Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 62 of 139

🦅 ABU CIKIN DUHU
🦅

5️⃣2️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

BARKA DA JUMMA,A YAN UWA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , , , ,
KADA KI MANTA LITTAFIN NAN NA KUDI NE DARI UKU NE NA FITAR MAKI DA SHIGA HAKKIN WANI NA FADA MAKI GASKIYA YAR UWA DON KIRA ZAKI IYA KIRANA DA WANAN LAYIN 08036959257.

Don Allah yar uwa ki guji shiga hakkin wani kada ki raina nauyin hakki a gareki kiji tsoron Allah don akwai ranan tambaya.
Ganin mami ya tayar min da sabon miki a rains don haka na shige dakina kai tsaye na fara darza kuka kaman an aiko min da sakon mutuwa.
Tambayan kaina nake menayiwa mami dana cancanci wanan sakamakon haka a gareta ?
Kafin in koma neman mafita a raina na abinda zai fitar dani wanan sarkakkiyar duhun dana jefa kaina a cikin rashin sani.
Duk da nasan ba nina jafa kaina haka kai tsaye ba yadda ake zato banda zabi a kan hakan daya faru dani sai yadda akayi dani a yanzu.
Ina cikin wanan tunanen naji an banko kofan dakin an shigo da sallama ta murya na sheda anty fadilace ta shigo dakin ashe.
Tun a kofa take bina da kallo rai a bace don a zatonta kuka nake na wani abu a yanzun ma kuma.
Sai bina take da kallon mamaki na wanan sallon iskancin dana tsiro yi a gidan bayan dawowan shi kasan ga yadda muka aje zanyi a baya da ita yanzu nazo ina masu faman koke koke haka a gida.
Wanda hakan ke nuna alaman kasawa a gareni bayan duk abinda ta koyar dani a bayan shi wanda hakan ke nufin zaman mu a tare baiyi tasiri ba kenan a yadda nake nunawa yanzun.
Wuri ta samu takai zaune a gefena ba tare da tayi min magana ba na dan lokaci kafin na dago kai na dan kalleta cikin wani yanayi ina fadin a cikin muryan kuka.
Anty me nayiwa mami da take nuna min wanan irin kiyayyan haka a fili shin anty don danta ya zabeni a matsayin sarakuwa a gareta hakan laifine anty don kawai banda gatan daya dace in zama sarakuwar nata ko mai ?
Ajiyan zuciya naji ta sauke tare da fadin meye damuwan ki da matar da ba,a gida daya kuke zaune da itaba yanzu.
Na katseta da fadin amma ai a gidan danta nake zaune anty don haka mami nada daman da zata shigo gidan nan ko wani lokaci kamar yadda dazun tazo na ganta ina gaida ita ta kyaleni.
Tazo gidan nan yau ke nan ta tambayeni cikin mamaki tazo anty na bata amsa wasu hawayen suna zobo min a idanuna lokaci guda naci gaba da fadin .
Har kofan gida na bita ina gaida ita mami ta kyakeni shin anty ni a haka rayuwana zai kare a gidan nan bansan matsayina a gun mami din ba ?
Zata soki zainab na fada maki hakan yafi a kirga kedai kawai a yanzu kiyi kokarin Allah ya mayar dake wani abu a rayuwa.
Amma fa sai idan kin cire damuwa da wanan shirmen hakan zai faru dake don idan kin matsa kin tayar da hankalinki karshen sa ki zama wani abin ki fiye da hakan ga kowa.
Do haka nake fada maki a kullun ki daure ki zama wani abin kwantace a duniya kafin hakan ya faru in ma har bata kaunar ki da danta ai ba kece kika dauko kanki kika kawo gidan nan ba kawo ki akayi da sunan aure.
Don haka ta samu danta daya kawo ki din tayi fadan haka dashi bake ba ke meye laifin ki a cikin zancen nan bayan cutar da rayuwan ki da akeyi yanzu.
Ta yaya mijin ka zaiyi tsawon tafiya irin wanan ya dawo a cikkn kasa ba tare da nuna maka wani kulawa ko damuwan shi a kan ka ba.
Don hakane nake kokarin nuna maki hanyoyin da zamu bi har mu samu a samu kanshi gareki idan ma wani abin ne akai maku a tsakanin ku har hakan ke faruwa.
Har wani lokaci muna dakin tana bani shawara akan mami dama shi ya jafar din akan inta kokarin in kawar da wani kunya ko nauyinsa a raina indinga cusa kaina gareshi ko yana nuna min baya son hakan da nake mai.
Jinta kawai nakeyi a raina sai fadi nake ta yaya zan kai kaina inda za,a wullakantani a daukeni ba kowa ba.
Zandai zauna a matsayin tallafawa rayuwan iyayyena da yan uwana a gidan sa don ni kaina nasan da bankai matsayin mata ko masoyiya a gareshi ba.
Bayan nayi sallah la,asar ne na fito zuwa dakin maizube inda na sameta zaune tana shan ferfesun a cikin wani plate mai zurfi a gaban ta sai tururi da yake tashi da kamshi a cikin plate din.
Ta dago tana fadin yanzu nake fadi in gama in kara lekaki zuwana biyu dakin yana rufe na dauka ai kina wurin mijin kine tun dazu ?
Dan murmushin yake nayi iya fuskana a raina ina fadin wani miji da baima san da zamana a gidan nan ba .
Zama nayi saman gado ina gaida ita tare da fadin tun safe ina daki kwance ban dai fito bane tunda yanzu gidan akwai maza masu shigowa ko wani lokaci.
Tace nima abinda ya zaunar dani dakin nan ke nan kada su takura da zaman mu haka shiyasa ma na fadawa malam zan dawo zuwa jibi tunda dai Allah ya dawo da mijin naki lafiya kuma.
Da sauri na dago kai ina kallonta tare da fadi cikin mamaki ki koma gida kuma maizube shifa ba mai zama bane kasan nan wata kila wani abin ma ya kawoshi yanzu haka dayazo din.
Don dazun ma naga mahaifiyarshi tazo gidan nan da safe sai naji tace a cikin mamaki ta shigo gidan nan bamu sani ba yar nan ai a gaisa dai ko ?
Maizube koni fitowa nayi na gansu a falo tare dashi haka kuma naga ta mike a cikin bacin rai ta bar gidan nan ko gausuwa dana bita waje nayi mata ban samu amsawan arziki a wurinta ba ta wuce.
Kai wasu dai sun dauki duniyan nan da zafi a ransu har yaushe wanan matar zata sauko daga fushi da kaddaran Allah da takeyi ne daku ?
Kada ki yarda ki biye ma duk wani hali datake nuna maki na kyama a gareki dan ba ita kike aure ba biyewa halinta kuma mijin ki ba zaiji dadin hakan ba don mahaifiyarsa ce ita.
Kinga kuwa ba zai taba lamuntan hakan ba koda itace bata da gaskiya kuwa ranshi zai bacine ga abin da zaki mata ke don haka ki daure ki hade tunda ba ko yaushe ne kuke haduwa da ita ba sai irin haka idan tazo ko kinje inda take din.
Shima kasa ki daure da halinsa ki zauna kiyi hakkuri mai hakkuri yana tare da riba wata rana duk wanan abin zai zamo tarihin rayuwa a wurin kine a kuma hada da addua ga komai da sadaka don kariya ga ko wani irin bala,in rayuwa.
Insha Allahu zan yi maizube na gode da shawaran da kuke bani a kullun keda anty fadila a gidan nan ba zan taba matawa daku ba a rayuwana na fada idanuna yana kawo hawaye a lokaci guda.
Nikan yaya kowa keson nayi ta cusa kaina ga ya jafar ne mutumin da har yau ko murmushin arziki ban samu a gurin shi ba balle wani maganan arziki irin na mata da miji ya shiga tsakani na dashi.
Ta yaya ake son in biye masa har muyi zaman auren da mutane suke hasaso min rayuwan jin dadi nan gaba dashi.
Don in kawar da zancen nace amma dai ba yanzu kike nufin komawan ki gida ba matar malam ?
Me zan zauna inyi a nan kuma tunda Allah ya dawo da mijin ki lafiya wurin ki kuma ai sai a raina muna hankali kuma idan na zauna haka.
Haba dai wa zai damu da zaman ki a nan don Allah kada kice zaki tafi ki barni a gidan nan ni kadai ba zan iya zama dasu ba wallahi.
Zaki iya mana ta ban amsa ko wace mace da kike gani haka ta koyi zama a gidan mijin ta harta saba da hakan kema a sannu zaki saba da zama ke dayan ai.
Maizube ban dauka wanan zaman da nakeyi a gidan nan ba na aure ne ba subbahanallahi naji ta fada da sauri har naji tsoro na dago kaina.
Idan ba zaman aure kikeyi ba zaman me kikeyi a nan kada ki yarda ki bata auren ki don wani dalili can da kike hange .
Kowa da yadda kaddaransa ke zo masa a rayuwa wanan shine naki kaddaran rayuwan kke zuwa mai Allah yayi akwai aure a tsakanin ku wanda muke fatan harda zuria idab Allah ya yarda nan gaba a tsakanin ku .
Jinta kawai nakeyi duk da nake yarinyace ni amma nasan hakan ba mai yuyuwa bane a tsakanin mu don ruwa ba sa,an kwando bane.
Tambayana tayi da naci abinci kuwa itama dai nasan kokarin kawar da damuwa a zuciyana takeyi lokacin.
Idan nabar nan zanje na duba abinda zanci na bata amsa da hakan na dan dade zaune ina tunane kafin in mike zuwa falo na bar dakin nata.
Ina ficewa falon na nufa dining erea dan samun abinda zan saka a cikina don naji cikina ya fara kugi a lokacin.
Kai tsaye wurin dining din na nufa kayan abincin dake wurin na fsra budewa a hankali gaba daya hankali na gurin abinda nake dubawa din duk sai naji ba zan iya cinsu ba a yadda nakeji lokacin.
Haka yasa sam bansan yana falon ba a lokacin yana zaune shi kadai a cikin falon ya tasa takardu da laptop din shi a gaba yana aiki a cikin su.
Zaune yake yabar abinda yakeyi ya zuba min ido daga inda nake tsaye ina bude kayan abincin danaga basu min ba nakai zaune daga inda nake tsaye din a cikin damuwa na kai zaune ina dafe kaina da alaman damuwa a tare dani sosai a lokacin a fuskana dana kai zaune din.
Kaman ace in dago kai daga inda nake zaune din don jin nauyin da jikina yayi kamar akwai mutum da yake kallona a lokacin yasani dago kai zuwa inda kujerun falon suke ina dagowa na dora idona akansa zaune.
Shine a zaune saman daya daga cikin kujerun dake falon zaune ya zubo min manyattatun idanuwan shi a kaina sai kace wani tsohon maye.
Wani kallo dana kasa fasarashi a lokacin naga yayi min mai nuni da ma,anoni da dama a gareni lokaci guda nayi saurin kawar da kaina gareshi tare da kara daure fuskana sosai na tamkesu.
Saboda kawai na kona masa rai don na dade da sanin halinsa yanzu a dan zaman danayi dasu a can gidan mami din don ba abu bane mai wuya ya disgani a wurin.
Karshema sai na mike don barin falon a lokacin don ba zan iya zama a cikinsa ba yana zaune a gurin yana zuba min idanu duk da naga tulin takardu a gaban sa.
Ina zaki naji ya fada a daidai lokacin dana mike ina shirin tafiya din jin hakan yasa na dan juyo dan kallon inda yake zaune din.
Ni ya zubawa ido yake kallo wanan karon ma dai babu daure fuskan nan nasa a idon shi don haka ban tsaya bashi amsa ba nayi kokarin barin wurin kai tsaye.
Muryan shi na koma ji yana fadin wai ba dake nake magana bane kina da alaman taurin kai a tare dake zainab .
Har sau nawa kike son in maki magana akan mami da yanzu kike wanan damuwan akan ta mami ni ta haifa ba ke ba don haka ki barni da mahaifiyata wanan ba damuwa ki bane ke .
Kalaman daya fada din sun matukar ban mamaki a raina ko dai wanan mutumin ya mata da shi yai sanadin rabuwana da mahaifiyar shine haka?
Don Allah ya jafar ka barni da abinda kaja min a rayuwana kayi sanadiyar hadani da mahaifiyar ka data nuna min kauna ta hanyan mai dani wani abu a rayuwana.
Ban zauna a gidan nan don wani dalilin ka ba sai don haka iyayyena suka zabar min a rayuwana yau gashi har wani daga cikin yaran ka yana ganin kamar auren Allah da Annabi kayi dani har yake kokarin yi min iyaka da kai a gidan nan.
Don Allah ya jafar na rokeka kamar yadda wanan mutumin ya fada min jiya a kanka na nisanci kaina daga duk wani lamari ka .
Nima a yanzu ina rokon ka ka samin ido kawai a gidan nan inyi zaman salama da rugumar kaddaran rayuwana a yadda yazo min dakai.
Ni kaina nasan gaskiya mami da wasu ke fada nidin ban dace dakai a sa,an aure ba idan makana da wani mafunune a kaina kan hakan da kayi yaya ina rokon ka ka tausayawa iyayyena kada kaja a illanta min rayuwana a gidan nan tunda har an fara yi min gargadi a kanka.
Wani kukane yazo min lokaci guda na kasa karasa abinda zan fada a lokscin don kukan dayazo min a lokaci guda din.
Yayin da shiko tun dana fara magana ya zuba min ido tare da tattara hankalin shi zuwa gareni yana kallona ba tare dayayi maganan komai ba har lokacin dana ja gwiwana da yai min sanyi a cikin karfin hali don barin falon.
Kasake yayi wani irin kunci da makina suna suna sauka mashi a zuciyar shi tunane barkatai yayi a wurin don ba mamakin karfin halin tunkaransa in fada mai wanan maganan gaba da gaba hakane ba ya daneshi.
Sai jin abinda na fada akan wanin danace yana kokarin yi man iyaka dashi a gidan nan ne tunanen shi a yanzu don yasan ba kowa ne zai mun barazan hakan ba sai Tujudeen kawai.
Ranshi yaji ya baci lokaci guda don me tajudden din zai masa wanan katsalandan a rayuwan shi ya tsorata yarinyar nan har ta tsorata dashi haka ?
Mikewa yayi da zuman bin bayana sai kuma ya koma ya dakata don zuciyar shi data gargadeshi dayin hakan a lokacin.
Da karfin gaske yake jin zuciyar shi na buga masa ya fada kan kujeran ya koma ya zauna yana lumshe idanuwan shi tare da jin magana kamar a yanzu nake fada mai su.
Mai Tajuddeen ya dauki kansa ne a yanzu da har zai mai wanan katsalandan din a rayuwan shi ba yau ba ya sani yana kishin wanan yarinyar duk da yasan dalilin shi na auren ta din.
Gashi har ya kai yaja masa raini a wurin ta ta yadda har ta iya kallon tsaban idanun sa ta fada mai magana haka iya son ranta ba tare da taji nauyin sa ba kamar yadda take ji a baya can.
A daidai kofan fitowa daga dakin sa muka hade da taju din wani kallo ya bini dashi na tsana ban tsaya bi ta kansa ba na wuce zuwa cikin part din mu kai tsaye.
A hankali ya tako zuwa tsakiyan falon har yakai bakin kujera bai iya dago kanshi ya kalli mai zuwa ba a lokacin kafin yai wani yunkuri ya tsunkayi muryan anty fadila tana fadi a bayan su.
Sir ko kuna bukatan wani abin motsa bakine a yanzu a kawo maku tana kokarin karasawa inda suke zaune take magana.
Sai lokacin ya cire hannun shi daya dafe goshi shi dashi ya dago jajjayeb idanuwan shi ya sauke a kanta tare da kada mata kai cikin karfin hali alaman a,a.
Ganin hakan koda baiyi magana ba ta gane mai yake nufi da hakan yasa ta juya da sauri ta bar wurin donta fahinci ogan nasu yaba cikin bacin rai a lokacin.
Zama taju din yayi a kusa dashi tare da tsura mai ido don ganin yanayin daya ke zaune a ciki.
Don baya son yana ganin sa a wanan yanayin yafi son ganin sa a cikjn yanayin nishadi da kuzari a tare dashi ko yaushe.
Don haka bayi kasa a gwiwa ba ya soma fadin wai lafiya na ganka haka ka zauna jiki a mace ?
Bai bashi amsa ba sai mayar da kanshi da yayi saman kujera ya daga kai sama tankar yana tunanen wani abu mai muhinmanci a lokacin.
Taju din ya kai hannun shi saman kafadan shi yana fadin wai meke faruwane da kai my man ka fada min matsalan ka ko wanan yarinyar ne take son bata min ranka ?
Cikin yan dakiku taju din yake jerawa jafar din wanan tambayan cikin bacin rai tare da kulawa a gareshi.
Yayin da jafar din ya sauke wani yar gajeruwan ajiyan zuciya ya dago kai tare da sauke jajjayen idanuwan shi ga taju din .
Kai taju din ya gyada mai tare da fadin nasan itace damuwan ka a yanzu don tun da muka shigo gidan nan naga yadda ta koma lokaci guda nasan za a samu matsala dakai don canzawan yarinyar nima ya ban mamaki matuka.
Bai bashi amsa ba sai dan shiru da yayi ya kurawa carpet ido kamar yana nazarin abinda zai fito bakin shi lokacin.
Kafin yace dashi ba itace damuwana a yanzu ba kaine taju don me kuma waya baka izinin shiga harkan gidana haka kai tsaye har kayi kokarin wuce iyakarka dani.
Taju din ya dago kanshi a razane yana kallon shi tare da shan jinin jiki don jin abinda ya fada din.
Kasan al,adan kasan mu kasan komai don me zaka wuce iyakar ka dani ka shiga harkan matana waya baka wanan daman yaushe har ka samu wannan matsayin haka ?
Kai ya dago da sauri yana dan kallon sa kafin jafar din ya nuna shi da yatsa yana fadin daga yau ban son ka kara shigowa gidan nan matukar bani na nemaka da kashigo ba.
Duk da ran taju din ya baci amma a fili sai ya daure yana fadin yanzu don wanan shine har ka wani tashin hankalinka haka ?
Sai kace wanan wani babban matsalane ni kawai nayi warni dinta ne don ta kiyayye shiga dakin ka kai tsaye bada wani manufa na fada mata hakan ba ai.
Murmushi jafar din yayi cikin bacin rai kafin yace dashi kasan nasan ka nasan halinka duk abinda zakayi ina warnin din ka akan yarinyar nan a tare dani.
Taju din ya marairaice murya kamar zaiyi kuka cikin ban hakkuri da nuna yayi laifi a gareshi nayin hakan iam sorry hakan ba zai kara faruwa ba tsakanin mu.
Shiru sukayi a falon yayin da kowa da abinda yake tunane a ransa kafin taju din ya sake fadin cikin yanayin kyarmar murya kayi hakuri please.
Sai lokacin ya dago kai ranshi a bace yana fadin kasan da kayi babban kuskure na bata min shirina akan wanan yarinyar don bazan so na rasa wanan yarinyar ba a rayuwana don ina matukar jin tausayin ta a rayuwana zaman ta yana da ma,ana mai yawa a gidana.
Taju din ya kara fadin nayi kudkuren yin hakan zuciyanane ya kasa hakkuri da ganin tana yawan shige maka da take kokarin a yanzu.
Wani kallo jafar din ya watsa mai da yasa ya mike ba shiri yana fadin iam sorry hakan ba zai sake faruwa ba tsakanin mu.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.