Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 61 of 139

🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

5️⃣1️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

YAR UWA DON GIRMAN ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA, DARI UKU NE KUDINSA DON NEMAN KARIN BAYANI KI KIRA WANAN LAYIN 08036959257, , , , ,

Shiru babu wanda ya bude kofan hakan yasa na tura kofan a hankali na shiga dakin csn na hango shi zaune saman sallay yana azzakar da counter a hannun shi.
Jin alama an shigo mai dakin yasa shi dago kai a hankali daga inda yake zaune ya hada gwiwan shi biyu wuri daya ya hade da hannayen shi saman kafan da counter din shi yana danawa a hankali.
Idon shi ya sauke a kaina kafin nayi karfin halin karasawa wurin shi a hankali ina fadin bansan kana ibada bane dama nazo fadama abinci na saman dining an shirya ma.
Kai ya gyada min a kasalance ba tare da yai min magana ba ganin haka yasa na juya da sauri don barin dakin don gabana dake fadawa ban ko tsaya yiwa dakin kallon tsab ba don ganin irin alatun dake cikin dakin nasa.
Duk da ganin namu dakin da muke ciki ya kai iyakar haduwa wurin tsaruwa sai naga wanan din nasa kamar shagone na shiga.
Ke jimana naji muryan shi a bayana yana fada a hankali naje na tsaya ba tare dana jiyo na fuskance shi ba don yadda yai maganan.
Da ban nan mami tazo gidan nan naji tambayan yazo min a bazata don haka na basa amsan tambayan da fadin ya mamud daine yakanzo dubamu sai ko ya jamal da yazo sau biyu .
Tsaki yaja yana mikewa tare da fadin ba wanan na tambaye ki ba ai nasan da mamud yana zuwa dubaku ai.
Gabana yayi dam sai nayi shiru don yadda ya katseni a cikin fada lokaci guda abin ya ban mamaki matuka.
Don haka tun bai fadi komai ba kuma naja kafana na bar dakin don gudun wani fadan kuma.
A tsakiyan falo na hango Tajjuddeen tsaye kamar yana nazarin wani abu saidai yana ganina ya nufo inda nake da sauri yana fadin.
Me kika shiga yi dakin ogo a yanzu wa ya baki daman shiga masa daki a wanan lokacin?
Idanu na zaro a tsorace don don jin irin tambayan daya jefo min a bazata wanda imani da tsoro tambayan ya mamayeni lokaci daya.
A cikin karfin hali na bude baki nace waya aikoka tambayana wanan dalilin yanzu.
Wani irin kallon tsana ya watso min kafin yace dani babu saidai hakan kada ya baki daman kusanta kanki gareshi kuma.
Kaina na dukar kasa nayi dan shiru kafin in dago a fusace ince dashi matsayin ka da kimar ka baikai ka yi man wanan tambayan ba a yanzu .
Kafin in bude baki in bashi amsa ya nunani da yatsa a fusace shima yana fadin ke ni zaki rainawa hankali ashe baki da kunya da nake ganin ki haka ?
Gaskiya jackson ya illanta maki rayuwa daya tsaya ya mayar dake mace haka mara moriya gashi kina neman kai kanki ida matsayin ki bai kai ba.
Idanun sa sun kada sunyi jawur zuwa tsatsan bacin rai dani haka nima domin maganganun shi sun daga min hankali sun tsoratani lokaci guda.
Na runtse idanuna ina jin kuna da radadi a zuciyana kafin in bude udanun nawa na sauke su a kanshi cikin tsana ina fadin .
Dakata wai malam ka daina yaba min kalamai kamar wani ya aikoka gareni kai a wani matsayi kake da zaka tsareni da wanan maganan akan mijina.
Ciki da alaman mamaki ranshi bace ya ware idanuwan shi a kaina yana fadin what ke kanki daya kuwa yarinyar nan kinsan ko wa nake a wurin jackson ?
Nima a fusace nace gomane gareni kai waye da har zaka tsareni da wanan dokan akan ya jafar din.
Daki kuma ko gobe zan shigesa ne don dakin mijinane bana wani ba kai wani matsayi kake dashi a wurin shi daya har ya baka daman yi min wanan tambayan ?
And kuma ka sani duk duniyan nan banga mahalukin da a yanzu ya isa min wanan banzan tambayan da kai min ba a yanzu kokai ka fadane a cikkn maye kila.
Kamar yadda kace rayuwata ta samu illa idan har hakane ina ganin ai wanan damuwatace bana wani ba ko ?
Daga hakan na juya na barshi a wurun tsaye baki bude yana bina da kallon mamaki don jin abindana fada.
Nayi kokarin mayar da mood din fuskana a hakan bai dameni ba saboda kar ya gane maganan shi yayi min ciwo sosai a raina.
Harna nufi hanyar dakina sai na canza shawara na nufi dakin anty fadila a lokacin saidai bata a cikkn dakin yasa na jiyo don na koma dakina cike da bacin rai atare dani.
Da kyar na samu na karasa daki na shige a take naji wani irin zazzabi yana neman ya rufeni lokaci guda.
Gado na fada na dafe kaina gabana yana faduwa nake fadin wanan sace irin bakar ranane haka gareni da har wani dan aiki zai fada min irin wanan magana kai tsaye.
Komawa nayi na zube rigingine ina lumshe idona yayin da buguwan zuciyana yake karuwa gareni lokaci daya.
Na dade kwance a hakana kafin tunane yazo min ina tambayan kaina shi din wai wani irin matsayi yake dashi a gurin ya jafar din da zai min wanan kalamin haka ?
Cikin wani hanzari na mike zaune bandaki na fada na dauro alwala nazo na hau sallaya na fara sallah ko wace ruku,u da sujjada sai na gayawa mahaliccina Allah damuwata kafin na danji sanyi a zuviyana.
Ban kara fitowa falon ba kamar yadda anty fadila ta umurci inyi don wanan maganan da mukayi da tajjudeen din ranan ga abi kuma ya tsaya min a raina sosai don ko barci bai barni nayi ba sai faman tunane da nakeyi a daki ni kadai.
Washe gari ma ban leko waje ba har wuraren sha biyun rana ina dakina a cikin damuwa da fargaba da zancen wanan mutumin a raina .
Gashi lokaci daya duk nabi na susuce ga baki daya idan mutum ya kalleni zai fahinci ina cikin damuwa a tare dani.
Suko a zaton su maizube ina wurin yaya jafar dinne a can na kwana a wurin sa don hakane ma tunda ta shige dakinta bayan zuwan shi bata sake fitowa ba har wanan lokacin.
Anty fadilace da tajini shiru ta leko dakin sai ta sameni a kwance cikin wanan yanayin na damuwa a tare dani din.
Tunda ta shigo dakin take watsa min kallo a razane kamar tana nazarin yanayina yayin da niko ganin ta dakin nawa yasa na dan kakaro fara,an dole a tare dani.
Saida ta kai zaune a kusa dani take fadin meke faruwane dake haka kin rame haka a cikin kwana daya ?
Kina da wata damuwa ne a tare dake da ya mayar dake haka lokaci guda duk kin zabge ko wani abin ke damun ki haka ko kuma ganin mijin kine ya sakaki fargaba ?
A ladabce nace da ita a, a anty lafiyata kalau illa dai kewan innata da kannena da nakeyi duk kwana kin nan.
Murmushi tayi taba fadin baki tashi kewan su ba saida mijin ki ya dawo kika saka damuwa haka a zuciyar ki lokaci guda.
Kaina na sada kasa ina dan murmushin yake kafin naji tace kinga fada min damuwan ki zainab don nima akwai abinda yake damuna dan zuwan mijjnki garin nan .
Don ba wani ya fada min ba Allah ya nufa inji komai a kunnuwa na yau din nan da safe na fito don duba masu girki dazu.
Da sauri na dago kai ina kallon ta don jin karin bayani daga abinda take hashe din lokaci guda kuma sai kunyar hakan ya lulubeni dan ganin yadda take kallona na kasa fassara hakan.
Naji tace watau zainab dazun din ne na tsunkayi wanan mutumin na tare da mijin ki yana waya a hasale .
Saidai jin abinda yake fadane yasani maida hankali in saurare shi dan na fahunci zancen kamar ya shafeki ko wani a gidan nan duk da ban tabbatar da hakan ba gaskiya.
Don naji yana fadin gaskiya ogan mu bai kyauta min ba ni a yanzu na tsani na bude ido inga wanan yarinyar a gidan nan.
A yanzu nayi nadaman yardan da mukayi har wanan mukai sake yarinyar nan ta kai haka tare dashi don yanzu gaba daya ta juye ta zama wata haddadinyar mace sosai.
Katseta nayi ina fadin anty wallahi dani yake don jiya nan da kika turani kiran yaya don na fito part din ya tsareni yana fada wai in daina shiga gun yaya din nan dai na labarta mata komai daya faru tsakanin mu.
A gigice tace wanan zancen da daure kai yake wallahi don haka kawai baki masa komai ba zai tsaneki haka ba tunda bashi ke aureki ba ai.
Me hakan ke nufi ne gareni kuma anty na tambaya cikin damuwa da tashin hankali a tare dani.
Kinsan wasu basu iya samun wuri ba ai sai sucd basa son kowa ya rabu yaci arziki sai su kadai hanyar jirgi daban ta mota daban don haka ya tsaya a matsayin sa zanwa maigidan magana kan hakan ai ta fada tana mikewa tsaye.
Ki tashi ki fita ki sake gidan kine mijinki ne banga wani da ya isa yazo yai maki wani iyawa ba a nan yanzu gaskiya don haka kada ki fara kiyi sake har hakan ya faru dake.
Har ta soma tafiya nace anty dama kin kyaleshi ai kada ki masa magana har sai idan ya kara min irin hakan zan so ayi mai magana din.
Saida ta dan tsaya kamar tana nazari kafin tace to shike nan tunda haka kikaga yafi a barshi in halinsa ne zai sake raina maki wayau ai dan iska damani sam bai kwanta min a rai ba ko kadan.
Bayan fitan ta wanka nayi na fito saida na dan dauki lokaci sosai ina kimtsa jikina a gaban mirrow kafin in shirya in fito waje sha biyu har ya gwauta a lokacin.
Tun daga nesa nake dan jiyo hayaniya a falon gidan ina dan jin muryan ya jafar din kamar yana fada sama sama wanda ban taba ganin hakan ba a tare dashi.
A hankali na tako ba tare dana san ko su waye yake tare dasu ba dasu
a falon a lokacin hankalina kwance na nufo falon .
Wanda na gani sanya saura kiris na juya don saida na kadu sosai ba kowa bane sai mami da anty Aisha a zaune tare dashi a falon .
Gaba dayansu suka juyo suna kallona a cikin mamaki da kaduwa da ganin canzawa da nayi na lokaci guda.
Mami ta dan yatsune fuska gami da tsuke fuskan a lokaci guda ta mike tana fadin ni zan koma ke nan tunda na ganka kaji sauki.
Saura kiris na sake futsari tsoron ganin mami din a bazata naga Aisha ma ta mike kamar a bazata ta ganni tana fadin cike da mamaki a fuskanta.
Zee a gidan nan dama kike zaune wai ko zuwa kikayi kema bata karasa ba don wani tsawa da mami ta daka mata lokaci guda yasa tabi bayan mami din da sauri.
Har lokacin na kasa magana sai ido nake binsu dashi a cikin tsoro da fargaba kafin na tattaro karfi da kuzari lokaci guda na bisu zuwa kofan fitan da suke shirin fita ina kokarin gaida mami din a cikin ladabi.
Tana kokarin shiga mota na karaso wurin da sauri tare da dan rusunawa ina kokarin gaida su banyi mamaki ganin irin yadda ta amsa min gaisuwan nawa a dakile ba don ba yabo ba fallasa.
Irin kallon da Aisha ke bina dashi na mamaki yasa na kara shan jinin jikina ban bar wurin ba sai da naga motarsu ta daga daga farfajiyan gidan don ko kallona mami bata kara yi ba a wurin.
Ajiyan zuciya na sauke don abin ya ban mamaki wanan wani irin kiyayya mami take nuna min hakane na ba gaira ba dalili a kaina.
Juyawa nayi na koma cikin falon gidan jiki ba karfi don ban taba zaton zamu hadu da mami irin haka ba a wanan lokacin.
Bansan har na tsaya ina tunane ba a wurin saida naji takon mutum a bayana firgigit nayi tare dajuyowa shine a tsaye daga kofa ya tsura min ido kafin ya fara takowa zuwa inda nake a nutse.
Yaja ya tsaya a gabana sai nayi saurin dukar da kaina kasa ina wasa da yan yatsun hannuna a hankali.
Maman ki har yanzu fushi takeyi damu kiyi don haka kiyi hakkuri da duk wani abinda zaki ga tayi maki a yanzu.
Samun kaina nayi da sake dan guntun murmushi a fuskana ina fadin ayyah mami har abada mami a matsayin uwa take a garen ai.
Don nima nayi missing din uwata mai tausayina da kauna na har kullun saboda kin bin umurnin ta danayi
Zan shanye duk wani bacin rai da mami zata nuna min har zuwa lokacin da Allah zai huce mata zuciyar ta akaina.
Ina fadin hakan na juya na fara tafiya don barin wurin don kiris nake dana sake hawaye a fuskana don bacin rai ga yadda mami din tayi min kamar taga mugun abu a lokacin.
A bangaren mami kuwa rai bace ta shiga mota sai masifa takeyi tare da fadin na fara yarda da zancen mutane da suke fadin harda asiri a
wanan zancen.
Yaushe na koma haka har yaushe na samu sauyin yanayi haka gaba daya na canzawa ganun ta idan badon a ko ina ta ganni zata iya shedani ba don zaman da tayi a tare dani da shakuwan da mukayi a baya.
Da sai tace wanan watace mai kama dani dai amma ba ni zainan din da ta sani band na canza haka lokaci guda a dan watannin da tayi bata ganni ba.
Muryan Aisha ya katse mata tunane da take fadin mami kinga yadda yarinyar nan ta koma lokaci guda.
Aisha ki rufa mi bakinki indai a kan zancen yarinyar nan ne zee ne kada in saba maki a gurin nan yanzu ki barni naji da abinda ya dameni please.
Jin hakan tayi shiru ta barwa ranta abinda ta hango a tare danni wai zeey din mamice wanan ta koma haka kuwa kodai mai kama da itace takoma haka haka wai ?
Har mami takai gida hankalinta a tashe sai innuwana take hanngowa a idanun ta tana kokarin kawar da zancen a ranta.
A gaskiga tasan yarinyar ba laifi a ko wani ba gare saidai zuciyar ta ya kasa natsuwa da hakan a kanta

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.