Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 3 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL TA BANK KO KATIN WAYA DON TURAWA A BANK ZAKI IYA TURAWA A WANAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK ALLAH YA BADA IKON BIYA A CIKIN DAUKI AMIN
Ki daure ki guji shiga hakkin wani abinda ka raina shike zama babba gareka don Allah yar uwa mu guji daukan hakkin a kan mu ki daure ki biya ki karanta don Allah.
Hjy ce zaune a falon ta hannun ta rike da waya kaya take oder da za, a turo masu dan yanzu ba sai ka fita zuwa waje ba idan kasa hutar da kanka waya ya wadatar da komai ga kowa.
Sallaman da akayi daga kofane ya dawo da ita cikin hankalinta ta dago kai tana kallon kofan shigowa falon nasu.
Da fara,a a fuskanta tana aje wayan daga gefen kujera take fadin kune tafe sannun ku da zuwa a cikin fara,a kamaf yadda ta saba tarbon duk wani dan uwa da zaizo gidan musanman daga bangareta kona mijin ta .
Yanzu ma yan uwan mijin tane su biyu sula shigo gidan barin abinda takeyi tayi ta tari bakin nata.
Yau kan mun taki sa,a kina waje don zuwan mu biyu ana fada muna kina ciki bazamu ganki ba.
A daidai lokacin ta sauke glass din dake idon ta tana fadin abako fada min zuwan ku ba gidan nan ko sau daya.
Dayan tace yau dai aimun taka sa,a mun samu kina wajen dan dariya hjy iyami ta sakeyi tana fadin mun dade bamu haduba.
Safiya ya bayan rabo wace ta kira da safiya tace wallahi haka al,amari yakan kasance ai rayuwa ke nan idan na tuna baya sai nakanji kamar abubuwan da su dawo sabo.
Dariya sosai hjy iyami ta sake tare da fadin kin tuna zamanin kurciya ke nan dai ga wanan zancen naki.
Safiya ta lumshe ido tana bin lafiyan kujera sanyin AC yana ratsa jikin ta a hankali tare da fadin bari matar yaya ai kowa tuna bara baiji dadin bana bane.
Jin hakan hjy ta fahinci mai take nufi yasa tayi saurin kawar da zancen tana fadin bari a kawo muna abinci muci nima yanzu na dawo gidan .
Yau na fita ziyarane har gidan su Ado da salihu nake don tun zuwa na garin ban leka kowa ba bako dadi mutum yana kulaka kai baka mayar da kara akace.
Tana fadin hakan ta mayar da hankali kan wayanta dake gefe dauka tayi ta kira mai aiki tare da umartan a kawo masu abinci tana da baki a falo.
Kai matar yaya wai wasu baki har yanzu dai wanan halin naki yana nan ashe ance idan kasan mutum ko shekara nawa ne kada ka tambayi halin sa.
Murmushi hjy tayi tana fadin meye duniya sa,ade wanan duniyan har nawa yake ga bawan sa.
Idan badon muzo mun gani da idanun mu bazamu taba yarda da kina nan a yadda kike ba a yanzu.
Wai sa,ade ina da wa yanda sukafi min kune a rayuwa duk mace mai hankali da tasan ya kamata ai baki nata ba ko yaya yake kuwa.
Don samun duniya sai idon ka ya rufe ka mata da goben ka ko makomar yayan ka yau fa in mune gobe bamu bane.
Wani lokacin koda kana raye sai kaga anayi ba tare da kai haka abubuwan suke zuwa ai kinga gara mutum ya gyara tun duniya bata kisa ba.
Mai aikin data kirane ta shigo dakin dauke da katon ture da manyan kuloli abinci saman shi dining ta nufa da zuman jerawa yadda ta saba.
Sai hjy iyami take fadin ki kawo muna nan yau a kasa zamu zauna muci dan dariya suka kwasa tare da fadin za a tuna da baya ke nan dai.
Lokacin da yaya yake aiki lagos muna gida tare dake ake zuba abinci a cikin katon ture mu taru munaci ana hiran arziki.
Ai wanan abin duk shigowan sadiya ya kawar muna dashi tana fadin wai muna taruwa ana gulmanta bazan manta da zuwan wanan yar uwan hjyn mu datazo daga kauye take fadin kema ai saiki fito ayi gulman dake.
Budan bakin sadiya sai cewa tayi ni ba zan shiga cikin su rainani ba ko ita wanan don diyan tallakawane ita bata san kanta ba.
Dan murmushi hjy iyami ta sake don tuna wanan labarin da safiya ke fadi yanzu sa,ade tace yau ina arzikin nata dana gidan su datake tun kaho dashi din.
Duniya ke nan alokacin tana dauka tafi kowa da komai bata san me gobe zai iya haifa ba a gare ta.
Hjy ce ke fadin bissimilah ku muci abinci ko juyowa sukayi a lokaci guda suna kallo abincin da mai aiki ta hada masu gwanin ban sha,awa kai kace wani dinner aka hada hakan .
Haka kamshin shi abin sone ga mutum balle ya kai ga baki yaji dandanon shi.
Daidai hjy na zama a kasan take fadin ance yanzu koyarwa kikeyi safiya ke kuma sa,ade nursece asibiti ?
Ashe kina da labarin mu ke nan har yanzu tana daukan cokali take fadin haba aiba zan taba mantawa da kuba a rayuwana .
Adaidai lokacin data fara bude kulan tana mika masu plate a gaban su da spoon da fork ga kofuna da lemoka don sha aka tabardar masu.
Nan kowa ya shiga dirkawa cikin sa abinci suna danci suna taba hira yayin da sanyin AC ya fara ratsa jikin su.
Sai da anty safiya ta hadiye naman da take tauna a bakin ta na kaza take fadin a gaskiya mun gode daz bamu lokacin ki da nuna rashin kyama ko babbanci a garemu yadda ake nuna muna har yanzu a gidan mu.
An mayar damu bare a cikin dangi duk kokarin da baba yayi yaga ya hada kan zurian shi kafin ya bar duniyan nan .
Zan iya cewa daga ke sai mijin kine baku nuna muna wani bambanci a tsakanin sabanin sauran dake yawan nuna mu barene a cikin su ko yaushe wani abu idan ya taso na family din mu.
Din kawai mu uwarmu kadai ta haifa a cikin su lokacin da yaya ke raye yana iya kokarin shi damu amma tun bayan rasuwan yaya din abubuwa suka kara lalace muna ga baki daya.
Wani abin saidai mu tsunci labarin faruwan shi a gare bamuci arzikin da za,a fada muna ba mu.
A hsnkali ta lumshe idanuwan ta tana maijin zafin yadda ake yawan nuna masu a cikin yan uwan su din.
Tace ku dauka har yanzu ma yayan ku yana a raye ne safiya don ya barni ya bar zurian shi komai ke damun ku kofa a bude yake dakuzo da bukatan ku nan mudin dai abin baifi karfina ba agidan nan.
Sallama yan matan hjy ne da suka dawo daga school saida su ukune kawai don farida yar wurin hjy ba a kaduna take karatun taba tun dawowan su suka sama bata gurbin karatu Abuja can take zaune tana karatun ta.
Sai hutu take dawowa gidan haka yasa idan ba hutu akeyi ba zaka gansu su uku ne kawai a gidan.
Kansu a sama suka gaidasu kamar basu sheda ko suwaye su din ba garesu don kawai raina masu arziki da sukeyi.
Safiyace take fadin wai ba Rufaida bace da salma nan dan juyowa salma tana fadin nice daga haka tasa kai tana kokarin shigewa daki.
Rufaida salma kuzo nan hjy ta fada a kausashe saiga su sun dawo da sauri suna fadin gamu mommy ta nuna su safiya da hannu tana fadin baku san wa yan nan bane halan ?
Mun sansu mama gwaggo safiyace da gwaggo sa,a salma ta fada a dan yatsune kafin hjy tace duk da kun san su saidai kamar baku san yaya suke da mahaifan ku bako ?
Nan kan shiru sukayi suna kokarin dukar da kawunan su kasa don sun fahinci mai hjy take nufi da fadan hakan.
Karna kara ganin kunyiwa wani babba wanan gaisuwan koda basu din bane wai salma sai yaushe zaku gyara halin kune don Allah ta fada a dan hasale .
We sorry mommy gajiyace dama ya hana mu tsaya dan Allah ku ban guri marasa ta ido kawai ta fada a dan hasale.
Bayan shigewar su dakunan sune anty safiya ta sauke ajiyan zuciya tana fadin kindai gani yanzu ke nan ai.
Wanan ba akidar kwarai bane ka nunawa yaro ga yadda kake da dan uwanka har abin yazo ya shafi naku yayan nan gaba.
Mikewa sa,ade tayi tana fadin antyce ma dai ta damu da wa yan nan mutane, nina dade da zubar da duk wani wanda ya nuna baison wata alaka zumunci dani ai.
Zancen ta baiwa hjy dadi ba ta fahinci akwai bacin rai a cikin halaiyan da yan uwa ke nuna masu kasancewar su su biyun yan uba ga yan uwan haihuwan nasu.
Sallama sukaiwa hjy tare da mata godiya da nuna jin dadin su irin taron data nuna masu din bata nuna masu halin da yan uwa suke nuna masu a cikin su.
Ita kanta bata samu mahaifiyar su a gidan raye ba saidai ga yadda take jin labari zamane akayi bana dadi ba a cikin gidan lokacin da mahaifan su suke a raye wanda itama ta dan ga wani abu a rayuwan datayi dasu gidan kafin Allah ya azurta mata mijin ta harsu bar gidan zuwa lagos karshe ma suka bar kasan ga baki daya.
Lokacin ita kanta sarakuwanta tana yawan nuna mata tayi hankali da yaran don su din ba jinin taz bane diyane kawai na maigidan ta da aka haifa mai auren baya daya kara na karamar yarinya daya auro.
Ga yadda take ji sarakuwar ta itace mata ta farko a guri mijin su saida sukai kusan shekara hamsim a tare ya auro mahaifiyar su safiya din.
A cewar hjy ita ba a hadawa diyan ta yan uba don haka ta hana mijin nata kara wani aure daga baya .
Surukin nasu yana sana,a a kauye har ya shigo birni ya fara sayar da kayan mata irin su dan kune da sarka da jakkuna.
Daga baya kuma daya bun kasa ne ya fara sayar da gwala gwale wanan ne ya kawo mai tarin arziki mai yawa har ya tamfasawa iyalan shi katon gida da suke zaune a ciki.
Bawai bokaye kawai ko asiri taga sarakuwar nata nbi ba saidai iri matan nan ne masu ji da izza da isa da gadara wanda take ganin yanzu diyan nata da jikoki suna koyi da wanan halin.
Saidai daga bayane kariyan arziki ya afkawa mijin nasu bayan siyasan shehu shagari da mazajen arewa da dama suka samu wanan koma bayan a sanadiyar canji da gwaunatin soja mai a lokacin ta kawowa mutane yayi sanidiyar karewa wasu bayin Allah da dama a cikin su har da surukin nata ya samu wanan iftila,in tare dashi.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.