Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 104 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWABARKAN MU DA SHIGA WANAN WATAN MAI ALBARKA YAN UWA UBANGIJI ALLAH YA SADA MU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN WATAN ALLAHUMA AMIN, , , ,
LITTAFIN KUDINE YAR UWA KADA KI MANTA DA HAKKAN DON KAUCEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , ,
Akwana a tashi ba wuya a wurin Allah yau gashi har na kamala karatuna a ta fannin fasahar kimiya a kasan chaina inda na fito da sakamoko mai kyau wanda yaya jafar ya nuna jin dadin hakan a fili har ya kasa boye farin cikin shi ga hakan.
Yayin da sadiya take matakin yar gaba da primary a shekara na biyu zata shiga na uku a yanzu daidai lokacin dani na kare nawa karatun .
Har lokacin muna matsayin kannesa ne ga ya J da muke zaune a gidan shi wanda kuma ta dalilin shi muka samu wanan matakin na ci gaba da muka samu a rayuwan mu.
Eh ba zance ya j ya daina duk wasu mugayen halaiyan sa dana san su a baya yana yi ba don a yanzu in ma har yana yine saidai in a boye yake wanan rayuwan do banga hakan a gare shi ba gaskiya.
Asalima a yanzu ga baki daya ya koma kamar ba ya J din da muka sani a baya bane don ga baki daya ya canza gaba daya .
Ya koma wani irin mutum mai taushi da tausayi ga ibada da kula a tare dashi ga natsuwa da kamala da kullun yake kara sauka masa.
Banga wani shirin da yaya yakeyi don zuwan mu gida ba asalima ni yanzu da zaman gida kawai nakeyi yasa wanan damuwan yake damuna a raina har karshe na kasa boye hakan a zuciyana.
Yau tun safe na tashi da wanan damuwan a raina gashi ni kadai ne a gida haka zan wuni daga kallo sai in shiga interneat ina searching shine kawai aikina.
Ina zaune a babban falon mu tv na aiki saidai ba kallon nakeyi ba hankalina yana gun computer na dake gabana ina hada wani kimiyan da nake tunanen hadawa danaga ana tallan shi ko ina a kasan.
Pretty me kikeyi haka ya fada a bayana na dan dago kai na kalleshi tare da dan sake murmushi a fuskana ina fadin yau ka dawo da wuri haka yaya ?
Na dawo ne don nasan ke kadai ce zaune a gida yanzu yasa naga ya dace ba dawo ba dubaki ashe ma na manta kina da abokin hira gashi a gaban ki.
Wanan bai rage min komai yaya sai kewan gida da yanzu yake damuna sosai ina son zuwa gida na ga Inna ta da yan uwana yaya .
Wani kallo yayi min daga inda ya zagayo ya zauna a gefena gida a yanzu baki ganin yin hakan zai taba karatun sadiya ?
Ai ba don karatun ta muke nan ba na fada a dan hasale OK tunda ke kin karasa naki zaki fadi haka ko ?
Ba hakana bane yaya gani nayi kayi alkwarin hakan a baya don Allah yaya ka kaimu gida mu duba su yanzu kusan shekara biyar ke nan muke nema rabin mu da gida fa.
Ba yanzu ba zainab gaskiya don so nake kici gaba da karatun ki a cikin shekaran nan in Allah ya yarda.
Ba zan tsaya karatu ba a nan gida zan koma karatun ya isheni haka yaya nima fa haifana akayi zanso na samu ladan da ko wani da ke samu ga hakan.
Bai min magana ba sai mikewan da yayi lokaci guda ba tare da yai min magana ba ya fice a falon na bi shi da kallon mamaki.
Wanan dan maganan ya jawo muna dan tashin hankali a tsakanin mu har yakai munyi dan kwanaki baya kula wani harkana a gidan yana shan kamshi dani.
Ban shiga harkan shi ba duk da hakan yana damuna sosai don sai yanzu na san ashe ba karamin sabone tsakanin mu a yanzu.
Tun ina daurewa har ya kai na kasa hakan ina shawara kan na same shi na bashi hakkuri sai dai nakan tambayi kaina idan naje ince masa me ?
Ban san ya ake abi sallon ba miji hakkuri ba indan irin haka ya faru a tsakanin su balle mu dake zama irun na wacin gadi da juna kinga hakan ashe zai min wuyan fahinta don nawa kaddaran auren yana daban dana sauran mata gaskiya.
Don haka ban kara gigin wanan shawaran a raina ba don haka na kawo ido na zuba mai kawai na bisa a hakan kowa yana harkan gaban shi a tsakanin mu.
Ina kallo sai dai ya dan shigo yai magana da sadiya ba zai dade ba ko ya zauna zai fita sai kuma gobe.
Saidai hakan ni bai hana in ya shigo da safe na gaidashi ba ya amsa min a dakile gashi ba inda zan kaishi kara inji sanyi .
Wurin mamine nasan ko nakai goya masa baya zata yi kan hakan karshe ma ta kara min wani zafin da yafi wanda nake ciki a yanzu din.
Don kanshi ko me ya gani ranan muna zaune falo da dare da sadiyan ba wani hira mukeyi ba sai rage dare a tsakanin mu ya shigo.
Ga hasken kwan falon na wuta ya haska mu tar ina zauna a cikin wani riga mai shara shara a jikina rigan baida hannu sune irin kayan dana sakawa a kasan don yana sauka min har kasa .
Gasu su ba jallabiya bane ba kuma abaya ba haka suke kamar kayan yan brazil da sukafi amfani dashi wurin wani bukukuwan su na shahara.
Sai dai ni da ba bukin nake zuwa ba a gida nakan saka abina ko shi ba don kwaliya ba don dai kawai ina dasune da yawa nake amfani haka dasu.
Kayan suna min kyau sosai a jikina idan na saka saidai ba wanan a raina nidai zan saka kawai don ba wanda zan burge ga hakan idan ma nayi ne don shi din ba wai burgeshi zanyi ko jan ra,ayin shi ba a kaina.
Sadiya yau kuna wani show ne a nan banda labari ya meka gani ta fada tana dagowa daga kwancen da take tayi rub da ciki saman kujera.
Gani nayi dai yau kunyi wani kyau daku ko zamu fitane ku ga gari ko kada wanan kwalliyan haka ya tafi a banza.
Ba a banza bane yaya tunda ka gani har ka yaba ai idan mace tayi kwalliya a mijin ta tayi akace .
Daga inda nake zaunw na watsa wa sadiyan wani kallo mai harara don abinda ta fada din nake fadin.
Miji sadiya yaushe nayi auren har zan wa mijin kwaliya ya gani dani da wance bata da aure babu bambanci a tsakanin mu a gun wasu daine nake matar aure kamar su inna da sauran yan garin mu.
Maimakon yai fushi da abinda na fada sai gashi ya wasance yana fadin sadiya kin yarda dav zancen nan nata wai ?
Gaskiyane yaya duba ga har yanzu bata haihu ba tana da wanan hujjan don burin su inna a kullun tayi waya damu zanji tana tambaya wai har yanzu shiru babu labarin haihuwa gareta ?
Killa shiyasa ta fadi hakan yanzu duba ga sauran yan kauyen mu sa,annin auren ta ai duk suna da haihuwa biyu ko ukku wasun su ?
Sadiya naso ace kin girma a gaban su inna da wanan wayau naki bazai dauki garin naku ba mema sunan kauyen naku ?
Lah yaya har ka manta da sunan garin namu niko ko barci na tashi akace min meye sunan garun mu zan ce Anchau da gudu.
Yau hausa suke a tsakanin su sosai don bai faye mata magana a cikin yaren hausa ba nice dai koda yaushe hausa nake mata a tsakanin mu don kada mu manta da yaren mu mu koma gida ai muna dariya wata rana.
Idan ba haka ba sai ince da yanzu sai turanci da yaren yan garin da take ji a yanzu don saurin daukan yare dake ga yaro ko ni ba a barni a baya ba wurun daukan yaren su don ina jin wasu masu saukin dauka a yanzu duk da ban mu,amula da kowa sosai kamar maya da yanzu naje gidan su yafi a kirga don kaina .
Gashi duk zuwa kakan maya din sai ta hada min maganin irin nasu ta ban wanda ban san irin amfanin su ba a gareni ina dai karba ina sha don sanin ba masu cuta min bane.
A zancen da yakeyi da sadiya din kuwa raina yakai kololuwar baci a lokacin dashi don fadin wai ya manta da sunan garin mu a cewan shi yanzu.
Ba abin mamaki bane don ka manta da sunan mahaifan mu ai yanzu tunda ka biya bukatan da kake dashi akan mu.
Murmushi ya sake tare da fadin ai ban isa in manta dasu ba a rayuwana sunan garin kawai na manta kuma sadiya nake tambaya ta fada min ba wani ba.
Ai gata nan sai ta fada ma da bakin ta kafin ma na rufe baki sadiya tace dashi ANCHAU ne sunan garin mu yaya.
Gaskiya sunan garin akwai dadi sosai kuma gashi garine da ya tara manyan yan boko da suka san kansu a tahirin kaduna kaf.
Yanzun ma ga wasu karin an samu harda yan scientic a cikin su mata masu kera fasaha da kansu don wanan matar tawa nan gaba .
Sai lokacin na gane zolaya yazo dashi akaina na neman jin bakina kawai yasa ya fadi haka akan garin mu.
Nace gara dani nasan asalin garin mu wasu ko kauyen su basu san hanyar shi ba har yanzu sai kame kamen garin wasu sukeyi da sunan nasu.
Sadiya ke kinji akwai wanda zaice bai san asalin garin su ba ko ga suna idan ba karya ba.
To idan nan sani din a tafi mana in ba tsoro ba na fada ina kwashe kafafuwana ina dorawa saman kujera tare da kawar da kai a gare su.
To zamu gani idan mun je Nigeria idan wani zai nuna min hanyar asalin garin mu lokacin da nake zuwa ke kina ina ?.
Zamu gani idan an tafin ai in ba burgan aiki ake muna ba a nan don banga alaman an sanda yan kauyen ba sai yan birni.
Wai yaushe zamu tafi gidane yaya sadiya ta tambaye shi da saurin don jin yace idan mun tafi Nigeria zai kaimu garin nasu.
Zamu tafi idan ki samu hutu sadiya har in yayi daidai da lokacin banda aiki sosai zamu tafi.
Ko yanzu dai ba wani amsa mai karfi na fada a raina ina dan tunane kafin naji sun buge da hiran gida shi da sadiya din fitan da basuyi ba ke nan a ranan sai washe gari muka samu fita dashi ya kaimu yawo cikin gari tare da yin sayyaya mai yawa muka dawo gida dashi a cikin farin ciki iyakar abinda ke tsakanin mu ke nan dashi ko yaushe.
Da irin wanan har muka shirya fada ya kare a tsakanin mu a yanzu mun koma daidai a tsakanin mu yakan shigo mu dan taba hira da yakan yi kamar na dole wani lokaci.
Wani lokaci zanyi zargin bai daina komai ba a cikin halaiyar shi don ba wani canji da nake gani dake nuna ya daina din.
Abinda ban sani ba shine abune mai wuya ashe koda mutum ya daina wasu halaiyar shi ya dawo daidai lokaci guda kamar yadda nake tunane ni.
Abin ba haka yake ba don shima yaya din yana fama da kansa ne sosai boye hakan yakeyi kada mu fahinta da hakan.
Haka zai ta fama da ciwon ciki wanda bai san kanshi ba sai da kyar zai samu ya lafa mai ko kuma wani kumfa mai kauri ya dinga fita mai a baki zai wuni yana fama da wanan laluran yana faman shaye shayen abinda zai lafa mai da ciwon .
Ranan ya fita wurin aiki sai gashi zuwa karfe daya sai gashi ya dawo ina dakina kwance ina barci .
Dakin shi ya nufa a gigice ya fada saman gado a yadda ya shigo din ko takalman kafan shi bai cire ba don zafin ciwo.
Kamar a mafalki nake jin wayana yana ringing da kyat na bude idona na kai ga wayan na dauka muryan shi babu dadi yake fadin.
Wanan maganin da kika taba bani nake son ki bani yanzu idan akwashi a wurin ki har yanzu ?
Kana ina yanzu yace part dina kwance banda lafiya tun daren jiya da kyat na samu na fita yau dama.
Maganin na dauka na jika kamar yadda tace na nufi wurun shi wani irin juyi na sameshi yana yi shi kadai a dakin da sauri na karasa inda yake din ina mashi sannu.
Ya tashi da kyat yana karban maganin ya kafa kan shi saida ya shanye ya cire baki sa yana miko min cup din daya sha maganin.
Zaune nakai gefen shi tare da kura mashi idanu na dan lokaci sannu a hankali na fara ganin yana karya zufa a goshin shi sai barci.
A cikin dabara na cire mai takakman kafan shi sai ya bude idanu shi ya sauke a kaina tare da fadin nayi barci ne ko ?
Wai da takalman zan cire ma ko zaka ji dadin barcin nan wurin ne yake yawan damuna sosai sai yayi kamar ya bari kwana biyu kuma sai naji ya motsa min ba dadi wallahi ya fada yana bata fuskan shi.
Da zaka daure ka sha maganin na yan kwanaki mu gani ko Allah zai sa a dace a hakan zan sha ya fada a dan maraice yana lumshe idanun shi a haka barci ya daukeshi yana sake ajiyan zuciya kamar karamin yaro.
Tagumi nayi ina tunane ni kadai a dakin sai bin ko ina na dakin nakeyi da kallo amma a can kasan zuciyana sai tunanen kada fa wanan abin ya halaka wanan mutumin ta dalili na.
Don yanzu kan na yarda da cewa maganin kakar maya ce ke bashi wanan matsalan haka yake hanashi sukuni da sakashi yawan ciwon mara da ciki da yake complain ko yaushe .
Lalai idan haka din ne kuwa ya zama dole in koma wurin kakar maya in mata bayanin komai dake faruwa kan abinda ta bani na bashi din yasha .
Don ni har yanzu ba wai naga wani canji bane a gurin shi banda wanan matsalan dake taso mashi na yawan ciwon mara din.
Gashi har shi kanshi ya fara zargin hakan don wanan zancen daya taba fada min a gaban mami din ya nuna yasan na bashi wani abu yasha da yake zargin hakan.
Kwana biyu yana shan wanan dan abin mai kama da kankara da nake jika masa yasha yana kuma dada kara samun sauki don idan ya sha sai wani irin zufa ne zai dinga karyo mashi a duk kafofin jikin shi lokavi guda sai ya tube yana neman sanyi a jikin shi.
Haka yakanyi duk tsawon kwanakin nan da yake shan wanan maganin dan hakane ma baya sha yanzu sai da dare idan zai kwanta.
Na gama bashi maganin na juya zan fitane naji yana fadinn wai zainab waya baki wanan maganin da kike bani ne ?
Na tambayeki ranan baki ban amsa gamsashiya har nake zaton ko mami ce ta aiko maki dashi ki bani tace bata san zancen ba ?
Dan shiru nayi kafin na dago kai nace mai na fada ma dashi nazo garin nan dama ina dashi a wurina nakan yi amfani dashi idan cikina yana ciwo.
A zaton ki zan yarda da wanan maganan da kike fada ne ko kin mata farkon zuwan mu kasan nan kiyi ciwo mara saida aka kaiki asibiti ?
Baka yarda ba ke nan dani ai da kada kasha tunda zuciyar ka yana baka zan iya cutama ne da maganin .
Ban ce hakan ba amma kin san dalilin da yasa kike min amfani dashi wanda yasa nake zargin hakan a kanki sai yanzu na kara tabbatar da hakan.
Kada ki dauke ni karamin yaro da baisan abinda yakeyi ba zainab na kallo shi da sauri don jin abinda ya fada yace eh.
Na dade da sanin komai shiya har da farko nake zargin ko mami ce ta baki kiyi min amfani dashi ashe tunanena bai bani daidai ba.
Kece don kanki kika ga daman yi min amfani dashi ai da saiki fada min tun a Dubai da kika fara saka min nasha wahala kamar zan mutu.
Kin ko san kwana na kawai ke gaba a wanan lokacin dan da zan iya mutuwa a wanan lokacin.
Hawaye ne yazo min masu dumi kan maganan da yake fada min din na kasa furta komai sai hawayen da nake zubarwa kawai.
Babu abinda zan iya fada tunda har ya gano hakan a yanzu nace dashi don kawai yana wanan halin na bashi magani ya daina ko don ina son shi nayi masa hakan bai sani ba tunda gashi yana fadi da bakin sa ya san na bashi wanan maganin kan wani dalili nayi hakan zan bashi amsa.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.