Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 131 of 139
ASSALAMU ALAIKUM FATAN ALHERI GAREKU DUKKA MASOYA ALLAH YA TAIMAKA YA BADA SA,A A RAYUWA AMIN
LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KIBBIYA DARI UKU KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA.
Idan na tsaya fadan irin wahalan da yasha a wanan lokacin zamu bata lokaci a labarin don amai da gudawa yayi shi yafi a kirga tun yana iya tashi yaje da kanshi har yakai baya iya tashi a lokacin.
Kuma ban daina mashi amfani da maganin wurin malam da kakan maya da suka bamu ai amfani dashi don matsalan.
Duk da nasan maganin suna da karfi suna daya daga cikin abinda ke karasashi zama weak a yanzu saidai hakan baisa na tsorata ba don malam dake kara min kwarin gwiwa da shi da maya a ko wani lokaci.
Har yan uwan shi ba,a bari sun san da zancen wanan rashin lafiyan nasa ba cewa ake ya yayi tafiya a lokacin.
Haka kuma ya mamud ya gargadi duk wani wanda ke gidan a lokacin idan azo nemasa yayi tafiya dazun da asuba duk da sunyi mamakin jin ogan nasu yayi tafiya ba tare da sanin su ba.
Don ya saba idan zaiyi tafiya ya tarasu ya dan raba masu dan kudin kashewa a hannun su sai sukaji ya tafi bai samu ganin su ba hakan sai bai masu dadi ba a zukatan su.
Sannu a hankali jikin ya fara dawo mashi daidai duk da hakan kuma ba a leka asibiti dashi ba nice sai yan uwan shi muke fama dashi haka a gida har Allah ya kawo mai sauki a hankali ya fara fitowa falo yana shan iska idan ya gaji ya koma daki kuma.
Yau da kanshi ya fito dan karamin falon shi ya zauna ya dan mike kafan shi a saman dan karamin stol dake wurin.
Ya dafe goshin shi da hannun shi daya tare da kurawa kasan dakin ido yana tunane.
Yayana yau da kanka kafito na fada abinda yasa shi dan dagowa ke nan daga yanayin da yake zaune din, ya dan dago kanshi ya dan kalleni tare da dan sake murmushi ta gefe fuskan shi.
Aje dan cup din da na shigo dashi a hannuna nayi daga gefen shi ya kalla ya wani bata rai kamar karamin yaro a lokacin.
Dan murmushi nayi na koma gefen shi na zauna ina kallon shi kafin ince sauki ya samu ke nan tunda har ka fara tsanar magani a yanzu.
Bana jin dadin sha sa a yanzu ya fada yana kawar da kanshi gefe daya nace hakkuri zakayi kasha daga gobe shike nan ya kare ai.
Zama ya gyara a irin yanayin dana riskeshi a ciki da farko sai dan shiru daya biyo falon tsakanin mu na dan lokaci.
Kafin muryan shi ya maye shirun da fadin zainab nasan kina kokari dani ba kowa bane zaiyi wanan abinda kike min duk da kinsan makasudin matsala kika zauna dani haka kuma kika yi jinyana a hakan .
Duk da irin halin da mami da yan uwana suke nuna maki a kaina hakan baisa kin gujeni da halina ba duk nasan abin yana damun ki a cikin zuciyar ki kuma.
Kiyi hakkuri ki yafe min duk wani abinda nayi maki tun haduwana dake zainab ina rokon ki da kiyafe min don Alla.
Da sauri nakai hannu saman bakin shi ina rufe bakin nasa da hannu ina fadi cikin murya mai nuna alaman kuka a lokacin .
Ka daina fadin haka yaya ko nayi aurena nayiwa kuma wa mijina nayi don ance aljannan mu mata yana karkashin kafan mazajen mu.
Kai din kuma koba aure a tsakanin mu kacancanci hakan a gareni ya don kaimun komai a rayuwana yaya ka ingata rayuwana ka taimakawa kanwa da yan uwana ashe nima din ba zan saka ma da irin alherin da kake min ba a kullun.
Taimako a tsakanin mu Allah ya hada zaman rayuwan mu a wuri daya hakan na nufin mun zama daya da kai a yanzu.
Idan kana cikin farin ciki ko akasin hakan nima hakan ya shafeni don nayi ma abu ba sai ka gode min ba kaina nayiwa hakan.
Wasu hawaye masu zafine suke zubo min na kasa magana naji ya jawoni zuwa jikim shi yana dan buga min baya kamar karamar yarinya a lokacin.
Zainab ki godewa Allah da ya sa kika zama silar shiryuwana a duniya dana mutu a cikin wanan halin da ko uwata ta kasa fitar dani a ciki sa ya zanyi me zan fadawa ubangijina a wanan halin.
Ke din zainab alherice ga duk wanda kika zauna dashi ke haske gun duk na tare dake zainab farin cikine ya dace dake a yanzu ba kuka duk da wani farin ciki sai a kuka bawa ke iya nuna hakan.
Don haka kiyi kokan ki a yanzu don kukane ya dace damu a yanzu don godiya gun ubangijin mu.
Ina son ki sani ni jafar nayi maki alkwari a yanzu duk wasu munanan halaiyan da nakeyi a baya na daina su har abada kuma inawa masu irin halina na baya da Allah ya fitar dasu a cikin sa kamar yadda yai min sanadi dana barshi nima a yanzu.
Yakai yanzu kunyan kaina nake ji da duk wani na tare dani dayasan hakan a kaina ina bakin ciki a yau dana wayi gari ina tuna nayi wanan halin dabbobin a baya zainab.
Sai kawai naji ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya a lokaci daya , rudewa nayi na rasa abinyi sai can na koma fadi in girgiza kai don Allah yaya ka daina wanan kukan bashine yanzu a gaban kaba.
Dacewa yayi ka koma ga Allah har idan kasan akwai wani sauran abin haramun a tare dakai har yanzu kayi gagawan fitar dashi a gare ka .
Ta hanyar yin sadaka ko ka tambayi malamai abinda ya dace kayi da wanan abin shine nake ganin abinda yanzu ya saura kayi .
Ma,ana a cikin dukiyan ka ko wani kaddara daka aje da kudin hharamun sai kayi gagawab fitar dashi a hannun ka don a yanzu ya haramta a hannun ka tunda ba ta hanyar halal aka sameshi ba.
Ajiyan zuciya naji ya sauke tare da lumshe idanuwan shi yana gyara zaman shi tare da mike kafafuwan shi duka biyu kafin yace.
Duk ba wanan bane damuwa na zainab don nasan dukiyana na zufanane na sameshi a kashin kaina ga baki daya.
Elimenatis din mu kawai na wayewa ne da harkan homo bawai don arziki bane ko wani abu kawai dai hakan wayewa ne a garemu duniya ta dauki mutum da tsoro ko wani abu can.
Ai akwai wa yanda basu da komai kuma suna ciki kungiyan tare da kowa kawai ni yanzu abinda ke damuna shine.
Sai ya dan ja numfashi yana girgiza kai kafin ya bude ido ya kalleni yana nunani yace damuwa na shine zaman mu dake zainab a yanzu.
Ban san a wani matsayi aurena dake yake gun malamai idan zasuyi bayani zainab ina tsoron kada su fada min ke din ai kin haramta a gareni yanzu .
Don tsawon dadewan da mukayi a tare ban sauke hakkina a kanki ba da kuma manufan da na aure ki akai a yanzu wani matsayi aurena dake yake ga Allah ?
Da sauri na daga na kalleshi kafin na mayar da kaina na dukar a sanyayye wani irin harbawa kitjina keyi lokaci guda don sam wanan tunanen banyi a lokacin ba.
Tunanen hakan sam bai taba zo min ba don ban dauki hakan a wani matsayi ba can na daban da zai iya kawo shamaki a tsakanin mu.
Tsam na mike daga yadda muke zaunen na dan gusa nisa dashi ina jin faduwan gaban nawa na tsanan ta.
A yanzu wani iri nake ji azuciyana da yayi wanan maganan dan jinyasa kawai ya kara saka shakuwa sosai a tsakanin mu wanan lokacin.
Shima din da alaman hakan ke damun shi cikin zuciyan shi a lokacin na sameshi yayi shiru dana shigo yana tunane.
Karshe mikewa nayi don ba zan iya jure zama a falon ba a lokacin bina yayi da kallo har na fice ya mayar da idanun shi yadda suke yana maijin tausayin mu a zuciyan shi .
Ina shiga daki na fada saman gado na sake wani irin kuka lokaci guda kukan da bazan ce ga dalilin yin shi ba a lokacin shin kukan bakin cikine koko na murna nakeyi a lokacin.
Abin mamaki nida na dawo Nigeria da zuman rabuwa dashi har abada a zuciya sai gashi yau abin mamaki ina sake hawaye akan ya furta zaman wata kila dashi a yanzu ya haramta.
Don wasu dalilai dabai cika ba na sharia tun yin aurena dashi dana zauna a tare dashi a matsayin nazo aure gare shi.
Ni kadai a dakin na kasa samun natsuwa a tare dani zuciyana ina jin ba dadi a yanzun tun bayan wanan maganan da mukayi dashi a part din shi din.
Haka na wuni sukuku dani da damuwa cike tare dani na rasa sukuni a wanan wunin ba abinda ke min dadi a zuciyana.
Bayan na sallame sallah isha,i ne na jawo wayana na tasa a gabana ina kallon lokaci a wayana ina dakon time din da nake tunanen malam ya shiga gidab shi a lokacin karfe tara ke nan na dare.
Saida na dan bada lokaci kafin na dauki kiran na danna maaa kira kamar kiran zai katse ya daga da sallama muka fara gaisawa dashi.
Yake tambayana jikin jafar din na fada mai yadda yanayin jikin nasa yake a lokacin yayi masa fatan samun sauki a tare dashi har abada.
Kafin nace da dashi malam tambaya nake dashi yace na,am ina sauraren ki zainab nan na jefo mashi tambayan sai naji yayi murmushi ya fata min bayani tiryan tiryan yadda zan fahinci yadda maganan yake a addinance.
Saida ya gama min bayanin nayi mai godiya mukai sallama na kashe wayan a hankali na kai kwance a wurin ina lumshe idanuna.
Dare yayi ban iya lekowa ko falo ba balle nace zan tafi na duba shi don yanayina ya koma kamar na mara lafiya yin yau.
Ina kwance a kasa a inda nayi sallah kuma nayi waya da malam ya wayar min da kai kan maganan kamahin turaten jikin shi ne ya ziyatci hanncina a lokacin.
Jin hakan duk dana gane shine ya shigo dakin a lokacin amma hakan baisa na daga ba daga yadda nake kwance a kasan dakin saman salayan.
Tun da ya shigo idon shi yake a kaina ya karaso yana dan kiran sunana da zainab ko barci kikeyi ne wai ?
Na dan daga tare da fadin idona biyo banyi barci ba ya kalleni ya dan sake murmushi a fuskan shi yaja jikin shi zuwa bakin mirrow ya tsaya tare da jingina da jikin mirrow din yana face dina.
Sake ambatar sunana yayi yana fadin zainab meke damuwan kine yau ko bakya jin dadin jikin ki ne yau din ?
Sai lokacin na dan dago na zauna a hankali ina kallon shi kafin na mayar da kaina na duka ina fadin lafiya ta kalau nake.
Kin manta da kina jinya ne baki lekani ba tun dazun ya sake tambayan yana hakan sai dan sake murmushin dole ina dan gyara hijabin dake jikina nace.
Ban manta saidai naga majinyacin nawane a yanzu ya samu sauki yasa na nisanta kaina dashi har zuwa lokacin da za a warware matsayin zamana da kai.
Shima dai dan murmushin yayi ya gyara tsayi yana fadin au kan wanan maganan yau yasa ban samu kula yadda aka saba min ba kullun ?
Ko kema bakya son rabuwan namu ne a yanzu kamar yadda nima nakeji idan hukuncin hakan ya hau kanmu ?
Na danyi murmushi tare da girgiza masa kai ina fadin a, a ko daya saidai kawai ina jiwa sabone da juna da mukayi da kai a yanzu.
Amma nasan ko mun tafi kai baka da wani kewa ko damuwa ai irin wanda mu zamuji na rabuwa dakai a yanzu.
Don dama a shirye ake da a aura maka wace ta dace dakai a rayuwan ka don farin cikin kowan ka koni a yanzu nasa ba sa,an ka nake ba.
Ya dan kalloni da mamaki a fuskan shi kafin yace wanan shine tunanen ki a kaina zainab ?
Har kina tunanen akwai wata macen data dace dani a yanzu kuma bayan ke ? ke dince zabin da Allah yayi min koda akadara hukuncin rabuwa a yanzu ya hau kaina sai dai in zauna hakana ba tare da aure ba a gareni.
Aiba kai zaka aurawa kan ka ba wanan karon aure za aima kamar kowani da dan gata a duniya irin naku na yayan attajirai a kasan nan don duniya tasan da auren ka.
Murmushi kawai yayi ya dago tare da fadin idan kin gama fadin abinda ke zuciyar ki yanzu saiki hado min magani nasha na kwanta.
Daga haka bai tsaya ba ya fice daga dakin na sauke ajiyan zuciya ina maijin daci a kasan zuciyana kamar ya fashe a lokacin.
Ban bita yadda nake ji a zuciyana ba na mike na hada mai maganin nakai masa na samu har ya kwanta saidai ba barci yakeyi ba a lokacin.
Ina tsaye har ya mike zaune yasha ya miko min cup din na juya na fita daga dakin bai kara ganina ba sai washe gari dana kai masa maganin yasha ba tare da yai min magana ba har na fita.
Yasan dai dalilin hakan a yanzu kan wanan maganance da yayi min da yanzu yake daya sanin furta hakan a garebi.
Don ya fahinci zan juya maganan ya zama wani manufa ta daban a gareshi saboda ya fahinci kawai wani aure nake zato a gareshi a yanzu.
Ya tambayi kanshi dama ina jin shi a zuciya har hakane ashe don gashi na fara nuna kishin shi da wata mace a duniya a fili.
Niko ina komawa dakin hjy na nufa na samu tana zaune tana dan kirga kudin ta tana jin na shigo dakin tayi maza zata boye kudin sai kuma ta fasa tana fadin .
Ai kece na zata ai wanine zai shigo dakin bake ba har abin yaso ban dariya na dan dara kadan ina fadin.
Hjy duk wanan kudin nakine haka tace ba kaji ba shiyasa bana son a gane su haka kada a saka min baki tana kokarin daure kudin cikin jikinta.
Sai kuma ta fasa tana fadin ko na dan baki wani abune ki rika dama dan kudin da bayin Allah dake zuwa gaida nine nake tarawa kinga dana koma sai in taimakawa kawun ku Amadu dana cefane kome kika gani yar nan.
Kinsan shi Amadu baidashi kuma ga tarin iyali Allah ya bashi kullun a cikin wahala yake na iyali shiyasa nake dan tausayin shi a cikin su.
Kaina girgiza jin takai aya ina fadin hjy bar kudin ki kaiwa kawu ya fini bukatan kudi a yanzu ni nan babu abindana nema na rasa a rayuwa.
Tace wanan nake maki fata yar nan ko yaushe gashi har kina fadi da bakinki a yanzu hakan shine shedan kwarai wurun mace ga mijinta.
Ni kaina naga alaman hakan a tare dake a yadda kika koma din nan kamar a tabaki jini ya fita din nan hakkuri ke nan idan ka yishi kana da riba sosai a wurin Alllah tun a nan duniya.
Ki kara rike mijin ki dakyau yar nan irin mazan ku yanzu tsadane dasu a duniya ba kowane ke samun su ba a rayuwa na dan murmusa na ciki na ciki ina fadi a zuciyana.
Kedai tsohuwa ayi sha,ani an cuci na kauye baki san komai ba don ABU CIKIN DUHU SIRINE namiji ko tallakane indai halinsa yana da kyau shine dace.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.