Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 52 of 139

Karfe hudun yamma mun gama duk wani shiri zuwa unguwan da innan tace muje mu gidan wani baffan ta dake can karshen layin su.
Sea tsawale nake tafiya don idon mutane dake yawo a kanmu a duk inda muka wuce dan gungun mutane a zaune.
Gidan irin ginan kauyen mune akwai zaure har biyu kafin ka kai kanka cikin gida gidane mai dauke da matan aure guda uku ko wace daga ciki an kewaye mata part din ta da dan kishefa guntun katanga da bazata iya ganin sasshen yar uwata ba sai idan ta shiga daga ciki.
Nasan gidan don yana daga cikin gidajen da muka bude ido dasu tunda mukai wayau muna kai masu abincin sallah da yawon sallah kamar yadda al,adan bahaushe yake a karkara.
Sashen uwargidan muka nufa tana ciki da taranta ta amsa muns muka shigo tun a waje muka fara gaida ita da yaran don zaman uwaye suke a gare mu tunda inna diyace a wurin su.
Matar da fara,a take fadin a, a lale marhabi ga amaryan birni a gidan nan yaushe garin inji maki bako ?
Kafin in bada amsa halima kanwata ta cabe da jiya suka zo gobe ko jibi zata koma idan anzo daukan ta.
Ke kan fafi ba, a tambayeki ba sa,adatu takai mata dan duka a aika suna kokarin rikicewa da fitina a tsakar gidan mutane lokaci guda.
Tsawa na daka masu tare da masu fadan haka da sukeyi matar baffan ina na fadin indai wa yan nan ne ai mun saba da halinsu ko yaushe suna gidan nan tare damu ai.
Zama nayi saman tabarban da dayan yarta ke kokarin shimfida muna lokacin da muke maganan muka kara tusa sabom gaisuwa tare da tambayana yaya can ya nabaro su.
Sai mukaji dauri aure kawai daga sama haka kokaiwa malam ashe kin gama karbe mai dan kudin sadakan shi kin tafi birni kinyi auren ki a can kin bar mallam a soro ko ?
Da murmushi nayi tace ai ba a mamaki sa ikon Allah don wanan auren naki Allah kadai yasan manufan hakan gareku ubangiji yasa alheri ne hakan ya kawar da duk wani sheri daga gare ku .
Wanda ke sakin suka amsa da amin ni dai a zuciyana na amsa ban iya amsawa a fili ba don kunya da kawaici irin na yayan hausawan asali.
Tsaraban da inna ta debo masu muka zo masu dashi nayiwa halima signal da ido ta mika mata tare da mata bayani kamar yadda inna tayi muna bayanin a gida.
Ta amsa da murna tare da fadin barin kaiwa malam ya gani kafin ya fita wurin daliban shi yasan kunzo don idan ya fita baku samu ganin shiba sai bayan magariba zai shego gidan kuma.
Ta mike tare da daukan su kayan shayi da sabulen da nazo masu dashi ta nufi turakan malam din dake zaune saman buzun rago mai launin fari da baki a shimfide a kasa.
Ga kwanon hura a gefen shi da kofin silver maidan girma na ruwa ya amsa sallaman umma hari matar shi lokaci guda.
Bai daina shan furan ba saida ta kare mai bayanin tsab ya dauki kofin ruwan dake gefen shi ya kora kadan kafin yace sun iso ashe tun dazun su nake dan dako ban fita ba dama.
Ki masu iso su karaso ya fada a cikin yanayin da malam bahaushe kanyi magana da matarshi a cikin gadara da isa .
Har takai kofa yake fadin ji mana da sauri ta dawo baya don jin mai zai fada kafin yace na yanke shawara kecev zaki bi wanan yarinyar kamar yadda uwarta tazo ta bukata ai mata gada don ba wani abinda yahanasu zata nema muddin ina da karfin sa in kasa yimata shi kamar yadda zanwa dan cikina abu babu jin kyashi ko wani abu haka itama yahanasu din .
Na sani malam inna habbi ta fada tana gyara tsayin ta don maganan yazo mata a bazata kuma bata da halin da zata musa hakan ga maigidan nasu.
Da sanyi jiki ta fita daga dakin kafinta kawo wurin mu babu wani alaman damuwa a tare da ita alokacin sai fara,a dake fuskanta tana fadin mu isa mu yake jira a sashen shi dama ashe.
Nan muka barta ta aika karamar su watau amaryan malam tazo ta raba abinda muka kawo masu din na tsaraba.
Yana zaune a yadda matar tasa ta barshi muka shigo muka gaisa ya dan jamu da ba,a kafin ya dago yana sallaman su sa,adatu da su dan fita daga waje ya gama magana dani.
Ba bata lokaci suka mike zuwa wajen mutanen gidan inda suke zaune kafin ya dago yace min amarya watau kin koma birni kin mana wayau ko ?
A cikin dan kunya nake fadin ba gani na biyo ku kauyen ba malam tunda nan na saba dashi ni yadan yi murmushi yana tono wani abu a cikin kayan shi kafin yace.
Dazun uwarku tazo min nan hankali a tashe tana fada min wani magana wanda nina dauke shi kamar zancen matane kawai.
Don a iya bincike na tun dazun din ni alherin hakan nagani ta ko ina dan akasin shi baida yawa sai dai abinda ba,a rasa ba kawai wani lokaci na zama tare.
Don haka yanzu dai karbi wanan ki fara sha ya miko min wani ruwan rubutu a wani tsohon goran yought daya dan dushe kalan farin shi.
Dole hakana na karba na kafa kai kamar yadda yace insha da bissimillah in raga in shafe kaina har zuwa wuya sa fuska da sauran ruwan.
Yayin da nake faman yi shi kuma yana kokarin yan tone tone acikin kayan shi yana nema wani abu, har lokacin dana aje mai goran magani a gefen shi.
Kin sha kenan ya fada ba tare daya jiyo Inda nake zaune ba, na amsa da eh nasha malam nagode na fada a sanyayye.
Kai haha dai wanan aiyiwa kaine ne hidima mukaiwa banza don a zauna lafiya balle namu jinin mu fatan mu dai ladabi da biyayya ga miji shine abin bukatan mu.
Karbi wanan ya miko min wani abu kamar bawan icce yana fadin ki saka a baki ki dinga taunawa a hankali koda a wayane ki fadi bukatan ki gareshi yau kiga aiki da cikawan wanan.
Na baki wanan din ne ba do komai ba sai irin bayanin sa uwarki tazo mi dashi koda yayi wana auren ne da nufin ya cutar dake Allah ba zai taba bashi ikon hakan ba a kanki wanan kuma dan bawan iccen da kike gani a hannun ki aiki shi gareki yafi akirga ki dai saka a baki kamar yadda nace dake yanzu ya kara bada da sauri na dan balle na jefa a bakina sauran na bude yar jakkana na kada a ciki.
Addu,oi masu ma,ana ya ban tare da min nasiha akan zaman aure da rike duk wa yanda na sama a gidan da zuciya daya duk wanda yace zai bini da sheri abinsa zai koma mai zuwa safe zaibawa yaron shi wani rubutun akawo min na sha.
A nan yake min bayanin tafiya da matar shi tare da hikimar shi nayi hakan wanda shi yasan dacewan zuwa da ita din da zamuyi da irin ranan da zatai min a can din idan mun tafi baidai fito fili ya fada min komai ba ya barshi a dunkule hakana.
Munyi sallama dashi da matan gidan da muka samu su fito dukkan su waje ana girkin abincin dare gwanin ban shawa dasu kansu hade ake komai a gidan.
Yamma lis muka shigo gidan mu don dan biye biyen da muka yan gidajen yan uwa da kawayena kafin mu shigo gidan .
Sallama mukeyi ga lantana a tsakar gidan mu kamar ba musulma ba ta kyalemu bayan sai data juyo ta kallemu kafin ta hakademu gefe guda tana jan tsuki taci gaba da abinda takeyi a wurin.
Muryan innan mune da taji sallaman mu daga dakin ta tafito tana fadin kundawo ke nan yanzu nake fada daku a raina don me zaku bari ai magariba kuna waje.
Marigaba fa matattaram sheri ne ko sa,an ka ake son a samu a daidai wanan lokacin akanci galaban mutum ai mai sheri.
Muna ta sauri wallahi inna nasan bakya son ai fita a wanan lokacin na fada ina kokarin cire hijjab din dana saka a jikina da zan fita.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.