Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 103 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWALITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA YAR UWA DON GUJEWA FADAWA HAKKIN WANI NA SAUKE NAUYI NA FADA ALLAH YA BADA IKON TSAREWA ALLAHUMA AMIN.
Bayan mun dan gama zaman da zamuyine ya samu ya mike da kyar muna mai sannu da jikin yana dafe da cikin nasa ta gefe haka ya bar falon ya tafi.
Na sauke ajiyan zuciya bayan fitan shi daga part din ina mikewa tsaye kallon sadiya nayi ina fadin shige ki kwanta dare yayi yanzu.
Ta mike ba don taso ba ta shige tana turo baki gaba na kashe wutan falon na shige ciki don in kwanta saboda gajiyan dana debo a ranan.
Saidai kodana kwanta barci ya gagareni sai faman tunanen abinda ya wakana a falon tsakanin mikewa nayi zaune don kwancin ya gagare ni a lokacin.
Tabsa yaya yana ji jiki don iyanzu yakai ga fadi da bakin shi ga alaman hakan kuma ina gani shawara na fara yi a zuciyana na yadda zan bashi wanan abin da tsohuwar ta kara bani yasha a yanzu.
Abinda ban sani ba shine ashe yana can daki yana mukurkusa shi kadai yayi amai tun yana iya tashi yaje yayi har tashin ya gagareshi.
Da kyat ya iya daga waya ya kirani muryan shi kawai ya isa ya sanar ma da halin da yake ciki a rude na mike dagani sai rigan barci zuwa dakin nasa a rude.
Kai ba dadi a yadda na same shi a kwance kaca kaca a cikin amai dan ihu na saka a cikin gigicewa yayi saurin bude idanun shi ya sauke su a kaina yana fadin.
Kada kiyi kuka zainab nasan nina jawa kaina wanan kila giyan da nake sha ne yake min haka a yanzu .
Ka bari in baka wani magani da nake dashi kila zai taimaka ma kafin mu kira muje asibiti dan murmushin karfin hali ya sake a fuskan shi.
Haka yasa na juya da sauri na nufi dakin na tsaban rudewa ma baisa naga maganin da farko ba sai na dauka nayar dashi ne wurin sauri.
Baki yar ba zuciyana ya bani hakan na tsaya nema a tsanake na ganshi can kasan jakkana dana jefa.
Da sauri na dauki na nufi kitchen din mu na hada na kai mashi baiki sha ba da taimakona ya mike ya shanye ga baki daya ya koma ya kwanta.
Kallon gadon daya baci nayi cikin dabara da hikima na gyara ko ina cikin ikon Allah sai gashi ya mike wai zai kewaya shine na samu daman gyara ko ina yadda nake so.
Da alama ya samu sauki sosai don har ruwa ya watsa a jikin shi kafin ya fito don yaji dadin jikin nasa daya sake mai.
Nina taimka mai ya saka tufafi a jikin shi can kuma ya yunkura kamar zai kara amai da ban san lokacin dana tallaboshi ba sa sauri.
Yana ta kokarin kakarun aman bai samu fitowa ba ya koma ya kwanta sai barci ganin haka na dauki wayan shi na nemi layin mami na kurata.
Tana dauka take fadin jafar ya akayine ya jikin da sauki ko nace a dan maraice mami bashi bane nine gashi kwance yau jikin ba dadi sosai.
Innalillahi tace a rude yanzu kuna asibiti ne ko gida muke mami idan na masa maganan asibiti baya son zuwa ne.
Ke wata irin yarinyace da har yanzu baki waye ba zainab idan kin masa magana baiji ba baki kaisa ko ki fadawa abokan sa suzo su kai shi mana.
Ban san abokan sa ba mami kuma yakan ce dani ai yaje asibitin idan na matsa mashi din.
Zainab idan kika bar min da ya halaka a kasan mutane ba zan yafe maki ba wallahi.
Mamaki da rudewa ne ya kamani lokaci guda na rasa amsan da zan bata sai kawai na kashe wayan gaba daya na aje a gefen shi don kunnuwa ba zaici gaba da iya sauraren wanan matar ba a yanzu.
Juyawa nayi inda yake kwance na dan kalleshi barci yakeyi har lokacin nima na dan kwanta a gefen har barci ya dauke ni ban sani ba a wurin.
Washe gari abin mamaki ko daya tashi sai naga ya mike da kansa saidai rashin karfin jikin da baida shi a lokacin.
Ya dan dade a cikin ban dakin kafin ya fito ya tayar da sallah a tsaye nan nasan yaji saukin jikin sosai mamaki karfin magani irin nasu nakeyi a raina.
Ya dade zaune yana addu,a kafin ya mike ya koma ya kwanta saman gadon ya koma barci ranan dai ban fita ba don yanayin da yake ciki din.
Yakai wani lokaci mai tsawo yana barci kafin ya tashi yana neman abinci yaci ya sake yin wanka ya fito a lokacin ya kunna wayan shi dake kashe.
Kamar jira ake ya kunna kira ya kama shigo mai wanda kiran daga nan chaina ne abokai da wuri aiki suke kiran shi.
Ban fada mai komai kan zancen wayana da mami ba saida ta kira shi da kanta tana fada wai haka kawai don keta na barshi gida ina kallon zai halaka ban kira a kaishi asibiti ba.
Haba haba mami yarinyar nan fa tayi kokari sosai a kaina kuma ko yanzu tana ciki yin sa ne.
Kaima ai kana kokari akan su don me ita bazatayi ba har tana fada min wai kana gidane a kwance.
Haba mami zainab bata cancanci wanan kalamin ba a gurin ki don nasani ta tare shi da fadin ta yata zata biyewa rashin hankalin ka ta barka a gida.
Ko dai meye ai mami zainab mata tace tasan zafina tasan ciwona don haka yarinyar nan tayi duk yadda akeso fa bai yarda uwar tayi wani magana ba kuma.
Suka dan dai taba hira akan ciwon nasa tana tambayan shi ainihin abinda ke damun shi tare da kara nuna mai bakin cikin ta kan halaiyan da yake yi wanda take zaton shi yaja mai wanan ciwon haka a yanzu.
Har dare yana duban yanayina ko zan nuna wani bacin rai kan abinda mami din ta fada mai nayi mata baiga alaman hakan a wurina ba shima sai ya share zancen baice dani komai ba.
Da dare na shigo na gaidashi tare da bashi abinci ban fita ba saida ya gama na mike zan bar dakin naji ya ambaci sunana da fadin .
Zainab haka yasa na juyo da sauri baiyi magana ba yasa na dan kara matsowa inda yake ban dai zauna ba amma na tsaya a cikin ladabi yake fadin.
A lokacin daya lumshe ido idon shi a rufe zainab me kika bani nasha jiya ne naji sauki haka da sauri ?
Magani oh wanan maganin ya dade a wurina dama dashi nazo tun daga gida na waraka ne kan cututuka ko wani iri na bashi amsa.
Ya bude ido yana kallona kamar me nazarin wani abu ya ce dama kina dashi tare dake baki bani nasha ba nake ta wanan wahalan haka naji dadin magani sosai ina shan sa kamar an zare mi ciwon naji lokaci guda.
Ban taba amfani dashi ba na fada ina juya don na matsu in bar wurin a lokacin kada ya kureni har ya gane ba gaskiya na fada mai ba.
Kwana biyu kwatsam su mami suka diro garin shi kanshi bai san da zuwan su ba ban nuna mata komai ba don tun lokacin da mukai wayan nan da ita wani abu bai kara shiga tsakanin mu ba kuma koda wayane.
Don sai naga kamar kwata kwata dai mami bata yi danine a rayuwan ta don banga laifin da za a dora min kan mutum mai shekaru kamar ya j ace wai nice zan matsa mai ya kula da kansa bayan shine ya kawo mu kasan ai.
Nan muka shiga dawai niya da su kamar ba komai a zuciyana sai dai a gaskiya na barwa kaina duk wani abu da nake shiryawa a yanzu game da kowan su gidan.
Lafiya kalau zan shiya masu abinci idan masu aiki sun gama ba zan fita ba sai na gama dasu don wanan tafiyan ba irin wancan bane da sukazo da yawan su .
Wanan daga mami sai samarinta biyu da Aisha kawai suka zo part daya aka bar masu don hakane ba wani takura a tsakanin mu yanzu.
A yadda mami take matukar son diyan ta wanda a yanzu na kara gane hakan sosai yadda duk da ya J yaji sauki a yanzu.
Amma hakan bai sa wai mami ta nuna wai ita jinyar jafar din takeyi ba a fili tana nuna tafi kowa sanin zafin dan ta da sanin abinda yake damun shi .
Wanda banyi tunanen cewa jafar din zai fada mata ba don da zai iya fadiawa wani nasan nice ta farko da zai fadawa hakan.
Kawar da ido da kai ga komai yasa mami din bata samu wani kafan yi min wani rashin mutunci ba don haka muka zauna lafiya da kowa a cikin har azumi yazo suna kasan tare damu.
Ranan a na zaune da safe samarin basa ciki suna waje sai shi da mami da Aisha ne sai ni da na shigo gaida mami din da safe zan fita zuwa school.
Baki fita ba ke nan har yanzu kina gidan nan ya fada yana zaune a kasa kusa da kafan mami din abinda ban taba ganin yayi ba tun zuwan mu kasan zama a kasa.
Karatun ai ba wai ta saka a ranta bane nake ganin mami ta fada ya dan gyara zama yana fadin ai mami zainab ta saka karatun nan a ranta sosai kuwa.
Zainab din zaka ban labarin halinta a yanzu kuma jafar don ta zama matar ka komai ko ta canza ne ban sani ba ?
Sorry ma na mance kin fini sanin halinta ai tana nan har yanzu da sanyin halin nan nata ai sai mami din taja wani tsuki tana kawar da kai.
Aisha tace ya j ai yanzu ba zaiso a fadi wani kalma a kan zee ba koda tayi laifin ma balle yana ganin batayi ba .
Aisha ke nan ki bar ganin mami da zainab suna abin su na uwa da yarta kice zaki saka baki tsakanin su har yanzu sai Allah ni zan baki labarin hakan.
Ni dai ina zaune a inda nake ban ce da kowa kala ba a cikin su naji yaci gaba da fadin a daidai lokacin dana mike tsaye yana cewa.
Har sako fa mami zata aiko dashi tun daga can ba zan san da hakan ba sai idan tunanena ya bani haka.
Sako kuma naji mami ta fada da dan mamaki ni dai fita nayi ban karasa jin zancen su ba.
Sai bayab na dawo ne na shiga gaida ita ta tsareni tana tambayana da fadin zainab jafar ya gaya min kece kika bashi magabin da yai sanadin barin shan giyar sa ko ?
Na dago kai da mamaki tace ya fada min komai don shi a nasa zaton ko nice na aiko da abinda kika bashi din har yaji sha ya fice masa a rai ina tsaye ne a lokacin sai nakai zaune.
Kafin ta kara fadan wani abu jalal ya shigo dakin yana fadin mami garin nan yana da dadin azumi sosai don basu da zafi irin namu can Nigeria gaskiya.
Jekiki huta zamuyi maganan daga baya mami ta fada don ganin jalal din ya kai zaune a lokacin .
Ya dago ya kalleni yana fadin dama magana ake irin na uwa da yarta nima dai ina ganin irin auren ya j zanyi mami in samu mata kamar zainab din ki don bana son mace irin Nuriya gaskiya.
Fita nayi daga dakin ina dan murmushi don abinda ya jalal di ya fada saidai zuciyana cike da zargin maganan mami yake alokacin
Bata kara min maganan ba nima haka banwa ko J din maganan ba saida akai azumi ashirin suka tattaro suka dawo Nigeria.
Munyi sallah lafiya wanan sallah har idi muka tafi wanda hakan bai taba faruwa damu ba tun zuwan mu a gida zamu dai zauna .
Sai dai mu kalla yadda ake bukukuwan sallah a kasashen duniya wanda mu nan cikin gida muke babu wani celebration da mukeyi.
Sai gashi a wanan shekaran tun da daren muka bar gidan mu muka kwana a wani hotel a cikin wani unguwa ashe a can ne masallacin su yake da suke sallah a garin.
Bayan an sauko ne motocin mu suna jiran mu muka dawo namu gidan wanan kan mun san ayi sallah don yadda yaya ya nuna muna har kwana biyu muna shagalin da murna da kai ziyara a gidajen yan uwa musulmai dake kusa don suna da musulmai tsararu a cikin kasan sosai ashe.
Hutun sallah ba yawa ga ma,aikata don haka sati daya mukayi ana shagalin muka koma makaranta don ci gaba da karatun mu.
Yaya kan a bangaren shi jiki yayi sauki sosai don bai wanan dafan cikin da yake yawan yi a baya yanzu.
Gashi yayi wani kyau raman da yayi don zafin ciwo a baya duk yanzu yana shigewa ba a ganin wanan sosai a jikin shi don dan cikowan da yakeyi yanzu ba wannan kaman.
Sai dai ina yawan tuna halaiyan mami na nuna kiri kiri son danta akan komai da take min don na lura nami ba ganin laifin dan nata takeyi ba asalima tana kokarin dora komai ne a kaina a ganina.
Don ko dan zaman da mukayi dasu anan duk da da farko taso nuna hakan a fili amma daga baya sai naga kuma ta canza ta daina nuna min wani abu.
Nima sai na dauka a hakan nake nuna ba komai a raina don haka kowa ya aje a ranshi da ba komai din dai.
Ganin yadda yanzu yaya ya koma wani silent bai son hayani duk da dama can din shi din ba mai hayaniya bane sosai amma dai sai na yanzu din yayi yawa sosai.
Don zai iya zama a wuri duk abunda zamuyi ba zai ko daga kai ya kalli mutum ba balle mu saka ran zaiyi magana kan kiriniyar mu har ya gaji da zaman shi ya tashi a wurin zuwa part din shi.
Gama sadiya da har rawa da marming zata dinga yi koda yana zaune don ba karamin sabawa sukayi ba dashi sosai a yanzu.
Wanda tun ina zargi a kan hakan har yakai na debe komai a raina nima mai dan girman bai damu dani ba balle ita da keda sha uku yanzu cif a duniya.
Yau ma kamar kullun ya dawo wirin aiki da yanzu mun saba dashi idan ma ya dora dan dakiku a kai mun sani zamu fara fadin yau yaya bai dawo in time ba.
Shiko da ya dawo baya zuwa part din shi kamar yadda yakeyi a baya nan wurin mu zai shigo direct mu gaisa ya dan zauna damu na lokaci kafin ya shige part din shi sai kuma bayan sallah isha,i zai fito aci abincin dare a tare tun bayan zuwan su mami wanan ya zama muna dabi,a a gidan yanzu.
Zaune nake na tasa laptop a gaba ina aiki ban san shigowan shi part din namu ba don itama sadiya ta shiga ciki dauko littafin da take assigment kan shi.
Muryan shi ne daya duka bayan kujeran dana zauna na mike kafa ina aiki a cikin system din na shagala ga karanta abinda nake sercheing a computer din.
Naji muryan kamar daga sama yana fadin wanan ai da wuyan fanhinta da kin bi ta cikin Google direct zaifi ki fahinta ai.
Ganin yadda na dan kadu ne yasa ya dan shafo kaina yana fadin kin cika tsoro da yawa duk security din dake gidan nan amma kike tsoro haka zainab ?
Ban ji fitowan ka bane yaya sai muryan ka danaji a kaina yasa na tsorata da hakan.
Zagayowa yayi ta gabana ya zauna yana fadin when last kukayi waya da mami tun bayan komawan su gidane wai ?
Da sallah ma ai munyi waya sau biyu dasu na bashi amsa ina dagowa daga duken da nake ina kallon shi don jin dalili tambayan nasa.
But tace dani mana yanzu kin daina kiran ta duk da na fada mata kin fara exam a yanzu baki da lokacin komai saidai tayi fada cewa exam ai ba zai hana ki kirasu ba .
Zan kira na bashi amsa ina tagumi don nasan wani abin ke shirin tasowa kuma a kan wanan maganan da mami din tayi yanzu.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.