwan nasu ne baiyi ba koda yaya ke fadin dama dai ai auren yinsa yayi don kada a matsa mai yarinyar ba sonta yakeyi ba har yanzu.
Tunda babu soyayya a tsakanin su da yarinyar yasa bai kulata har su samu fahinta nikan nayi mamakin hakan da yaya take fadi ai.
Dan murmushin manya hjy ta sake kafin tace da yar nata shin Ramatu kin taba ganin inda akai sharia kan mata da miji irin haka ?
Kyake yar ku kawai da halinta nina dauka kawai lokacine baiyi ba don Allah ba ai masa dole sai lokacin daya dibarwa mutum yayi.
Yaran nan duk kansu hankali ke garesu don basu fita fili suna fitsara irin na yaran yanzu yasa take fadin hakan amma ai mai hankali yana gane wani abu a tsakanin su shi.
Ina nan kuke hiran yadda ya rude da ciwon ta a asibiti har kuna masa sherin hakan kawai dai ku barta da halinta jinin sune bai hadu da yarinyar ba a yadda na dauka.
Sun dauki lokaci mai tsawo suna tataunawa akan mu da mami kafin su juya hiran zuwa hiran Nuriya matar ya mamud.
Nafito wanka na shirya kafin in fito dakin na nufi dakin da hjy take don in gaidasu da kwana a zaune na samesu suna hira ga abin karyawa da suka karya dashi a gefe daya.
Da sallama a bakina na shiga dakin suka amsa min nakai zaune ina fadin hjy ina kwana ya karfin jiki take fadin lafiya yar nan .
Ya naki jikin ina da sauki i yanzu nace Alhandullahi hjy na juya wurin mama Ramatu ina gaida ita ta amsa min a cikin fara tana fadin ya dare zainan an tashi lafiya Alhamdullahi na bata amsa.
Daga haka nakai zaune a gefen carper din da suke zaune suna hiran ga abinci nan ki karya hjy tayi min tayi.
Kafin inyi magana mama ke fadin a, a hjy da mijin ta suke karyawa fa yanzun kuma kyace ta zauna nan tace aiko zaku hadu dashi idan ya fito.
A daidai wanan lokacin yayi sallama ya shigo dakin saida ya kalli hjy kafin ya juyo ya kafeni da idanun shi har saida na tsargu.
Mama ya fara gaidawa sabanin ni dana fara gaida hjyn a lokacin dana shigo din dakin hjy ce tace kin gani idan na nuwa yar nan so da kauna kuga laifina a hakan kuna fadin wai nafi son ta da kowa.
Yanzu ki duba ina zaune amma dan nan keya fara gaiyarwa daya shigo shi dakin nan matar shi ko datafishi sanin muhinmanci na ai kinga ni ta fara gaidawa data shigo.
Bai bata amsa ba sai da yakai zaune kusa dani yake fadin wai mama mai wanam tsohuwar take fada ne haka tun dazun ?
Fada takeyi da kai ka fara gaidani kafin ita ya juyo inda take zaune yana fadin da me kike nufi in bar uwata da take zaune in fara gaida ke ?
Ai idan ina da rana ka fada randa babu ni yace baga iyayyena ba ina gani ta mere bakin ta tana fadin ke dai kawata kada ki biyewa wanan butulun mijin naki nayi murmushi kawai ina dukar da kai kasa ina dan wasa da hannuna.
Ta sake nunani tana fadin ka gani Allah ya baka mata mai.alkunya ba irin ka fitsarare ba mara kunya.
Haka ma wancan kanin naka mai irin zubin ka yazo jiya yana min huci kamar wani tsohon kimarci wai am bata masa rai.
Wa ke nan keda zubina ya tambaye ta take cewa masu suna irin dayan nan wanda yaso kwaso farin ka da tsayi.
Mama Ramatu tace jamal take nufi fa kasan ita hjy bata da gwani a wurinta jiya kuma kai aka yaba akan jamal din gashi yau kuma ana kushema.
Barta kawai ai idan mun tashi tafiya chaina da ita zamu tafi wanan karon hjy na fadin kadai je da uwarka gata zaune ni kuma ina dago kai ina kallon shi.
Don jin zancen komawa chaina da yayi a lokacin don na tsani inji zancen tafiyan nan namu a bakin kowa a yanzu.
Balle yanzu da nake ganin can din yake da babban matsalam rayuwa data shafi halin da yake ciki a yanzu yasa gaba daya na kara tsanar kasan a rayuwana.
Amma kai kadai zaka tafi wanan karon ko hjy ta tambaye shi ya kai hannu ya dauki wayanta dake gefe yana bin shi da kallo kamar yana nazarin wayan.
Ba tare da ya dago kaiba yace ita matar tawa gunki zan barta idan ban tafi da ita ba can din ?
Ni dai in tawa ce kabar yarinyar nan a kasan nan kusa da gida zaifi idan ka tashi kazo ka ganta yafi sauki wallahi.
Wayan dake hannun shi din ya aje mata a gefe inda ya dauka da farko yana fadin wanan sabon zance kike son dauko min hjy.
Yaushe zan iya zuwa in wani dawo nan kasan kuma yanzu banda wanan lokacin gara dai muna can din hankalina zaifi kwantawa ai.
Budan bakin mama Ramatu sai cewa tayi nima abindana fadawa yayan mu ke nan da take wanan maganan wai ba zaka koma da zainab din ba wanan karon.
Kamar ba hjy ce ta tsokalo maganan ba a yanzu dana dauka zata goyi bayan zaman nawa a nan sai ji nayi tana fadin.
Ku barshi ya koma da matarsa yafi mai kwanciyan hankali hakan ita lokacin da mijin ta yake raye ina can suke da zama gaba daya shekara da shekuru kuwa.
Ai kawai ku barta tabi mijin ta shi yafi, na fadawa mami hakan ba zai yuyu ba tun ranan don haka abar wanan zancen don Allah ya fada yana bata rai ya mike don barin dakin a lokacin.
Mama Ramatune ta tsayar dashi tana fadin nace ko zaka leka gidan yayane da safen nan ina son zuwa yau din akwai sakon da zan bayar akai min gida a can.
Haka yasa yaja ya tsaya yana sauraren ta kafin yace da ita ba yanzu zan tafi ba mama amma idan zaki tafi akwai driver a waje sai ya kaiki ai.
A lokacin na mike don barin dakin nima don idanuna ya riga da ya cika da hawayen takaici a lokacin nakai kofa yaja ya ban wuri tare da bina da kallo.
Yaki kawata hjy ta fada ban iya juyoba a lokacin kuma nasan dani take maganan sai dai naja na tsaya daga kofa kadan.
Au kardai ince kema din baki son bin mijin naki can ne yanzu mama Ramatu ta fada tana kallona.
A, a kada kuyi mata fassaran daba shi ba babu wanda zaiso yabar gida irin haka shekara da shekaru mutum naizo gida ba fa .
Tazo din kuma bai barta ta gama bin dangi ba ya tayarwa mutane da hankali kamar gareshi farau yin mata .
Yaki nan kinji kyale shi idan ba zaki koma ba yanzu sai ya tafi ya barki nan har ki kara ganin mu ai muma nan bamu gaji dake ba.
Baiyi magana ba sai fita da yayi daga dakin ya barni tare dasu baki hjy ta fara ban kan nayi hakkuri ai dama haka aure ya gada.
A cikin zancen su ne na fahinci tafiyan mu a yanzu bai da wani nisa ke nan duk da ni bai min zancen tafiya ba har lokacin.
Duk dana dan sake jiki munyi hira da hjy a dakin nata haka baisa na sake zuciyana kan zancen tafiyan namu ba a lokacin.
Tambayan da hjy din ta sako min ne ya dawo da hankalina gareta tana fadin ina dai kawata ba kin biyewa mijin ki bane kuna tsarin iyali nan da sukeyi na kafirai.
Lah hjy wallahi bai taba min wanan zancen ba tun zamana dashi kawai dai bama rayuwa irin na sauran ma,aurata dashine har yanzu , na fadi hakan don na kawo hanyar da tafiyan mu zai fasa a lokacin na fadi hakan.
Kamar ya ban gane hakan ba da kika fada yanzu don magana kikai min a dunkule hjy haka maganan yake dana fada.
Na fada ina dukar da kaina kasa lokaci guda ido hjy ta kura min na dan lokaci kafin tace ki min bayani yadda zan fahinta don wanan ba karamin magana bane kike fadi a yanzu zainab.
Shin kina nufin bai taba tabaki a matsayin aurataya ba zainab ko dai kina nufin bai gamsar dake ne yadda ya dace.
Zainab ki kwantar da hanlinki ki fada min gaskiyan komai yadda ya dace jafari ba fin karfina yayi ba dagashi har uwantasa zan iya daukan mataki a kansu kan hakan.
Jin ta ambaci sunana na sake fadin hjy haka maganan yake har yanzu bawai wani zama mukeyi dashi ba yadda ya dace haka.
Wai zancen nan gaskiyane ko al,mara nake ji don na dade da zargin hakan a gareku har in wanan zancen ya zamo gaskiya gaba dayan ku zan dauki mataki a gareku har uwan naku data boye min hakan.
Ba laifin mami a nan hjy don ina ganin bata san da wanan zancen ba har yanzu innalillahi hjy ta fada hankali tashe tana fadin shike nan yaron nan ya cuce mu a rayuwa.
Me yake nufi da hakan daya aikata ya tauye maki hakki yana daukan alhakin ki haka yar nan ko baida lafiyane ba a sani ba haka ?
Lafiyan shi kalau hjy kawai dai bai sha,awan mata ne yace na fada kai tsaye har ina mamakin kaina banda malam kakana ban taba irin wanan maganan da kowa ba a duniyan nan sai ita hjy da nake fadawa ranan.
Yau na shiga uku ni zainabu Abu kuna da wanan matsalan haka akai shiru aka saka maku ido a cikin sa.
A kira min mijin naki ta fada hankali tashe na mike da sauri na tashi zuwa kiran nasa inda nabar tsohuwar a zaune.
A falon shi yake zaune yana shan coffee mai zafi sai turiri yake tashi a cup din daga gefen shi ya bude laptop din shi yana aiki a cikin sa.
Na shigo ya dan dago ya amsa sallaman nake fadin hjyce tace na kiraka yace me kuma zan mata yanzu ya fada yana dan jan tsuki dagani aikine mai muhinmanci yakeyi a lokacin.
Akan zaman mune da kai na fada mata komai yau take kiran ka akanshi wani irin dago kai yayi yana fadin what da karfi tare da fadin me kika fadawa hjyn ?
Kanki daya kuwa zainab ko kin samu matsalane na dan kalleshi ina murguda baki kafin ince kaina daya wallahi.
Nadai fada matane don ba zan yarda in koma wurin wa yan nan muggan abokan naka ba a kashe ni a banza wanan kasan ba .
Ko a nan din sukaso kashe ki kina ganin ba zasu iya bane idan ma wasa kikeyi a hakan kinyi kuskure wallahi zainab ya fada yana ture computer shi a gefe daya ya mike tsaye.
Talkaman shi dake aje gefe daya ya zura a kafan shi ya fita nabi bayan shi ina kallon yadda hankalin shi ya tashi lokaci guda.
Har mun kai kofa yaja ya tsaya ya jiyo a hasale yana fadin ki gagauta gyara duk abinda kika fada a yanzu don kinsan condition din da hjy take a ciki yanzu .
Idan maganan ki ya kara ja mata matsala a yanzu ta kara kwantawa ciwo ki kuka da kanki ga duk abinda zai iya biyowa baya gun yayanta dake.
Baki da hankaki ne ko ina wayau ki ya shiga da zaki zauna kina wanan zancen da hjy at her age baki tunanen komai da zai iya biyowa baya ba.
Ya juya ya fara tafiya ina biye dashi har lokacin a bayan shi ba tare da jin komai ba na warning din da yai min din kan hjyn a raina ni dai kawai mafita nake nema a yanzu.
A tare muka shiga dakin dashi mun samu hjy tabar kasa inda na barta zaune tana jin mun shigo ta dago kai ta kalle mu .
Yanayinta gaba daya ya canza a lokacin kallon shi tayi ba tare data yi magana ba ta nuna muna kujera mu zauna.
Shi yakai zaune saman kujeran yana kallon ta na samu wuri a kasa na zauna sai dan shiru ya biyo a dakin .
Can ta dago kai ta kallemi tana fadin yanzun muna hira da kawata nake bugun cikin ta a haka naji wani maganan daya daure min kai a tare daku jafari.
Me kikaji hjy ya tambaya ta kalleni tace takwara sake maimaita abinda kika fada min yanzu a nan.
Na dukar da kai kafin na sake dagowa ina fadin cewa nayi a matsayin budurwa nake da kike tambayana ko nasha maganin haihuwane ban haihu ba har yanzu.
Hjy ya tare da fadi nasan zainab a yanzu zata iya fadin komai da zai kawo rashin komawan ta can tare dani .
Nagodewa Allah dake ta fadawa wanan maganan haka ba wani ba ai gata a zaune me na rage ta dashi na zaman takewan aure da akeso namiji yaiwa iyalin shi.
Duk mai hankali dai ya dubi zainab a yanzu yasan bata tare da wani damuwa a gidana shi haihuwa ba Allah ke kawo shi ba idan lokacin hakan yayi.
Nasan ina da rauni kwarai wurin mu,amula da taraiya da ita a yanzu na kuma sha bata hakkuri a kan hakan tun da ni din ba mazauni gida bane ko yaushe.
Hjy tace a, a takwara wai haka maganan yake dama kika barni ina tunanen wani abu har hankalina ya daga haka ?
Hjy ni dai ki masa magana gaskiya bana son komawa kasan nan wallahi na fada kamar zanyi kuka a lokacin.
Don ga daman magana ya samu a gareni kuma hakan yanzu ba zai yuyu ba don ya samu wurin fakewa akan ciwon hjy din wanda gaskiya ne ya fada kuma.
Wani abu zai iya samun hjy din a dalilin maganan mu din gaba daya zasu dawo su tsaneni kan hakan danayi tunane.
Sai kawai naja bakina nayi shiru ban fasa kwan gaba daya gun hjy ban da nasan zata dauki mataki a kanshi.
Sai ga hjyn ta koma fadin nasan maza da yawa a zamanin nan suna irin haka ga iyalin su wanda hakan ba daidai bane sam wallahi.
Kuna shiga hakkin iyalan ku da yawa akan aiki da iyakarshi a wanan duniyan zaku barshi yau ina mahaifin ka yake ya rasu ta ba kanta amsa.
Duk ko son aikin ka ina ganin bakai na balarabe ba shi da ko yaushe kaje gidan sa baka masa ganin daya kai uku ko biyu ko yaushe yana kashen duniya yana aiki.
Kuma hakan bai hana shi zama da iyalin shi ba ai har a sameku don haka ina kara tuna maka a yanzu tunda har kaji yarinyar nan ta fadi haka.
A gaskiya tauyewan yayi yawa a gareta ke nan tunda har yana cikin korafin da zata iya fada .
Kada ka manta da yadda auren ku ya kasance da yar nan a baya don haka ka guji duk wani abinda zai kawo matsala a tsakanin ku yanzu.
Hjy indai wanan shine matsalan za a gyara da yardan Allah ya fada har lokacin bai tare da walwala a jikin shi.
Tun daya fita dakin ya barmu hjy tana saman bakin ta dani har akai azahar muka mike don zuwa sallah.
A inda na idar da sallah naji kawai nayi amfani da kayan kakar maya a ranan ya kamata in gwada ko wani kamar yadda tace min inyi dasu.
Nayi din ko wani har sha da shafawa da dai sauran su don su ba hayaki a cikkn maganin su sai dai sha da shafawa kawai zanyi a jikina.
Tun dana shafa ban fito ba duk da baka sanin nayi amfani dashi ma don haka na shige daki abina shima bai leko dakin ba kamar yadda ya saba idan yana gida.
Ban kuma kara ganin shi ba sai da dare da zamu kwanta barci na shiga dakin na sameshi yayi zaune ya daga kai sama yana tunane har nayi sallama bai amsa min ba.
Nima idona ya bushe a yanzu game dashi don haka ban damu da amsawan shi ba a lokacin na gama abinda zanyi na kwamciya na kwanta abina ba tare dana tanka mashi ba.
Ban sani ba ashe maganin yana aiki a kanshi a lokacin ya fara jin wani irin bakon yanayi yana sauka a gareshi a hankali har bai san lokacin da magana yazo mai ba.
Ina hawa gadon naji muryan shi yana fadin ke wani irin abu kika shafa haka mai kamshi ya sawa mutum kasala da hawa kan mutum ya fada yana dan lumshe idanun shi kafin ya sake fadin yayi min karfi a kai.
Ba tare dana kallo shi ba nace ban shafa komai ba sai turaren dana saba amfani dashi kullun na shafa na fada ina jan bargo zuwa jikina.
Banji takowan shi ba sai ganin shi da nayi a kusa dani tsaye gaba daya idanuwan shi sun canza kala kamar ba nasa ba yana fadin ina tambayan ki kina kokarin kwanciya ki kyaleni.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.