Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 105 of 227

“Ka cika da yawa, ka saka kamar na su”

Ya rage ya saka daidai ya sake kira the same thing.

“Idan mun shiga ki ce Ummi ta kira shi ni wayata ta lalace bata kira kin ce ai abun da take cewa”

“Okay, ni meye number na?”

Gudun rigimarta ya saka dole ya bata number.

“2”

Ta share hawaynta da rigar jikinta sannan ta shiga falon, shi kuma ya juya ya shiga motar daman yana da gurin zuwa bata bari sun tafi ba tace ya kawo ta gida.
[6/24, 4:36 PM] My S Line: 43

Idonta be sauka a ko'ina sai akan Tea da ta bari dazun, kamin ta kalli dinning room tunawa da a nan ta bar Maleek a lokacin da suka fita, ba ta yi zaton Ummi ta dawo ba dan haka bata haura sama ba sai ta zauna a kasan kujerun da suke nan ta bude wani chocolate din tana ci, tana daf da cinyewa zomonta ya zo gurinta da gudu ya fara shinshina jikinta. Tana ganin haka ta tashi ta shiga Kitchen ta kunna tap ta wanke hannunta sannan ta dauki cup ta aje ta zuba ruwan zafi ta saka Lipton kamar yadda ta ga Ummi tana mata, sugar da sauran kayan hada tea da suke kitchen din sun mata tsawo domin suna a cikin cabinets ne, ita kuma ba wani tsayi ne da ita sosai ba idan ma zata ce ta dauko sai idan zata hau wani abun ne, dan haka ta dauko ta dawo dinning ta aje cup din ta bude sugar ta saka fiye da cube din da Ummi take saka mata sannan ta dauki daya ta kai baki tana tsotsawa, daki-daki ta bi har ta hada wa kanta tea ta dauko ta fito dinning area din ta dawo falo ta zauna, tana busawa saboda ya rage zafi.

“Idan Ummi ta dawo zamu ce ta kira Sulem ko?”

Baby rabbit dinta take tambaya da yarenta tana shafa kansa.

“Zill na baka labari? A can garin mu ina da bera da yawa a dakina, kuma ina da zakaru, kuma ina da Eid, na san yanzu ya manta ni, ko kuma yana jin haushin guduwa da na yi shiyasa ba zai zo ba na yi kewarshi sosai”

Shi dai zomon ya zauna a jikimta shiru sai saurarenta yake kamar fahimtar abun da take fada.

“Yanzu ni da kai Ummi ce mamanmu ko? Ko kuma ni ce mamanka kai ni kuma Ummi ce mamata”

Ta dauki tea zata kai baki sai ta kalli stairs Maleek dake tsaye rike da key ta gani tsaye yana kallonta. Babu annuri a fuskarta ba kuma fushi yake ba, rashin walwala ne irin ba wanda ke cikin tsananin damuwa domin idanuwanta sun nuna haka as well as fuskarsa. Aje cup din ta yi ta mike tsaye tana kallonsa a zatonta fada zai mata saboda fitar da Jabir yayi da ita, a kokarin ta na kare kanta ta duka ta dauki ledarta da cup din ta nufi inda ta saba boya ta zauna tana sauraren ta ji ko binyo ta zai yi. Shi kam bata ita yake ba, a zahiri ita yake kallo amman a badini tunaninsa da hankalinsa suna gurin damuwarsa ne. Ganin be wuce ba ya saka ta sake lekowa sai ta ganshi tsaye har yanzu inda ta tashi yake kallo sai dai wannan karon ta ga abin da ya daga mata hankali, hawaye ta gani a idonsa, saurin boyewa ta yi gabanta ba faduwa. Tana jin saukowarsa ta takure guri daya ta yi zaton gurinta zai zo, sai ta ji shuru hakan ya saka ta sake lekawa ta ga baya gurin, fitowa ta yi gaba daya, ganinsa ta yi zaune akan kujera ya cije ya cije baki yana kallon wani gurin dabam.

“Ya Maleek”

Yesmin ta kira shi be amsa mata ba be kuma juyo ba, sai yayi saurin tashi ya fice daga falon ba tare da ya bari ta ga hawayensa ba. Waira ta kalleta ba wani sabo ta yi da ita ba dan haka bata ce mata komai ba ta koma ta zauna a inda ta saba boya ta dauki tea ta rike da hannu biyu kamar yadda ta saba yi ta shanye duka. Sannan ta sake fasa wata ledar chocolate din ta fara ci tana yi tana lashe hannu, sai da ta gama sannan ta fito rike da cup din ta nufi kitchen jin motsi ya saka ta boye sai ta fara lekawa ta ga Yesmin ce ke kokarin kunna gas sannan ta shiga ta aje cup din ta wanke hannunta, bata san rike sunan Yesmin ba, dan haka ya saka ta matsa kusa da ita ta taba rigarta.

“Zaki kira min Sulem”

“Waye kuma Sulem?”

“Wanda ya zo, ko ki kira Ummi”

“Ummi tana dakinta, shi kuma Sulem ban san shi ba”

Tana jin haka ta yi saurin fita kitchen din ta nufi stairs da gudu ta fada dakin Ummi sai ta tarar da Ummi a bathroom.

“Ummi... Ummi”

Ta kira sunanta daga bathroom din Ummi ta amsa muryarta a shake.

“Na'am Baby Waira gani na fitowa”

Gurin kofar Bathroom din Waira taje ta tsaya har sai da Ummi ta fito, sai ta rumgume ta tana murnar ganinta ita dai idan Ummi bata cikin gidan bata da natsuwa da kwanciyar hankali duk sai ta ji kamar bata da kowa a duniya ta zama marainiya.

“Oyoyo Yata i miss you”

“Ummi baki tafi da ni ba”

Waira ta fada tana kallon idonta dake kumbure har bata oya bude da kyau.

“Waira ko dan kin ji ina ce miki Baby? Ke fa ba yar karamar yarinya ba ce da zan rika yawo da ke, daman can ai ba fita nake da ke ba, dan haka ki daina cewar ma ban tafi dake ba”

“Ummi idonki ya dahu”

Ummi ta yi dariya tana murza idon.

“Ciwo yake”

“Kuma Ha Maleek yayi kuka”

“A ina kika gani? Maybe saboda Nimra bata da lafiya ne, kin san tana asibiti ko?”

Ta daga kai, Ummi ta sake ta ta nufi wayarta dake cikin jaka tana ringing, bude jakar ta yi ta dauko wayar number one of ma su kula da gate din ta ne yake kiranta.

“Wa'alaikussalam”

“Hajiya an wuni lafiya?”

“Lafiya kalau”

“Na kira wayar Alhaji be daga ba shiyasa na kira wayarki, wani ne ya zo da mota yana son ya shigo ciki, na ce wa yake son ganin wai Zahra”

“Waye shi?”

“Bari na tambaye sunanshi”

Tana jin lokacin da yake ta tambayarsa ya sunansa amman yaki yayi magana.

“Musa bar shi ya shigo na gane shi”

“Toh Hajiya”

Ta aje wayar ta nufo falo Waira ta biyo bayanta. Yesmin dake zaune ta dago tana kallon Ummi wadda ta zauna kan kujera idonta na kan kofar falon, juyawa Yesmin ta yi ta kalli kofar sannan ta juyo ta kalleta.

“Ummi lafiya”

Ummi ta daga mata hannu alamar ta dakata. Da wani irin karfi aka murda kofar falon aka turota, daga Ummi har Yesmin da Waira sai da suka mike tsaye suna kallon Ameer da ya shigo falon fuska babu annuri, kai tsaye ya nufo inda Ummi take domin ba kallo kayan alatu suka kawo shi ba balle ya tsaya bata lokaci. Tsaye yayi a gabanta kamar without any rest yana mata wani irin kallo da ya fi kama da tsana. Waira ta saki baki tana kallon Ameer da mugun mamaki shi kam ko ganinta be yi ba domin baya ganin kowa a falon sai Ummi kadai daman zuwan nata ne. Yarfar da hannu ta fara yi tana son ta tuna sunansa ta kasa amman tabbas ta gane shi, abun ka da mai son mutane ta ga wanda ta sani sai jin yayi an shiga tsakanin shi da Ummi an rumgumeshi da karfi. Yana kokarin saka hannu ya ture kowaye ta dago kai shi kuma ya sauke nasa kan kasa dan ganin wanda ya yi masa wannan kasadar. Murmushi take masa mai sauti hakoranta a washe, lokaci daya ya gane wacece ita, ya tuna inda ya fara ganinta, alakarta da gidan ta tuna masa cewar ita ce yarinyar da ya saka a motar Nimra, daman Nimra ta fada masa yarinyar tana gidansu, a yanzu ya gane duk ganin da yake mata a gidan take. Yesmin ta fisgeta ta jefar da karfi kan kujera.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.