Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 23 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1ï¸Â⃣7ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH KA GAFARATA MUNA ZUNUBBAN KABA MU IKON AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU DUNIYA DA LAHIRA AMIN.
DO MIN SAMUN LITTAFIN NAN CIKKAKE ZAKI IYA TURA DARI UKU TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL NAGODE UBANGIJI YA HORE YA BADA IKON BIYA ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , ,
Idona a kan abin ina dan juyawa a cikin kofi naji wanan tsawan daya daka min sai da hanjin cikina ya kada don tsoro lokaci guda.
Allah ya gyara ban sale cup din ba ya shigo ya karbi abinsa yana mai bina da wani kallo mai kamar na tsana.
Wayace ki taba min wanan ya fada rai bace kamar da gangan na taba mashi abin bashi ya turoni dakin in gyara ba.
Dan marairaicewa nayi ya karbi abin shi zuwa daki sai gashi ya fito da cup din ban san inda ya juye abin ba.
Fita yayi daga dakin ba tare da yayi min magana ba hakan ya bani daman yin aikin a tsanake.
A gurguje na gyara komai duk da hakan dakin ya gyaru da kyau na kulle masa na fito na kai key din dakin mami.
Nikan don doki har na shirya kayana tafiya kawai nake jira washe gari na zata tun safe zamu wuce sai naga sabanin hakan.
Saida yamma bayan la,asar muka bargidan zuwa filin jirgin ashe da jirgi zamuyi tafiyan kuma.
Karfe shidda na yamma duk muna gida a lokacin har na bude dakin mami ina gyara don tun tafiyan ta dakin a rufe yake.
Sai yau da muka dawone ta miko min key na bude duk da a gyare muka barshi da zamu tafi hakan bai hana yadan yi kuraba.
Na gyara har bathroom na fito zuwa dakina shima na gyaro na shiga wanka dongon riga silk mai adon kamfala ne na dauko daga cikin kayab da anty Aisha ta bani na saka.
Saida nayi sallah har isha,i na fito falon don yunwa da nake ji lokacin in samu abinda zanci a cikina.
Suma mutanen gidan gaba daya a falo na same su saman dining suna cin abinci mami da yaranta maza su hudu sai yan matan mami din gaba dayan su har anty Aisha.
Simi simi na fito na zo diban abincin wasun su suka kuro min ido hannuna rawa na dibi abincin ina jin mami tana waya tana fadin muna kaduna yanzun haka.
Insha Allahu da safe zamu shigo Igabin naji tana fadi haka yasa na san zasuyi tafiya washe gari saidai ban san ko dani bane.
Diban abincin na juya zan wuce naji muryan yaya Jafar na fadin ke saida hanjin cikina ya kada don jin muryan shi saidai ban tabbatar ba ko dani yake don kaina na duke na basu baya.
Na kara takawa gabana na mumunan faduwa da ban san dalilin haka ba duk lokacin danaji muryan yaya jafar din duk da ina tsron kowa a gidan saidai nashi yafi yawa a zuciyana.
Ko dan ganin kowa ma yana shakarshi ne a gidan don tsare gida irin nasa .
Haka naci gaba da takawa cikin karfin halin zan tafi dakina inda na saba zama inci abinci hankali kwance zuciyana cike da addua nake tafiya.
Ya sake fadin come and join us ina zaki da abinci ga kowa nan a zaune hakan yasa nasan lalai dani yake magana na juyo a hankali.
Yana rike da cibin abinci da yake ci a hannun shi ya rike baikai a baki ba gabana na faduwa yace.
Daga yau a nan zaki rika cin abinci tare da kowa kinji abindana fada maki yana nuna min kujera da hannun shi .
Kai na gyada mai, tare da nufar gurin kujeran dake saiti da inda yake zaune babu kowa saman kujeran na zauna.
Idanuwan yan matan gidan duk a kaina bama su kadai ba har mami dake waya a lokacin idonta yana kaina.
Ko ban daga kaiba nasan akwai idon dake kallona a lokacin don jikina ya bani hakan ba ido daya ba ba biyu ba kodana dago kai duk idanuwan su na a kaina suna kai cibin abinci a bakin su.
Tundana zauna ya maida hankali gun abincin dake gaban shi hankali kwance yake kai cibi a bakin shi a hankali .
Daga mami har ya matan dama su jamal suka dago ido a sukwane suna kallon shi shiko ko a jikin shi.
Sai juya cibin dake hannuna nakeyi na kasa sakin jiki inci abincin yadda ya kamata a wurin.
Yadda kika san guba haka nake hadiyan abincin ba wai don baya da dadi ba don hadine na musanman akayi don zuwan su yau din su mama kande suka girka abincin mai rai da lafiya.
Mikewa yayi tsam mami tace har ka gama cin abincin ke nan ko rabin plate fa baka ci ba ba tare daya juyo ba yace mami iam ok zanje na kwantane.
Allah tashe mu lafiya mami tace yace amin yana tafiya sai jalal yace but yaya security dinka za a fada masu sutafi ke nan tunda ka shige ko ?
Na sallamesu tunda muka fito massalaci dazun idan sun gama zasu tafi ya bashi amsa yana tafiya da dan sauri kamar mai uzuri.
Mami ma bata dade ba wurin ta mike tabar falon sai mazan da suma suka mike lokaci daya falin ya rage mu kaida a ciki.
Duk lokacin danayi yunkurin dago ido sai in samu ana aika min da wani irin mugun kallo da tsana dan dama salma da Aisha su ba kallon tsana bane saidai kallone mai kama dana mamaki lokacin.
Amma dai yarinyar nan kina da sa, a yau kece yaya hero ke ba umurnin zama a saman table kici abinci tare da kowa a gidan nan.
Ke ko ba dole ba tunda ta iya makirci kamar ta mutu ta mairaraice ita gata Allah ba dole ta bashi tausayi ba Nazira ta fada
To kodai kin zauna a cikin mu ba a dai taba canza maki suna daga zainab yar aikin mami zuwa diyar gidan nan kamar kowa Rufaida a fada .
A, a, za a yi kiranta ki da yar gida mana duba yarda yan kwanakin nan gaba daya tayi fresh da ita haka duk sai suka kalloni lokaci daya.
Nagaji da cin fuska na mike don barin wurin, dama abincin ya fita min rai lokaci daya na dauki plate din zuwa kitchen.
Ina ruwan ba saban ba yau har wanan ce zata bar abinci haka bataci don samun wuri.
Ban kara fitowa dakin ba don na gamawa mami komai itama nasan ta gaji ta kwanta tunda akwai tafiya garesu washegari.
Nasan da zancen tafiyan mami don naji tana waya kan tafiyan yasa na tashi da wuri na nufi dakin ta koda abinda zata sakani a lokacin.
Aikuwa iba shiga dakin na samu ta fito daga wanka saida nayi mamakin hakan don bata ko tsaya jira inzo in wanke bandakin ba ta shiga.
Gaisheta nayi na nufi bandakin har ta karasa shirinta na dawo na fara gyara don ko kadan ban kawo dani za a tafi tafiyan ba don banga alaman hakan ba.
Hankali kwance nake aikina ina shiryawa maki kaya kamar yadda ta umurceni inyi mata anty Aisha ta shigo dakin tana gaida mahaifiyar nasu.
Bayan dun gaisa mami ke fadin ina fatan kin shirya dai don banson bata lokaci ga tafiya kin sani dai.
Mami wani shiri zanyi kauyefa zamu tafi banga abinda zan shirya bani ko haka zan iya tafiya ai ta fada cikin zolaya.
Mami tace da ita ai kauye garine don akawai yan Adam a ciki na dauka dai daji zaki tafi ai ta kwashe da dariya don tasan ta tabo mami din .
Gaba dayan mu zamu tafine mami ta tambaya tana kallon mahaiyar nata lokacin da ni kuma nake masu dan murshi don jin amsan da mami din ta bata.
Naji mami tace eh dake da yan uwanki maza ba na fadawa kowa tunjiya don kada yau su kawo min wani zance na daban.
Hae su Nazima ta sake tambayan mahaifiyar nata sai mami din tace haba dai Aisha ai ba zan sake zuwa dasu ba tunda da biyu suke zuwa
Tun wancan zuwan da sukai min tsiya nasha alwashin ba zasu sake zuwa garin nan da yawuna ba.
Mami samu,naka ne fa ba wani gari ba can Aisha ki fice mun a ido tun raki bai kai ga baci ba a dakin nan.
Zainab jeki ki shirya kada ku bata min lokaci ta juyo inda nake tana fadi hakan yasa na gunde dariyan da nake masu jin an abamci sunana ga tafiyan nasu da za,ayi wanda ni banso hakan ba don sati biyu da komawan school ke nan mu.
Dole na mike ba yadda na iya na koma dakina na fara dan shiryawa yan kayana kala uku a dan karakin jakkar da Aisha taban da zamu tafi kaduna.
Karfe goma safe mun karya sai kaya ake ta fita dashi ana sakawa a mota yan matan sunso subita amma mami tace ba zata dasu ba tunda suna raina mata gari idan sunje.
Ga motocin da za ai tafiyan dasu sai wani sheki suke ga hasken ranan daya fara gama gari suna daukan ido a ranan.
Suna falo zaune na fito da kayan mami zuwa wurin mota kamar yarda ta umurceni indauko zuwa bakin mota jamal yana gurin zai nuna min inda za,a saka jakkar kayan nata.
Wanan wau da ita za,a tafi halan Nazifa ta fada sai Rufaida take fadin kema ai kin sani itace yar miko min kawo min dole a tafi da banza.
Maganan yai min zafi sosai saida ai aikina ne din hakan don sun fadi hakan bakomai bane gareni tunda kowa yasan abinda ya kawo ni gidan ai shine aikatau.
Mota guda muka shiga nida mami da Anty Aisha sai driver nice a gaba zaune tare da driver suna baya a zaune su.
Tun kan a baro gida banyi magana da kowa ba har mukai nisa ga tafiya naji Aisha tana fadin waiko mami lafiya yarki take ?
Kodai abinda su Rufaida suka fadane ya bata maki rai kikai shiru tun dazun ?
Mami tace ai kinsan ita din ba gwana bace wurin surutu barta da saurin aiki kan kamar inji mema suka fada matane daya bata mata rai haka ?
No ba wani abu bane serious maganan su necan suke fadin wai ita dni ai dole aje da ita don yimin miko min .
Kai wa yan nan yaran akwai tsegumi garesu bari Allah ya dawo damu lafiya sai na masu tsiya dai a kan yarinyar nan .
Don banga abinda ta tare masu a gidan nan ba da suke matsa mata haka ko da yaushe.
A raina nace kayya mami kullun haka dai kike fada kin kasa yin maganin su haryau su kuma basu barni ba da fitinan su.
Wai mami yaya Jafar din ya yarda zai tafi gidan kawar taki ya duba yarinyar Aisha ta fada don a kawar da zancen .
Don tsuki mami tayi tana dauko abu a cikin jakarta tana fadin ai kin san hali shi dai.
Danayi mai magana dariya kawai yayi min ya mayar dani karamar yarinya sai na masa da gaske zai maida hankali wurin abinda nake son shi dashi ai.
Mami da kin barshi ya zaba da kanshi nima ban goyi bayan wanan auren hadin ba kindai ga yadda na yaya mamud ya zama a karshe ai.
Ni dai ina gaban mota ina faman tunane a raina har muka kai garin samu,naka din sai bin garin nake da kallon irin ni,imomin da Allah yai masu a garin.
Wani gida motan mu ya tsaya duk da anyi gyaran gidan daga wajen shi amma mutum zai iya gane tshon ginane na mutanen da masu shi a lokacin akaiwa gyara.
Tundai in ka shiga daga cikin gidan zaka samu part part gidane babba da ya kumshi jama, a masu yawa sosai a cikin sa.
Sai tafiya muke ana faman yi muna sannu da zuwa har muka kai kofan wani part daya sha gyara sosai an masa irin ginan zamanin nan .
Wasu mata biyu ne suka fito daga part din suna faman yi muna sannu da zuwa dukkan su na shedasu don sunje abuja na san su a lokacin.
Da sallama muka shiga falin babba wanda yasha gyara da kujeru manya manya na zamani komai dai na bukata a kwashi a falon.
Sai hoton wata dattijuwa dana gani tayi gwagoron irin daukan da akaiwa photon sai kuma photon mami da mijin ta duk da bantaba gani wanan photo ba amma na san fuskan marigayin mijin nata don akwai photunan manya a falin mami har gidan su na Abuja a saka a falon gidan.
Mami bata zauna falon ba ta shiga daga cikin dakunan a ca nake jiyo muryan ta ni da Anty Aisha ne a falon zaune muka gaisa da sisters din mami din suna tambayan mu yaya hanya ?
Can murya mami ke fadin ina kuke ne ku shigo ga hjyn a daki zaune kuzo ku gaisa kafin wa yancan su shigo.
Mikewa mukayi zuwa dakin wata tshuwace a zaune saman gadon alfarama kamar ba dakin tsofi ba duk da tsohuwace matar hakan bai hanata kwaliya ba tana cikin atamfar supar a jikin ta.
Aisha kan muna shiga gadon da take zaune ta haye tana fadin wanan ce mara lafiyan da mami ta tayar muna da hankali ga mutum na gani garau haka ba alaman ciwo.
Tsohuwa mai barkwanci tana fadin ke kuma wanan shiga haka kamar matar limami chochi fa ?
Duke nayiwa shi dan Allah dai udan zaki tafine ki tafi kiba mutane wuri kina dagawa iyayyen mu hankali haka.
Daga inda nake zaune kafin taba Aisha amsa nace ina wuni mama sai ta mayar da hankalin ta a gurina tana fafin kedai yar albarka kunzo lafiya ?
Yaya hanya ya kuka barsu a can nace lafiya yaya jikin mama Allah sa kafara ne ?
Da alama taji dadin yadda muke gaisawa da ita din sai wasan baki take tana fadin amin yar albarka.
Niko ko yar taki da ake fadi kin samu ke nan yarinya haka mai hankali Allah yasa ku raka tare.
To mu da ba, awa addu,an a hana mu raka din kaji min tsohuwa daga ma kin samu anzo gaidake har da zaben yiwa mutane addu,a.
Muryan yaya mamud ke fadin ni ina matar take gani nazo kada ki tafi muna son ki a hakan ko dan kwanciyan hankalun uwayen mu.
Kaji ja,iri kice dasu kike tafe ashe yau ina da babban bako a garin nan mamuda yaushe ranon ka da garin nan tana kokarin mikewa tsaye da kyar.
Aisha ta mayar da ita ta zauna mami takai mata duka tana fadin Aisha yo ga tsiya karki balla muna tsohuwa garin shashancin ki.
Barta ai gani take kamar ta fini kwari a hankan yanzu sai in lankada maki dukan tsiya a wurin nan.
Duk aka sa dariya sai ga daya sister din mami ta shigo tana fadin hjy yau fa kinyi baki harda Jafar akazo gaida ke.
Mami tace har kwana kuwa zasuyi maki a nan sai ki shirya ke nan kedasu yau a gidan nan.
Tana tafin dadi da murna ta samu ta mike da kyar tana lale marhabi da manyan bakina yau kuce amarya nake sai na zaba ashe tana fita daga uwar dakin nata din zuwa wurin su ta taresu.
Zeey jeki dauko mi kayana ki shigo dashi dskin nan mami ta fada na mike saida tsohuwar ta gama fita na dan bi gefen ta na fito daga dakin.
Suna zaune dukkan su tana masu lale marhabin cikin jin dadi har na fito kayan da mukazo dashine aketa faman shigowa dashi gidan.
Jakkar mami dana Anty Aisha na dauko na shiga dashi daga cikin daki kafin i koma in dauko nawa sai kuma na rasa yadda zanyi da jakkar nawa.
Na dan tsaya daga kofa ni ban shiga ba sai da dayan sister din mami takece min dan Allah shiga da ruwan nan mikawa su anty in gama da wayan nan.
A lokacin na samu komawa dakin na samu mami ta kewaya ban daki Aisha kuma tana rashe rashe saman gadin tsohuwar tana waya.
Ruwan na aje masu kafin in dan samu sakon gado na aje dan jekar kayana a wurin na juyo ina fadin anty Aisha ga ruwan .
Da hannu tayi min alaman a, a na dai samu wuri na tsugunna duk da kishin ruwan da nakeji ban yarda nasha ba tun kan mami ta fito tasha.
Ta fito tana fadin an shigo da kayan nan duka zeey don miyan nan kada a zubar dashi don Allah fadawa Ramatu ta kawar dashi kada a zubar.
Don miyane mai yawa na zabbi dana kan saniya banda nama da mami ta saka a soya a zuba a babban ruba mai marfi kuma.
Na mike da sauri duk da ban san wacece Ramatun ba a cikkn su sai dai nayi sa, a suna falon dukkan su nake fadin mama Ramatu mami tace akwai miya a waje akawar dashi kada a zubar.
Ke wanan muryan wa zaisan kina magana a hanka yaya jalal ke fadi yana nunawa mama ramatun ni a lokacin.
Na sake maimaita abindana fada da farko tana fadin aikuwa gara da aka fada muna bari yanzu a kawar dashi gurin.
Umma ina key din dayan dakin yake akai kayan a ciki tana tambayan tsohuwar data mayar da hankalinta kan diyan mami da suka sakata tsakiya da hira.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.