Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 25 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

1️⃣9️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

YAN UWA FATAN ALHERI HAR KULLUN A GARE KU UBANGJI YA GAFARTAWA MAGABATAN MU DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA ALLAHUMA AMIN.

YAR UWA BA ZAN GAJI DA TUNATAR MAKU BIYA KAFIN KI KARANTA BA DON KAICEWA SHIGA HAKKI GA MASU IMANI ALLAH YASA MU DACE AMIN DARI UKU NE KACAL KI GUJI RAINA HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH.

Saida gabana ya fadi don jin muryan dodona da ya shigo gidan bani kadai na gane ina tsoron shi ba don har salma, Rufaida da Nazifa.
Idan ya shigo na kanga sun shiga taitayin su a gidan har jamal da jalal suna wanan rawan jikin da kama kai a gaban shi idan yana kusa .
Nima hakan da nagani ya darsa min tsoron shi a lokaci guda duk da ban taba ganin wanda yaiwa cin fuska a gabana ba.
Dagowa nayi a rikece ban ko debi abincin kwarai a platen din ba don in gudu in koma dakin mu.
Na dai samu gaida shi da kwana na jakafata na shige dakin zama nayi don cin arish da kwai dana debo a falon .
Nayi loma biyu ne naji mami na kwala min kira daga falon da sauri na mike na fito falon ina fadin mami gani.
Tana can tana magana da mama Ramatu kanwarta a lokacin kafin ta juyo tana fadin .
Yauwa zeey don Allah yi serving din yayan ku gashi nan ya shigo yanzu ni zan dan fitane yanzu zan dawo.
Tana fadin haka ta mike sai naji yana fadin amma da mota zaku don akwai dan nisa daga nan gidan.
Eh ai shine yasa nace Jalal ya sauke mu kada yaje nisa yana waje yana jiran fitowan mu ai.
Amma mami jalal ne zai jaku ga driver suna waje sai shine zai jaku ban faye yarda da tukin yaran nan ba gaskiya yake fada da turanci.
Sun saba jana a mota ko a kaduna don hakane ai na yarda da tukin motar nasu.
Allah tsare yace yana mayar da kanshi ga wayan dake hannun shi aikin shi ke nan ko magana yake hankalin shi a kan waya ko sytem din shi shiya a raina nasa mashi mayen computer.
Abincin na gama zubawa lokacin falon daga shi sai tsohuwar dake zaune itama kudi take kirgawa daga haban zanin ta nakai mai abincin gaban shi na aje.
Ruwa na koma na dauko na aje mai cikin dan muryana nake fadin yaya ga abincin nan do gudun kada inyi laifi kuma gare shi.
Jin abinda nace yasa shi dan juyawa saman lafiyayyen kujeran falon tsohuwar da zaka iya da kira dakin wata amaryace can don haduwa.
Wayan ya aje daga gefe kafin yakai kallon shi ga abincin ya dago kai yana kallon tsohuwar kuma.
Kai kai kai wanan tsohuwar ko fashi kika farane haka ina kika samo wanan kudin haka masu yawa ?
Yanzun kuma bakiki kariba don baki da tausayi sai kuma kin karbewa mami dan kudin ta maimakon ki kara mata.
Kafin tsohuwar ta dago kai tana fadin ja,iri da hausan ka kamar na mai koyo uwar taka mai tausayina ita take aiko min da kudin ai.
Yau kuwa zance ta daina don ba kashewa kike yi ba boyewa kike yi idan an baki ashe.
Ina wurin fridge ina daukan ruwa insha suke wanan barkwamcin da kakar tasu na dauko ruwan na juya zan wuce daki don da farko tsoron shigowan shi ya hanani daukan ruwan .
Naji yace ke wanan uban abincin da kika zuba ni dawa zanci shi haka ?
Tsayawa nayi wuri daya da goran ruwan a hannu na ya sake fadin sai kizo ki dauka ki cinye shi tas.
Cikin karfin hali nake fadin na debi abinci yanzu yana daki na aje zanci kai wanan yaron da fitina kake wallahi ina laifin yar nan tana iya kokarin ta da kai.
An fada maki kowa irin kine dake loda abinci a cikin sa yana kiba kamar za,a tafi gasan gwaji dashi halan ?
To ba zataci ba idan zakaci kaci da yawan fitina har yaushe zaka zauna kana matsawa yarinya mutane haka.
Yar nan ko karyawa bata samu tayi ba yanzun taga ba yan uwanka abin kalaci suka fita kai kuma kazo da naka tsurkun yanzu.
Idan kayi fushi sai kaje kayi aure kowa ma ya huta mitar ka na tsiya kaji min yaro da jarabar tsiya haka.
Hjy dama naga kin gaji dani ai ki huta min gori yau kaduna zan kwana idan Allah ya yarda idan ka tashi ka wuce jos zaifi ma sauki ai.
Ina tsaye wuri daya ni ban gusa ba ina sauraren da bai karewa da tsohuwar ko da yaushe sai dai idan basu hadu ba idan kuma bata ganshi ba ta kafa mita ke nan ina ya shiga.
Zo ki dauki abincin nan na fasa ci ya fada da dan karfi simi simi na tako zuwa gaban shi ina zuwa nakai kasa tare da fadin.
Don Allah yaya kayi hakkuri na fada ina kaiwa kasa kamar zanyi kuka a gaban shi bace min dagani a nan na firgita sosai tare da kai hannu ina daukan plate din abincin.
Na juya ya sake fadin zo nan na dawo baya da sauri zuwa gareshi hjy ko sai faman yi mai masifan hakan takeyi bai kullata ba.
Baki da wasu kayane sai wanin black dress din da kullun kike sakawa ba kyau gani ?
Kallon kayan na jikina nayi ina fadin anty Aishace ta bani sune sabbin kayana yanzu dasu kawai nazo garin nan.
Fadan da kakan nasu takeyine ya hana taji me yake fada min don babu yadda zata jishi a yadda yake maganan.
Tafi don Allah ya fada in deep voice na juya da sauri don in bar wurin kafin yakai ga makeni yadda naga ya hasala din nan.
Tunda na shige ban kara fitowa ba shi kuma bai fita daga falon ba don ina jin muryan shi jefi jefi da hjy tsohuwa a falon.
Har su mami suka kai ga dawowa gidan hakan yasani kwantawa na kirkiri ciwon karya don da Anty Aisha ta ganin kwance take tambayana nace kaina ke ciwo.
Data fitane mami ke tambayan ina inane tace tana daki wai kanta ke ciwo tace .
Yo ai dole kai yayi ciwo ko don fitinan wanan masifafen dan naki da kika barta dashi ta bashi kalaci ya aza mata fitina.
Aiko ya Jackson baida fada hjy kece dai baki fahince shi ba Aisha ta fada tana kallin dan uwan nata.
Murya mami tasa ta kirani daga falon kamar ince wayo don wani irin faduwan gabane ya zuyarci zuciyana lokaci guda .
Saboda tsoracewa gashi yai min fadan jallabiya baka dana saka a jikina wanda har yanzu shine dai din a jikin nawa.
Don gigicewa ban ko tsaya daukan dan kwalina ba kaina dake da kitso tsoro hudu da nayiwa kaina a daren da zamuzo sun kwanta suyi lub dasu ga bakin gashi na sai sheki yakeyi.
Na fito nazo na zube a gaban mami din dake maganata da mahaifiyar ta kan rashin sake jikina a cikin su.
Ban iya dago kai na kalli kowa a falon ba kaina yana sade a kasa ina jiran inji abinda zatace dani.
Shiko ko kallon inda nake baimayi ba tunda nazo gaban mami din gashi a kusa dashi mami take zaune a daya kujeran dake gefen shi.
Meke damun kine zeey mami ta fada tana duban yanayina kai na dan girgiza tare da fadi cikin karfin hali mami kaina ke ciwo dama tun kan muzo nan na kuma sha magani ya fada min don kada tace a kaini asibiti.
Haka baida wuya a gurin mami dan abu kadan gare su yanzu asibiti ne za a ce akai mutum.
Mami tace dawo nan ki zauna ki daina wanan yawan zama ke kadai da kikeyi a daki ko yaushe koshi yana ja maki ciwo.
Banda zabi sai yadda mami tace dani dole haka ja mataciyan kafata da yai sanyi na hau saman kujeran data nuna min din.
Yaya jafar da ke rubutu a cikin sytem shi cikin kwanciyan hankali sai lokacin dana kai zaune ya dago kanshi yana fadin .
Ke meke damun kine wani irin magani kika sha nayi tsuru tsuru da ido don ban san me zance ba sai da mami ta kara tambayana nace.
Mami dama wanda aka ban asibiti ne a abuja sauran daya rage na sha dazun.
Sai naji yaja uban tsuki ya mike yana gyara dan riganshi daya takure don zaman daya dade a zaune.
Zaka fitane kafin ya ba mami data tambayeshi amsa sai hjy tace yo ina zai fita tunda tsoron mutane yake ji a waje.
Wurin ta ya nufa direct yana fadin zo muje ki rakani kada kada a saceni garin naku.
Wai wace ke zaune a kauye ke fadin wani na tsoron mutane ke idan ba tsoron kikeyi ba meya hanaki komawa kaduna ki zauna da mami.
Ja,iri ba zan tafi ba a dakin mijina zan mutu inda ya barni ba dakin wani ba ya fice yana dariyan maganan ta.
Ya dan jima a waje ina nan zaune falin tare dasu mami daketa baki suna fita don zuwa gaida mami din sai faman basu alheri mami keyi.
Nasan dai da yawan masu zuwa gaida ita yan uwantane saura kuma abokan arzikine.
Yayi sallama ya shigo falon suka amsa mai inda nake ya nufo yana mika min magani nasa hannu biyu na karba a cikin ladabi.
Mami ke tambaya maganin meye wanan din yace stress don kila aikine yai mata yawa yana mika min ya juya ya fita daga dakin.
Haka ya ban dama tashi na hade maganin don dole duk da ban san maganin kome yake nufi ba aiko na fara jin jikina wasai.
Ina sallah azahar sai barci ban tashi ba kuma ba wanda ya tayar dani din don sun dauka dai da gaske banda lafiya ne din sai bayan sallah la,asar na falka na tashi nayi sallah.
Ina idar da sallah nayo falon part din tsit yake babu wani hayaniya acikin sa yasa na gane mami ta fitane a lokacin.
Ko ina na gyara tunda aikinane nagama na hada kayan abincin da nagani ta nan na gane su yaya mamud sun dawo sunci abinci sun fita.
Don da alama shi yasan garin sosai kilama yana da abokai a garin sabanin shi mai zaman gida ko yaushe.
Salati naji a bayana mama Ramatu na fadin yanzu yarnan harda baki da lafiya baki kwanta kin huta ba ?
Kina nan kina tikan aiki haka mama naji sauki na bata amsa ina dauraye kwanoni dana tara wanda na wanke.
Kinga idan baki da lafiya bar matsawa kanki haka ai kowa yasan ciwo ko a daga maki kafa dashi.
Ni dai na gama ban ce uffan ba sai dan murmyshin da nakeyi kawai dakin na koma na shiga wanka kafin magariba yayi.
Iya kacin ganina da yaya Jafar ke nan tunda ya ban magani saida darene nake jin su mami na magana wai ashe fitan da yayi tunda ya kawo min magani kaduna suka nufa.
Yana zuwa kaduna gida ya nufa don yana son yayi wanka abinka da goggagen dan boko mai ilimi ashe duk zaman garin ya ishe shi .
Dan daurewa yayi kawai don ya farautawa mahaifiyar shi da kakan shi raine.
Sai dai ya kasa kanne zama har kwana biyu ko ukun da mami tace zatayi da mahaifiyarta a tare dasu don suga yan uwa yan uwa su gansu.
Tun daga kofan shiga yake jiyo hayaniyar yan matan a gida yake mamakin me suka samu hakane suke wanan hayaniya haka ?
Rawa suke tika ga kida yana tashi kamar gidan club Nazira da Ruby suna wani irin rawa wanda bai dace ace sunyi ba.
Ba wanda yasan da shigowan shi har ya tsaya yana kare masu kallo a wurin kafin kamshin shi dakewa mutum sallama ya daki hancin su.
Duk suka juya suna kallon kofan salma na zaune tana shan milk a cup tana dan kurba a hankali itama daga inda take din zaune tayi arba dashi.
Rudewa ko wacen su tayi ya tako a hankali zuwa part din shi dake gidan don wanka yake son yi da sauran abubuwan daya bari a nan.
Da sauri Nazira taje kashe kidan baiko juyo ya kara kallon inda suke ba ya shige part din bayan ya bude tare da gwauro kofan da karfi.
Duk yadda yake jin shi a da sai yaji komai ya gushe mashi bacin ran yaran nan ya mamaye zuciyar shi.
Yes yasan da yana wasu abubuwa da suka kaucewa addini da tarbiyan shi amma tsani yaga diya mace tana kauce hanya.
Zama yayi sama gado dakin tare da tokare hannaye shi ya kama haban shi yana tunanen zancen su da mami da take fadin.
Ba zanso ka ketare gidan nan ba idan baka son yar hjy hindu sai ka zaba a cikin wa yan na yaran guda uku da ke gidan nan don nasan dukkan su babu wace ba zatayi makaba a cikin su.
Tunda kai na fahinci baka da time din tsayawa dating da wata mace a yanzu tsuki yaja yana mikewa tsaye.
Deep in thought yaya za ayi ya auri daya daga cikin yaran nan da idon su ya gama budewa haka wai.
Dadai yaso bin ra,yin mami don shi ba wata macen da ta tsaya mai arai yanzu don hakane zaibi zaben mami din gareshi.
Wani tsuki ya kara ja ya fara cire aninin gaban rigan dake jikin shi fara longsilve yana maijin tarin haushin su a ranshi.
Wanka ya fada ya dan dauki lokaci kafin ya fito ya samu waya shi nata ringing ya nufi inda ya aje wayan yana dagawa.
Yaya mamud ne a layin yai mai kira biyu bai daga ba gana ukune ya samu ya daga yake fadin ya jafar kana inane haka mami tana tambayan ka ta kira layin ka not reacheble.
Ina gida yanzu haka ya bashi amsa kai tsaye gida yanzu na fito mami da hjy suna tambayan inda ka shiga yanzun hakan ina kofar gidan.
Kaduna fa nake nufi ya bashi amsa kamar a hasale don har lokacin yana jin ranshi babu dadi ga abinda idon shi ya gane mashi din nasu Rufaida.
Kokarin tayar da sallah dake kanshi yayi kafin ya gama ya shirya cikin wani jallabiya ya nufi gado ya fada.
Saidai duk yadda yaso yayi barci hakan ya gagareshi don baison ya batawa mami rai ko kadan tunda yai mata alkawari ya zama dole ya cika mata burin ta..

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.