Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 129 of 139

ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAN UWA FATAN ALHERI GARE KU KO YAUSHE UBANGIJI ALLAH YA SA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA DAMU DA IYAYYEN MU DA ZURI,AN BAKI DA TARE DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA AMIN, , , ,

YAR UWA KADA KI MANTA DA NOVEL DIN KUDINE KI SHAGALA BAKI BIYA BA AKWAI NAUYI A HAKAN KIN SANI, , , ,

Allah sarki yar uwa novel dina bana soyayya bane ko wani jin dadin duniya ina novel ne don fadakarwa a yadda rayuwa ke tafiya a yanzu don ki gyara da kanki ko ki gyara wasu ta hanyar novel dina ubangiji Allah yasa mu karu da juna anan duniya ranan lahira ke shedace akan duk abinda na rubuta a ciki.
Bana fata ko in yarda alkalamina ya kaini wuta don kawai in gyara maki rai in saka zuciyoyin ku a cikin wani yanayin dana san za,a tambayeni a kansa gobe kiyama.
Novel dina kan abinda ke faruwane a cikin gidajen mu na hausawa a yanzu da kuma yadda zaki fitar da yar ki ko kanwarki a cikin kangin rayuwa don haka idan zaki karanta ki karanta a hakan don idan kin lura wanan rayuwan na yanzu bawai don kayi aure zuciyar ka ya huta bane da itun kalubalin dake baya.
Allah ya iya muna yasa mufi karfin zukatan mu a rayuwan mu na zaman duniya Allahuma amin Allah.

Zaune yakai bakin gadon tare da dafe kanshi na tsawon wani lokaci yayin da gaba ya shiga faduwa don basan halin da yake jin kasa kusa ba.
Sanin shi din ba cikakken mutum bane kamar kowa a yanzu kallon da nake mai ke nan a zuciyana karfin addu,an iyayyene da ikon Allah dake aiki a kaina na tabbatar ya zaunar dani a yanzu gidan shi.
Don wani lokaci idan ina tunane zanji zuciyana yana raya min na gudu na tafi can duniyan da ba,a sanni ba inyi rayuwana acan da zama a gidan wanan munafukin Allah a yanzu.
Amma koda zan tashi sai naji zuciyana ya canza min shawara akan hakan zanjini wani lokaci wasai ko kuma ina tausayin shi.
Kinsan zama na hana mutum ganin laifin wanda kake zama dashi ko yaushe wani lokacin zaka san ba a daidai mutum yake ba kuma ka kasa rabuwa dashi a hakan.
Idona biyu dai a lokacin ina sauraren shi dan filin dana bari a gefen dana kwanta naji ya kai kwance a wurin hakan ya sani dan bude idanuna ina kallon shi a fakaice.
Kwanciya yayi a rigingine tare da daga kafanshi daya ya tokare na dan kada shi kadan ya jingina bayan shi da kan gadon yana kallon saman dakin.
Zainab a tunane a yanzu ba zaki iya fadawa kowa matsalan ki na zama tare dani ba duba a yadda na rikeki a zuciyana nake gani.
Sai dai kash a she yadda na dauka abin ba haka yake ba ke a wurin ki a zuciyar ki kuma kuma koda yake kinyi kokari a hakan ma don sam banga laifin ki ba ko kadan zainab.
Nasan wanan kwarai ban cancanci wata mace ta zauna dani ba a hakan sam don yadda rayuwana yake da akasin da mu hausawa mukafi tsana a duniya.
Allah yasan nasan kinyi hakkuri kan hakan amma ki kara dora hakkurin ki akan wanan din don ni kaina jikina yana ban zan bar wanan harkan nan gaba kadan insha Allahu.
Sai lokacin na samu magana don hakkurina ya kai karshe a lokacin na fara fadin ka daina ka daina shan giya ko ka daina kwana da maza yan uwan ka ko kuma tsafin zaka daina ?
Naji yace hummm zainab ke nan a yanzu nasan kinsan komai don haka kome zaki kirani dashi ki kirani dashi a yanzu din ya fada yana runtse idanuwan shi a hankali.
Wani iri naji a raina ba dadi don hakan ya zama kamar gori nayi mai a yanzu din ban san lokacin dana bude bakina ina fadin
Nasan jarabtane hakan a gareka don Allah kan jarabci imanin bawan sa tako wani hanya don yaga karfin imanin shi to amma yaya tunda ka gane hakan ka yaki zuciyar ka ka mayar da lamarin ka ga ubangiji ka Allah shine mafita.
Ka dauka ba mai iya yiwa bawa komai a duniyan nan sai Allah shike kashewa ya raya kuma aduk lokacin daya so hakan ga bawan sa.
A jiyan zuciya naji ya sauke daga inda yake kwance din a gefena naci gaba da fadin yau yaya baka zama kayiwa kanka tunane akan wanan rayuwan naka.
Idan akace yau babu kai dukiyan naka da kake nema ya zama ganima da abin wasoso ga duk ahalin ka .
Tunda ba zuria ko wani ka aje a duniya da zai gajeka ba a yanzu a kadara kana da zuria din yaya yaya ka ke son su kasance a cikin al,umma da rayuwan su.
Ni kaina a yanzu a kunyace nake shiga yan uwan ka tunda ina ganin kowa yasan irin rayuwan kyaman da kakeyi a yanzu balle yayan ka na cikin ka da kowa ke maka fatan samu a duniyan nan.
Ina maganan nan ne badon kwadayin abinda kake dashi ba ko dan nagada a,a ina magana ne don tsakanin mu dakai ba a san gawan fari ba a wurin Allah .
Kadara kai namiji ne a kullun mami tana maka fatan samun wata macen wayayya wace ta dace da rayuwa irin naka.
Ya kake tunanen zataji idan ta riskeka a cikin wanan halin baka tuba ka koma ga ubangijin ka Allah ba kana zaton zata kyale duniya bata jiku ba ke nan.
Hannun shi naji ya dora a saman kaina lokaci guda ya dafa min kai yana gyara kwanciyan shi a yadda yake kwancen da farko.
Zai,nab naji ya fada a hankali tare da sauke numfashi a cikin wani irin yanayi ya fara magana a hankali yana fadin .
Nima a kullun akai zancen haihuwa gareki ina mai jin zafin hakan don nasan laifin ba naki bane nine mai laifin ga baki daya kuma ake dorawa a kanki.
Nasan ba ko wace mace bace zata iya daga min kafa a hakan koda kuwa duniyan nan da abin cikin sa nake bata alherin shi a kullun.
Sai a asirina ya tono ga jamma,an duniya zuwa yanzu din kowa ya gama sanin koni waye a hakan nayi nadama ina fada maki ko yaushe kan shigana wanan harkan duk da ba zance ga lokacin dana tsinci kaina a hakan ba duk da nasan ko nayi rantsuwa ba mai taba yarda da zancena a yanzu.
Tsam naji a duk kan ilahirin jikina don jin saukan hannun ya jafar da nayi ya sauka a jikina wanda hakan ya sani dan razana da yin hakan da yai min din a daidai lokacin da ban taba tsamanin hakan ba a gareshi.
Dan tsoratan da nayi din yayi daidai da runtse idanuwan shi a daidai lokacin yana jin wani bakon yanayi yana sauka mai wanda hakan yake ganin sa kamar zai aikata wani sabone gayin rikon da yai min din a lokacin.
Sai dai kuma duk da hakan ya kasa cire hannun shi daya riko ni dashi a jikina din a lokacin maimakon ya cire din kamar yadda zuciyar shi take gargadin shi da yi saima kara rikoni da yayi a lokacin ya matseni sosai a jikin shi .
A daidai saitin kunne yake magana yana fadin kamar mai rada kin san me zainab ban samu ko fadin a, a ba gareshi a yadda nake razane dashi a lokacin.
Tsorona daya shine kada ya matseni yace zai min dole ta baya wanda hakan tun lokacin da umma ta umurceni da zuwa dakin shi koda bana son hakan idan nazo na saba zanji duk abinda nake ji a kanshi ya gushe min a zuciyana.
Wanda ni ba komai nakewa tsoron haka ba sai gujewa bacin rana irin wanan yaga kamar ni din irin mazan da suka saba mu,amula da sune yazo ya halakani a banza banji ba ban gani ba.
Kaduwa sosai jikina keyi naji yana fadin ko kowa bai yarda da rantsuwana ba aduniyan nan ke zainab nasan zaki yarda da abindana fadi a kaina a ko inane kuwa zaki shedeni a kan wasu halaiyana da kika sani a baya da yanzun da nake fadin na daina din a yanzu.
Duk da tsoron da nake ji a lokacin nasa hakan baisa hankalina ya gushe har na kasa fadin yardan Allah da amincewan shi a yanzu gareka yafi na kowa da zaima ka.
Don Allah subbahanahu kaiwa sabo kuma yafiyan shi zaka nema a yanzu don ya yafe maka kurakuran ka yaya.
Komawa ga Allah gareka a yanzu shine babban abinda ke gaban ka duk na mutane mai saukine .
Allah zai iya sa mantuwa ga zukatan wasu su manta da ka taba aikata hakan a baya, tuban ka zai iya sa Allah ya shafar dasu komai a kanka ga baki daya.
Banyi aune ba a wanan lokacin da nake maganan sai ji alaman kukan nadama da naji yana yi a lokacin.
Nima kukan ne yazo min don ko banza naga wani na kuka haka nake nima sai hawaye yazo min balle wanan da yake shakikina a yanzu mafi kusa dani da kowa a duniyan nan yana cikin wani hali na rayuwa.
Da kyat yayi shiru koshi wayan shi dake ta ringing ne a lokacin ya sa ya mika hannu ya dauka ba tare da yayi magana ba sai sauraren mai magana a lokacin da yayi.
Yana gama wayan ya kashe ya aje a gefe daya ya rufo hannayen shi gaba daya a saman jikina lokaci guda ya matseni ta yadda muke iya jin numfashin juna a lokacin a haka kowa da nasa kalan tunanen barci ya daukeni a jikin shi .
Misalin ukun dare ina barcin kamar a wahalce acan cikin barcin nake jin wani irin nisi a kusa dani wanda tun kan na bude idanu nasan inda nishin yake fitowa .
Shine duk da yana cikin wani irin yanayi hakan baisa ya raba jikina da nasa ba yana rike dani da hannun shi daya a jikin shi.
Yayin daya dafe maran shi da hannun na hagu yana yanka wani irin gumi tun daga kafan shi har zuwa kanshi .
Na tashi a rude ina kokarin kwacewa don na samu na taimaka mai a halin da yake ciki yake fadin kada ki daga nan zainab .
A wahalce yake magana a lokacin duk da na saba da ganin hakan wani lokaci wanan yanayin yafi na duk wanda yayi a baya muni sosai.
Can yakai ga wani irin zabura kafin ya kai ban daki ya fara wani irin kakarin amai kamar zai zubo mai kafin yakai bayin a lokacin.
Ganin hakan yasa dole na mike zaune ina binshi da kallo a cikin yanayin da yake din na ban tausayi da al,ajabi.
Don nasan wanan halin da yake ciki a yanzu yana da nasaba da rikon da yai min muka kwanta a tare ya jawo mai wanan wahalan haka.
Raina naji yayi wani irin baci lokaci daya na gyara zama ina hada kaida gwiwa na takure a wuri daya na dinga kuka a hankali.
Yafito bayin dafe da maran shi yana tafiya dakyat yazo bakin gadon ya dan zauna a gefe ya dukar da kanshi kasa kamar mai tunane.
Sauka nayi zuwa ban daki na dan dauki lokaci na gyara ko ina koda na fito na samu yana sallah a zaune na bishi da kallo.
Muna zaune ba wanda yai magana a cikin mu kowa na lazumin shi motsin da naji daga bayan mu yasa na dan firgita kamar anyi tsoki an fita daga dakin nashi lokacin naji da kunnuwana sai dai Allah ya gyara ban yarda na juya ba .
Wani irin iskane aka fara yi a wajan gidan kamar hadari ya yaso a garin ko guguwa mai karfi cikin dan lokaci kuma muka daina jin hakan.
A daidai lokacin ne na kula da yanayin da yaya da ke zaune a kusa dani yake ciki yana wani irin kaduwa kamar mai jin sanyi ko zazzabi mai karfi a lokacin.
Ni kan naga ta kaina a wanan rayuwan yau nice auren dan giya dan luwadi dan mafia kuma ashe shiga kungiyan ma bala,ine kala kala a rayuwan mutum irin haka.
A dadafe mukaga safiya dashi saidai wanan karon akwai bambamci ga yadda na saba ganin shi a baya idan yayi ciwon shi gari yawaye sai ya mike tamgararan.
Wanan karo kan yasha bamabam da wacan din don zuwa safe kamar ciwon karuwa yakeyi a lokaci.
Sai amai da gudawa yakeyi sosai wanda hakan ya tayar min da hankalina ya mamud na kira a boye don yayi min kashedin fadawa kowa halin da yake ciki din a ranan.
Ba bata lokaci ya iso gidan layina ya kira na fada mai ina sama wurin shi ya sameni a nan saman dakin shi do ban fito ba har lokacin.
Yana ganin yanayjn da dan uwan nasa yake cikine ya rude tare da tambayana zainab yaushe ya fara hakan nace dashi.
Lafiya lau muka kwanta dashi zuwa rabin darene hakan ya faru dashi har wanan lokacin wanan kan ba abin kyalewa bane dole mu sanarwa mami taji ya mamud din ya fada .
Layin mami ya fara nema ya fada mata nan ta hau fada don me ba a wuto dashi asibiti ba tun dazun ko so muke ya halaka a gida.
Mami kizo fa wanan kan ba abin kaiwa asibiti bane gaskiya sai jikinta yayi sanyi ta koma magana a hankali tana fadin .
Wani irin yanayi ne mamud kuyi wani abu don Allah kafin na karaso ta fada hankali tashe me zamu iyayi ga hakan mami sai kawai ta fashe da kuka ya kashe wayan.
Ina jin haka nace yaya ina zuwa na fita zuwa dakina bincike na fara yi kafin ingane maganin da tsohuwa kakan maya tayi min bayani ranan idan naga irin yanayin nan tare dashi.
Na fito da sauri zuwa kitchen na jona heater dan kankanin lokaci ruwan ya tafasa na hada komai na nufi dakin yan aikin gidan sai faman gaidani sukeyi da kwana ban tsaya binta kansu ba yadda na saba sama sama nake amsawa idan sun gaida ni din.
Dakin na nufa na samu yaya ya kamashi zuwa bandaki sun fito na shigo dauke da cup din maganin ina mashi sannu.
Saidana aje cup din nake fadin ya ko zaisha wanan maganin kafin mami tazo mu gani yace zaisha mana zainab kin hadane ya fara sha agani.
Na dan zauna ina fifitawa har yayi sanyi don ta fada min sai yayi sanyi sosai zaisha kamar yadda tace din haka nayi komai daki daki.
Yana kurbawa na farko ya saki wani irin gyatsa mai karfi lokaci guda sai kuma ya fara hamma ba kakautawa muna tsaye muna kallon shi nida ya mamud din .
Ya kara sake wani irin gyatsa har mai warin tsiya saida muka kawar da kanun mu ga kallon shi da sauri anan kasan ya leme sai barci .
Dan uwan na fadin ka hau gado idan barci zakayi zaifi ma dadi jafar ina har barcin ya kwashe shi ko a lokacin.
Daga inda nake na sauke ajiyan zuciyar da har ya fito fili ban sanda hakan ba sai ji nayi ya mamud na fadin .
Zainab kiyi hakkuri da wanan jerabawan da Allah ya aiko maki dashi haka tun ran gini ran zane Allah ya rubuto kece zaki shiga a cikin wanan wahalan haka.
Godiyan mu ga Allah da hakan ya kasance kece a gidan shi a matsyin matar shi a yanzu da wata ce ko wace mami ke gani a lokacin itace ta dace da jafar din ai da tuni zancen ya wuce nan ko.
Amma yanzu kinga tun mami naganin kwadayine har yanzu ita da bakinta ta gane gaskiya tana godiya da haka ya kasance kece a matsayin mata a gareshi.
Nasani zainab watarana mami zata rokeki gafara da bakin ta kan hakan tunda yanzu tasan abunda Allah ya shirya a zaman ki dashi haka.
Hakuri yana da dadi zainab don hakkurin ki yayi muna amfani kowa yanzu ya sani Aisha kanta jiyan nan nake jin tana fadin bata san da wani ido zata kalleki ba a yanzu.
Ko yanzu na sani maganin da kika bashine Allah ya taimakeshi ya samu barcin nan da yayi a yanzu don wallahi da badon Allah ya gyara ba yasha wanan abin da bansan me zai faru ba zuwa yanzu gareshi.
Hawaye ke fito min a idona na kurawa inda yaya din yake kwance ido kawai ina kallon shi ga mutum har mutum idan ka ganshi amma ya samu akasin rayuwa a tare dashi.
Muryan ya mamud din ne yake fadin ni nasan babu yarinyar da zata zauna da jafar ko na tsawon wata daya a wanan hakin haka da yake ciki.
Yanzu ne kowa zai gane shi mutum yana da ranan shi ta hanyar da baka taba zato ba don ance ke yar tallakane baki cancanci auren shi ba a lokacin.
Sai Allah ya nuna muna tallaka yana da ranan sa sosai don zaiyi abinda kudi baya iyayiwa mutum shi a rayuwa don na tabvatar da zabin mami din ya aura a lokacin da yanzu wallahi duniya ta gama sanin komai a yanzu.
Sallaman mami da su jamal ne da suka shigo hankali tashe dakin ya katse shi ga maganan da yakeyi a lokacin.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.