Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 72 of 227

“Hello”

“Ranka ya dade wata mata ce ta zo nemanka.... ”

Ta mamaki ya gama sauraren kiran sannan ya ce.

“Ka je ka fada mata ba zan dawo yanzu ba”

“Toh”

Mamaki ya cika shi, domin shi dai be yi da wani za a zo nemansa a gidan ba, gidan ma ba Nimra ba be taba kawo kowa a gidan ba, bw ya jin ko Daddy ya san yana zuwa gidan a yanzu balle kuma wani da be fadawa ba. Ya sake daukar wayarsa ya kira Nimra ya tambayeta ko akwai wanda take tsamanin zuwansa ko kuma ya biyo bayanta. Tana jin haka sai hankalinta ya tashi.

“Aa amman wa suka ce maka?”

“Ban tambaya ba, na ce ya fada mata ba zan dawo ba, zan tsaya daga nesa na ga ko wacece”

Nimra ta kashe wayar da sauri ta mike tsaye ta fita daga dakin da take kwance ta fito harabar gidan kamar mahaukaciya. Ta nufi gurin mai gadin tana masa tambayoyi.

“Dan Allah wacce ta zo ta fada maka wace ce ita?”

“Aa bata fada min ba”

“Dan Allah fita ka tambaya wacece ita kuma wa za a ce masa idan ya dawo”

Ba musu mai gadin ta fita ya leka waje har sai da ya hango inda Ummi ta aje motarta ya taka ya isa gurin yayi knocking din glass din motar ta bude masa idonta har ya kumbura tsabar kukan da take a motar, jiki ya mutu domin ta riga ta san mai afkuwa ta afku.

“Hajiya na kira shi yace ba yanzu zai dawo ba, amman wa za'a ce masa idan ya zo?”

“Zaka iya kiran min yarinyar da take cikin gidan nan?”

“Gaskiya ba zai yiyu ba”

“To dan Allah zaka iya ba ni aron wayarka? Saboda tawa wayar tana gida na manta”

Sai da ya dan dade yana tunani sannan ya ciro wayar ya mika mata, ta karba ta saka number Nimra, Nimra dake tsaye jikin gate tana jiran dawowar mai gadi wayarta ta fara ringing sai ta ki ta yi picking har kiran ya tsinke, sai da aka sake kira na biyu sannan ta daga.

“Hello”

“Nimra kina ina?”

Jin muryar Ummi ya haifar mata da sarawar kai, ta juya ta kalli gidan.

“Ina gurin Saloon Ummi”

“Saloon din kenan a cikin gidan wani? Yaushe kika lalata kanki Nimra? Me muka miki da zaki watsa mana kasa a ido? Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un ki fito yanzu nan ina jiranki a waje”

Kalaman da zata hada ta tari furucin Ummi sai ta rasa har Ummi ta yanke wayar, kuma ta kasa fita ta kasa komawa ta kasa yin komai sai gumi take tana hawaye kamin ya duka a gurin ta fara kuka...

©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 30

Ji ta yi kamar hanjinta za su fito a lokacin da wayarta ta sake yin ringing, wani irin rawa jikinta yake kamar mazari, sai dai ganin Number Ameer ya saka ta yi saurin dauka.

“Hello Ameer Ummi ce?”

“Wace Ummi? Na santa ne?”

“Mahaifiyarmu”

Ta sake fada cikin kuka.

“Oh Really wow i like it”

“What do you mean you like it?”

“Na kusa karaso bari na zo sai mu yi magana”

“No no no karka zo kar ta ganka tana waje tana jiran na fita”

Ya yanke wayar ba tare da ya sake ce mata komai ba, tana kokarin kiransa Mai gadin ya dawo min sai ta yi baya da sauri a zatonta Ummi ce ta shigo ciki.

“Ina take?”

“Ta wuce”

Ta juya baya tana dora hannunta a saman kai.

“Na shiga uku na lalace? Waya fada Ummi ina zuwa nan?”

“Toh Wallahi ban sani ba”

Ya amsa kamar da shi take magana, sai ta juyo ta daka matsa tsawa.

“Kai dan Allah ba da kai nake ba, ka rufe min shegen bakinka, ai duk laifinka ne”

Ya tabe baki ya koma gurin zamansa yana fadin

“Allah ya kara daman ina bakincikin abun da kuke aikatawa, zamani ya lalace yara sai fadarewa suke”

Da gudu ta shiga falon ta zauna saman kujera tana kiran wayar Ameer dake ta ringing ya ki ya daga.

“Ka daga Ameer ka daga”

Can kuma ta yanke kiran tunawa da ta yi da Ummi ta tafi, kusan tun da take a rayuwarta bata taba shiga tashin hankali irin wannan ba, bata saba yi na Ummi karya ba a lokacin da ta koyi yin karyar kuma ba ta yi zaton asirinta zai tonu ta wannan hanyar mafi muni ba. Shigowar Ameer ya saka ta mike tsaye da sauri ta nufi inda yake shi ma ya nufota.

“Ya aka yi haka ta faru?”

“Ban sani ba, wata kila wani ya fada ma mata ne, ko kuma ya kawo ta nan”

“Na so na tararda da ita da sai na yi mata bayani ko yanzu zamu tafi gidan tare zan fada mata komai”

“Wane irin bayani kuma? Ameer are you okay? Zan yi magana da ita tukuna”

Ya kama hannunta.

“Nimra ina fatar kin shiryawa wannan, daman soyayya dole akwai kalubale balle kuma irin ta mu da muka boye, amman ni I'm ever ready to marry you, ban san miyasa iyayenki suka tsane ni ba, but i trust you na san zaki iya shiga ko wane irin hali saboda ki ga soyayyarmu ta daure haka ne?”

Ta daga mishi kai.

“Good kamar yadda zan iya aikata komai akanki, and ina tunanin wannan dama ce a gareki da zaki bayyana musu wanda kike so, kuma ki fada musu cewar ba zaki auri kowa ba sai wanda zuciyarki take so, matukar suna kaunarki na tabbatar za su bar mu mu auri junanmu, kuma ki daina wannan kukan haka ba wani abun tashin hankali ba ne, zamani ya zo da an daina abubuwa da yawa, yanzu an waye ba kamar da ba ne zuwan dakin saurayi ba wani abun ba ne, kawai dai boyewar ne ina tunanin zai zama laifi a gurinsu, shi ma kuma laifinki ne domin tuntuni na yi ta neman ki ba ni damar bayyana kaina a matsayin masoyinki kika ki, i hope ba zasu ce za su raba ni da ke ba Nimra, saboda zan iya mutuwa idan iyayenki suka aikata haka, domin ni na dade da fadawa iyayena cewar ke nake so kuma sun goya min baya”

Ya rairaice mata yana ta saka mata maganganu a cikin kai kamar gaske, ita kam jikinta ya dauka kuma ta yarda har sonsa da tausayinsa sun karu a zuciyarta.

“Zan yi magana da Ummi zan fada mata gaskiya, kuma na san tana da fahimta zata fahimta amman Abiey...”

“Idan har uwa zata fahimta me zai hana uba ma fahimta matukar yana son farincikin yarsa? Ko dai ance na yi ma iyayenki wani abun da ban sani ba ne Nimra”

Ta girgiza kai.

“Aa bari na tafi”

Ta saki hannunsa ta nufi dakinsa ta dauko jakarta ta fito ta mayafinta ta saka talkaminta ta fito ta dauki wayarta dake kan kujerar falo ta sumbanci Ameer sannan ta fice. Binta yayi da kallo sai da ta fice sannan yayi murmushi.

“Now iyayenki za su ji zafin da mahaifina ya ji a lokacin da kuka yi sanadin da ya koreni, bari mu gani ke ma korarki za su yi, ko kuma za su ba ni dama na fito neman Aurenki ne? Not just them Maleek ma would feel the pain....”

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.