Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 100 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWALITTAFIN NAN NA KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA NA FITAR DA HAKKI NA FADA MAKI YAR UWA ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMAN SA AMIN.

Maza mutanen mu da irin hikimarsu ta maza badan yaso ba sai dole don yanzu shima yana dana sanin kakabowa kanshi aure daya yarda yayi don kawai ya farautawa mamin shi rai.
A yanzu yana dana sanin yin haka dayan san duk mata daya suke a wurin hali da bai yarda yayi wanan auren ba yake rayawa a ranshi.
Yarinyar daya dauka bagidajiya zai iya yaudaran ta da kudi da wasu kyalkyal din duniya duk da yana zube matasu kamar ba gobe amma tana son zame mashi ciwon idon rayuwa.
Sam bai taba zaton hakan ba da sauri ya dauka koda zan fahinci hakan sai bayan shekaru sun ja san nan zata iya fahintar rayuwan da sukeyi dashi a gidan.
Sai gashi a cikin yan shekaru ta nuna mashi halin mata a wurin wayau da hikima har ta iya hadashi da mahaifiyan shi haka.
Hadi na zargi da kake har mami na zubar da hawaye da bata taba irin saba tana ikirarin cewa zata sa a kashe shi shima duk inda ya shiga a duniyan nan.
Tabbas mami zata iya tunda ta furta hakan har in yayi gigin aikata hakan kan zainab din da kanwaera.
Shi ta yaya ma zai aikata hakan wai da har mami ta yarda da hakan da sauri don zainab din ta fada mata kawai zatayi amfani da wanan zancen.
Yana gama wanan tunanen ya dago kanshi dake duke ya kurama zainab din ido na dan lokaci .
Yarinyar ta rame sosai tayi wani hasken dake daukan ido tausayi ta bashi sosai don tana a tsorace ne ko damuwa har lokacin.
Baisan irin kalaman da zai mata amfani dashi ba a bakin shi ta yadda zata fahince shi a yanzu ta kwantar da hankalinta.
Don karyama ko yaudara bai taso ba gareshi yanzu tunda da idon ta ta ganshi bawai zato ba ko jiji da takeyi da farko.
Yanzu kan idanun ta ya gane mata koshi waye don haka babu sauran wani zancen dadin baki a kan hakan daya rage a bakin shi saidai hikima.
Muryan shi naji yana fadin wai yaushene zaku samu hutun makaranta ya fada yana kallo na ?
Jin abinda ya fadane yasa na dago kai da sauri don a zatona yana tambaya ne don ya mayar damu gida lokacin.
One month coming zamu samu saidai ita sadiya zata rigani samun hutu na fada mai a sanyayye don jikina da baida karfi sosai.
Ina son in kun samu hutu zamu tafi Dubai mu dan huta a can sai kunyi hutun naku can ga baki daya don nima zan dauki hutu a lokacin.
Fuska na bata ina kawar da kai daga kallon shi don jin abinda ya fada tunda ba gida zai kaimu ba a lokacin .
Ashe ya fahinci hakan danayi naji ya sake fada a daidai lokacin sadiya na fitowa daga daki yace ko Dubai din bai maki ba na kaiku America ko wani kasa kuyi hutun a can ?
Ni ba inda zan tafi na fadi hakan ina murgada baki kafin yace wani abu sadiya ta cabe da fadin yaya mune zamu tafi Dubai din ?
Eh sadiya a can nake son kuyi hutun ku wanan karon don ku dan ga garin tunda baku taba zuwa ba ko ?
Yayan mu shine bamu zuwa Dubai din don Allah karkice ba zamu can din ba ina son zuwa naga Dubai din nan da friends dina ke bada labarin sa.
Iyayyen su masu kudine idan kinji suna zance ke ko yar waye da zaki matsawa rayuwan ki zuwa can ?
Amma ai kanwan jafar ce ita din ko, ko anfada maki kani baya tunkaho da dukiyan wanshi ne ?
Wani kallo nayiwa sadiya din kafin nace tabi dai duniya a sannu irin haka ke kai mutum ga halaka karshe har mutum ya bar addinin sa ya fada sabon Allah.
Murmushi yayi tare da dan shafan gefen fuskan shi ya mike tare da fadin while sadiya saiki fara shiri ko ?
Don mukan Dubai zamu tafi mu huta ko ta daga kai tana satan kallona nidai nawa ido kawai na zuba masu ban iya furta komai ba garesu.
Haka muke samun kulawa daga gareshi a wanan lokacin don gaba daya yanzu ya sakawa duk wani motsi namu a gidan idanu idan yana gida.
Banda sakewa don kullun a cikin farga nake haka kuma yanzu nasakawa raina zaman dakin don falon da na riskesu a cikin sa suna fasadin su ya fita raina gaba daya.
Dana kalli daidai wurin dana gansu din a ranan sai naga kamar a lokacin ne suke aikata alfashan su .
Dakina ne ya koma min wurin zama muddin ina gidan saidai sadiya ta sameni a ciki muci abinci muyi hira ko kallo a nan.
Har wanan lokacin Maya bata tambayeni zancen magani ba nima ban tayar da zancen ba gareta don na manta da wanan zancen don abin yaya yayi nisa sosai.
Saima nake ganin ina wanan tsohuwar zata iya da taimakon kan haka al,amarin shi sai addu a kawai.
Ko banza sai nake ganin ai su din ba musulmai bane kuma ba Allah ma suka sani ba don haka ai abinsu ba zama dole a amsa masu ba a wurin Allah.
Kawai saina dinga addu,a da kyauta idan na biyo hanya naga marasa galihu saina tsaya na dan masu alheri.
Jerabawa ya sakamu a gaba hakan yasa ban ma da lokacin kowa a yanzu saina karatuna don ina son in fito da sakamako mai kyawo idan na gama.
Kwanan mu hudu da hutu muka daga zuwa Dubai inda mukaiwa dubai din saukan dare kafin mu kai hotel din da zamu sauka an fara kiraye kirayen sallah asuba.
Wani tsadden hotel ya sauke mu a kusa da ruwa muke duk da darene amma hakan bai hanamu gane kyau garin ba.
Dakin da aka saukemu shike kusa da nasa wurin dai sai kingani gwanin ban sha,a sallah nayi na haye gado sai barci ko abincin da yai odar akawo muna na karyawa ban tashi naci ba sai karfe daya na rana.
Sadiya bata dakin wanka na kara yi don naji dadin jikina bayan nafito na zauna ina gyara fuskana duk daba makeup nakayi ba a fuskana yau sai na samu kaina da shafa poweder kadan a fuskan nawa.
Gurin mayarwa ne naci karo da wanan maganin da kakan Maya ta bani don da wanan jakkar na tafi kauyen su maya din a ranan da naje can din.
Nayi mamaki kwarai dana ga wanan abin ashe ban cireshi a jakkar ba har nazo nan dashi uwar duniya.
Riga na mike na dauko na saka a jikina duk da bawasu kaya muka dauko ba don yaya ya hana hakan wanda zamu canza idan munyi wanka sai na jikin mu kadai muka dauko.
Kofan aka turo sadiyace a gaba yana binta a baya suna dauke da kaya niki niki a hannayen su haka yasani juyowa ina kallon su.
A saman gadon dakin suka zube kayan shi bai tsaya ba sannu kawai nayi mai ya juya ya fita bayan ya amsa min.
Baiko karasa fita daga dakin ba sadiya ke fada min yau yayan mu naga garin nan ashe haka wanan garin yake cike da musulmai ?
Ina kukaje na tsare ta da tambaya yayan mu ya shigo ya sameni zaune kina barci yace nazo muje unguwa.
Kada ki kara fita da kowa idan baki fada min ba na fada fuska daure Allah ya taimakeni tana matukar tsorona sosai don fada nakan mata idan tayi ba daidai ba.
Zama nayi na fara bude kayan suturu ne irin na mata yan duniya da suka amsa sunan su a ciki sai kuma na sadiya din leda daban ita sun kai kusan kala goma.
Ikon Allah na fada a fili a raina kuma rayawa nayi yanzu shi yaya bai gajiya da labto mana kaya haka ko a gida can chaina bazance ga yawan tufafina ba yanzu.
Sai kayan kwalama wanda ko ban tambaya ba na san saboda sadiyace ya sayo su haka kala kala.
Yunwa ne ya fara ziyarana sai lokacin na daga ido na hango abin karyawana saman table din cin abincin dake dakin mai kama da karamin palace.
Mikewa nayi zuwa kan table don na zauna tare da bude abincin irin cimarsu ne na larabawa aka shirya saman table din.
Dan kadan na tsakura na barshi don tafarnuwan da yai yawa a ciki duk da suma chaina suna cin tafarnu amma basu kai nan ci sosai ba.
Bayan karfe biyar shi ya shigo dakin da kansa yace muzo mu fita mu sha iska a waje munga kifaye suna wasa a ruwa wanda suka dauke min hankali sosai wurin kallo gwanin ban sha,awa;
Mun baza ido munyi kallo sosai ranan sai kusan magariba muka dawo cikin masaukin mu a gajiye.
Dadi kan muna shan shi zuwan mu dubai har yakai na kasa fahintar wanan daulan yadda yake kashe muna kudi don zuwa hutu kawai da mukayi a nan din.
Ban tashi sanin taju yana garin ba sai ranan da dare na fito daki kamar wace akacewa na fito wajen a cikin daren .
Na kama hanya zuwa waje don kawai iskan dake kadawa mai dadi a wajen dana shaka ta tagan dakin.
Kwatsam na gashi a gaba saida nayi wani irin kaduwa mai ban tsoro kafin na jawo karfin hali insa a rayuwana na dake na watsa mai harara kamar yadda shima yake min kallon rainin wayaun.
Shamlace man kaji kunya kato dakai kana bin karamin yaro kuna lalata dashi don taushewan kwakwalwa da batan basira.
In dai J ne insha Allahu sai ka zama abin kyama a gareshi nan gaba don ko kallon kare ba zai ma ba a duniyan nan indai akwai Allah na daga hannuna sama ina nuna saman alaman Allah na nan.
Na wuce shi ba tare da yai min magana ba naji mamakin hakan kwarai da yayi don sai murmushin mugunta ya sake kawai.
Ina tsaye rai a bace ina tunane wanan irun bala,in da yake tunkarana haka koda yaushe na jafar din.
Karama dani mai karancin shekaru a wanan halin haka ni yanzu ma na rasa abinda zanyi saidai kawai na barwa Allah lamarin sa.
Don abin ya wuce gaban mamaki sai la haula wala kuwati kawai za a ce ma lamarin nasa tunda har naga wanan katon kuma a nan.
Rasa abinda zanyi nayi a wurin na kunna wayana ina daukan hoton wurun don ya debe min kewa da bakin cikin dake cina a rai.
Don wanan karon nayi alkawarin bazan wa J din magana ba kan hakan saidai in bar abin a cikina kawai Allah yayi min maganin su da kanshi
Jimana naji an fada a bayana nayi saurin juyowa inga ko waye ke magana haka dani a wurin .
Taju ne tsaye ya saka hannayen shi a cikin aljihun wandon shi yace kada kiga kin fada min magana na kyaleki.
Yanzu dai nasan kin san ko wayw ni a gurin J din a tunane ki kina ganin har J din na iya rayuwa badani ba ?
Don haka yanzu ki ba kanki amsa a nan ya juya ya fara dan tafiya sai kuma ya juyo yace ku mata wawaye ne koda yake kwadayine ke damun ki keda iyayyen ki shiya kawo hakan.
Ya sake wani shu,umin murmushi a fuskan shi ya juya ya tafi ya barni tsaye a wurin ina binshi da kallo cike da kunan rai.
Har na dawo dakine ba tuna da wayana a kunne yake don ba kiran kowa nakeyi ba a nan tunda banda layin kasan a wayana.
Gado na fada sadiya na kwance tana kallon a system dina wanda aikinta ke nan sai sallah kawai ke tayar da ita lokacin.
Yaya kin fitane nace eh na sha iska ne a wajen bayan haka bamu kara magana ba don kwance nakai rigingine fuskana yana kallon saman dakin ina faman tunane.
Barci ya daukeni a hakan itama ashe tayi barci tabar sytem na aiki waya na kuma shima ya nuna a kunne yake don dan wutan da yake nunowa yana aki aiki.
Ya dawo ya shigo dakin don ganin wutan mu a kunne dayayi sai ya samu duk barci mukeyi a dakin dukan mu ga naurorin mu a kune a kusa damu.
Yayi niyar ya tayar damu daga barcin sai kuma ya barmu ya fara kashe system din dake wurun kan ta a yashe.
Bayan ya kashe system din ya mika hannu ya dauki wayana zai kashe ya ga video ne na dauka ya dan tsaya yana kallo.
Forwarding din shi yayi abin ya bashi mamaki don hotunan wajen hotel ne ya bayana yana magana sai dai baya jin me ake fada don ba kara.
Girgiza kai yayi yana murmushi ya dago ya kalleni ina kwance nayi barcina bansan inda nake ba ma a lokacin ya kashe wutan dakin ya fita.
Sai cikin dare na falka naga yadda muka kwanta tashi nayi da sauri na nufi kofan don in rufe sai na samu kofan a rufe ba key a wurin haka yasa na gane ta baya aka rufe mu.
Da tsoro na dawo cikin dakin ban kwanta ba abandaki na shiga nayi alwala nazo na tayar da sallah na dade a zaune ina addu,a da rokon Allah kan ya tsaremu ya karemu daga halaka.
Zancena da taju ne yake dawo min sabo saka sunan iyayyena da yayi yafi komai tsaya min a zuciyana.
A karshe wani dabara ya fado min a raina a hakan har aka kira sallan asuba na mike na gabatar sai lokacin na koma barci.
Da yake na sa abu a zuciyana sai banyi wani barcin sosai ba don kada yaya ya shigo ban sani ba.
Dakin ya shigo kuwa bayan mun gaisa dashine yanawa sadiya sherin wai ta fara zama yar lukuti tana dariya.
Yaya yau ina son shiga ruwan can don haka idan ka fita kada ka dade ka dawo mu shiga na fada kai tsaye ba tare da shakkan komai ba.
Bashi ba har sadiya tayi mamakin jin wanan maganan daya fito a bakina lokacin yace a cikin mamaki dama kin taba shiga ruwane ke nan ?
Ban taba ba yau dai nake son in fara na bashi amsa da hakan ya gyara tsayuwa yana fadin idan aiki ya barni zan dawo din Allah dawo dakai lafiya .
Yana fita na bishi da kallo tare da mamakin kaina nayin wanan karfin halin haka da nake son gwadawa a yanzu.
Tun lokacin na fara shiri na na fita har zuwa bakin shagunan dake layin hotel din na sayo wasu irin kaya masu matukar kyau ga tsada.
Kwalliya mai daukan hankali na tsarawa kaina don ban taba sanin na iya ba haka tun dan koyon da nayi zamanin zama da yan matan mami a gidan ta ina jin zancen su a wurin yin kwaliyan su zakaji suna gardama wanan yayi yawa wanan bai ji ba.
Kodana dauko rigan zan saka saida na runtse idanuwana kafin na bude na daure na saka kayan hakanan sai gani na koma kamar wace zata wurin fashion.
Ni kaina saida na gigiza dan ganina haka ba komai bane yasani hakan sai daukan irin shawarwarun fadila da yau nayi a zuciyana.
Don ina son in gwada in gwada sa,ata da hikimana na diya mace da fadila ke yawan fada min ko yaushe da takace.
Mu mata makamine gun da namiji komai taurin da namiji da cijewa ko gagara a duniya sai mace ta juya shi a wata tsigar nata wata rana.
Ta hanyar yaudarar ta ko kisa ko kuma kisisina da kutungwila irin na mata da maza basu taba gano hakan sai mace yar uwarta zata gane mai take shiryawa.
Wanan baiwa ne irin na mata da Allah ya halicci diya mace wanda su matan bayan addu,a wanan ne makami na biyu da suke amfani dashi a wajen mazanjen auren su ko hurda.
Ranan turare yasha kashi don duk wanda na gani har wanda ke cikin jakkana nayi amfani dashi a irin hakane na dauko wanda idan baki matan ba fadilace ta banshi da dadewa lokacin da zamu zo chaina tace ta karbo min nayi amfani dashi.
Uku da rabi na fara wanan shirin kafin karfe hudu don saida nayi sallah la,asar na zauna yin kwalliyan nawa na kammala komai daidai lokacin daya dace in kammala din.
A nasa bangaren kuwa yana tune da hakan yasa ya baro abin da yakeyi zuwa masaukin namu don shi ba mutum bane mai saba alkawari duk halin turawa shine akidar shi.
Don da hakan bai samuwa da bai mun alkawari ba tun farko dakin shi ya fara yadda zango yayi wanka ya shirya already yayi booking din wani haddaden jirgin hotel din da zamu shiga ruwan dashi.
Dakin ya turo wanda kamshi ne ta ko ina ya fara taron hancin shi ya fara raba ido a kan mu Allah ya taimake mu ina zaune saman gado ina zaman jiran tsamani ya shigo.
Duk da kusan wata biyun da suke shige idan ya kalleni gaban shi sai ya fadi ko yaji wani bakon yanayi a kaina yana ziyartan shi .
Wanda hakan yakan daukeshi don kawai yasaba da mune kwarai a yanzu yasa tausayine ko wani abu yakan ziyarci zuciyar a kaina don yasan badai feeling bane wanda maza kanji akan wata mace.
Shiya dauka hakan sabone kawai da tausayina da yake ji ayanzu ne don yasan bayai min daidai yasa yana jin wanan akaina idan ya kalleni wani lokacin.
Don saboda wani lokacin yakan zauna yana yin tunane mai zurfi kan matsalan namu tunda mami ta sakashi gaba yanzu don da kyat take daukan wayan shi koshi sai ya bi ta hanyar ya mamud yake samu su gaisa saboda Allah ya aza mai son mahaifiyarsu a ranshi.
Don hakane yakan zauna yana neman way out kan matsalan nasa da yake da wuya ya bari shima ya sani saboda yasha gwada barin ya kasa yin hakan.
Sai yanzune yasan ya fada tarko mai wuyan fita a cikin rayuwan shi wanda zaice kurciyane da zugin abokai sukai tasiri a ranshi a lokacin don kawai duniya ya fada halaka.
Gashi arziki da suna duk sun samu a duniya saidai shi gareshi a yanzu wanan duk banzane a wurin shi tunda har mahaifiyar shi da uwar cikin shi suna kyamarshi saboda halin shi.
Da wanan ya shigo dakin namu sai dai yau din muna hada ido dashi daga inda nake zaune nayi wani irin zama kamar wata Queen of manshion saman gadon.
Wanda nima dai haka kawai yanayin zaman yazo min bawai nayine da ganganba don kawai kada kayan jikina ya baci ne na zauna hakana.
Ras ras yaji a gaban shi wani abinda bai taba ji ko hangowa a gareni bane ya hango tare dani yau din daya shigo ya tsinkayeni hakan.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.