Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 114 of 227
“Taso ki kwanta”
Ta taso tana kuka ta bi bayansa ya san bata son mutane, kuma gidansu yanzu akwai mutane dan haka ya nufi dakinsa da kanshi ya tura kofar dakin ya bude mata. Da kai yayi mata alama da ta shiga ta kwanta, sai da ta daga kanta sama ta kalleshi sannan ta shiga, sai ta kwanta a kasa jikinta na taba gadonsa. Blanket ya dauko ya shimfida mata kan doguwar kujerar dake dakin yayi mata alama da ta koma can, sai ta tashi ta nufi gun ta kwanta ya dauko karamin bargo ya rufa mata.
“Da gaske Nimra ta mutu?”
Kallonta kawai yake ya rasa kalar amsa da zai bata, ya san ita ma tana jin kamar ba gaske ba ne, abun it's so hard to accept. Be ce mata komai ba ya nufi kofar dakin ya fice yaja mata kofar. Downstairs ya sauko yana kallon gurin da Nimra ta gi yawan zama, kitchen ya zarce kai tsaye ya kunna tap ya tara cup ya sha ruwa, sai ya ji su da daci. Ya aje cup din yana kallon harabar gidan da komai yayi tsit, da cije bakinsa ya girgiza kai idonsa suka sake cika da hawaye. Immediately ya baro kitchen ya dawo dakin ya zauna yana da Nafilar dare.
Washe gari aka yi mata sutura, aka yi mata Sallah kamar yadda addinin musulunci ya shar'anta, sannan aka dauketa zuwa gidanta na gaskiya wato final destination. Hauka ce kawai Namra da Ummi ba su ba, amman sun yi kuka har hawayen suka kafe musu. Duk dauriyar Abiey sai da ya fashe da kuka a lokacin da aka zo sakata kabarinta. Har sai da aka rike shi Maleek kuka Mahmood kuka duk wani na kusa sai da yayi kuka a lokacin da suka rufe Nimra...
______________
Allah ka jikan Mahaifin, shi ne first gawan da na fara arba da ita a rayuwata. Please include him in your prayers Allah ya lullube kabarinsa da Rahma ya yafe masa. Tabbas mutuwa akwai ciwo💔😭
[7/4, 8:48 PM] My S Line: 47
*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
“Abun is some how, amman taya aka dauki tsawon lokaci haka babu wanda ya fada maka?”
Ya juyar da fuskarsa dayan gefen yana kallon wani bangare na dabam.
“I think Daddy yana kokarin kare ni, domin ta ba shi ni kyauta, kuma ya rika ya rike ni ya so ni fiye da yadda yake son kansa, idan kuma yana son kwanciyar hankali dole ya bar magana ta kasance a rufe”
“Wata kila ita ma tana da dalili na aikata haka fa farko, kuma a yanzu ba ba zata rasa dalili da ya saka ta bayyana maka ba”
“Bata da wani dalili Humaira, kawai ina tunanin mijinta da take aure a yanzu ya nuna cewar baya so na, shiyasa ta aikata hakan ko kuma tana tsoron talauci, a yanzu kuma ban san dalilinta na bayyanawa”
“Ameer...”
Ta kirashi sai ya juyo ya kalleta.
“Ban taba ji, kuma ban taba ganin uwar da ta dauki cikin ďa wata tara ta haife shi kuma tace bata sonsa ba, ko da kuwa ďan nan ta hanyar zina aka same shi balle kai da aka haifa da hanyar sunna, kuma irin ku da suke nisa da iyayen kun fi komai shiga rai, dole akwai wani abu mai karfi da zai saka ta aikata haka, saboda ka aje duk wani abu da kake ji a zuciyarka ka fuskance ta ka tambaye dalilinta na aikata maka haka, wata kila zata baka gamsasshiyar amsa”
“Bana ma som ganin fuskarta a yanzu, bana son komawa gida, gaba daya na rasa me ke min dadi”
“I hope alakarka da Daddynka ba zata canja ba”
Ya girgiza.
“Ba zaki fahimci abun da nake ji ba Humairah, i wish bayan na mutu hakan ya faru”
“Mahaifiyarka bata kyautar da kai a gidan marayu ba, bata jefar da kai a hanya kamar yadda wasu iyayen suke ba, bata bada kai inda za ka sha wahala ba sai a inda aka nuna maka gatan da ko mahaifinka na gaske iyakar abun da zai yi kenan, please Ameer ka dubi wannan abun da idon Rahma”
“You take her side saboda mace ce yar'uwarki”
“No ina fada maka gaskiya ne, kuma ita ta fika zama abun tausayi, wata kila da zaka tambayi labarinta da zaka ji bata da laifi abun da ta aikata”
“Kalli yadda alaka ta kullu tsakanina da Nimra da ace ta kai na biye a yadda ta so na mun gudu mun yi aure yaya kenan? Ashe ma kanwata ce it hurt so bad, all this while Maleek yana kallona wani sakare saboda ya san komai”
Ya daki sitiyarin motar da karfi har sai da Humaira ta zabura.
“Calm down please ba lallai ace ya sani ba, maybe su ma ta boye musu”
“Amman Humaira ya zan kalli duniya da wannan?”
“I think zaka cigaba da zama a matsayin dan Daddy ita dai ta yi subutar baki ta fada maka gaskiya, kuma ina son ka kalli abun da budaddiyar zuciya please”
“Okay na kalli abun a yadda kike son na kalla, then what zai canja abun da ta yi? I don't even know my real father, sunansa ban sani ba ya rayuwarsa take ina yan'uwansa suke duk ban sani ba, wannan kadai ba abun bakinciki ba ne? Yanzu ne duniya zaka min dariya ashe duk abun da nake takama ba na ubana ba ne”
Ya dafe kansa.
“Na mahaifinka ne mana, shiyasa na ce ka kalli abun da budaddiyar zuciya, saboda ka fuskance ta tattauna da ita ka yi mata tambayoyi, kuma ka san yadda za ku bullowa abun saboda samun mafita, bayyana wannan abun wani abu ne na sirri da be kamata kowa ya ji ba, kuma za ku iya rufe wannan abun a tsakaninku”
Ta kunna wayar hannunta ta duba agogo.
“It getting dark ya kamata na shiga gida kar a fara nemana”
Ya gyada mata kai.
“Please keep reciting Hasbunallahu Wani'imal Wakil, aka samu sauki In Shaa Allah”
Nan ma dai kan ya gyada mata yana ta kallonta har ta fice daga motar da ke bude. Duk wani tsana da ta yi masa da kiyayyarsa da take ji a ranta sai ta ji abun ya tafi, tausayinsa ya cika mata zuciya, yadda yake rayuwa yana alfaharin da cewar Mr Bashir mahaifinsa ne ace a yanzu ba shi ne ya haife shi ba, abun dai kamar a shirin film ko littafi, domin abu ne da be cika faruwa a zahiri ba. Tsaye ta yi tana kallon motarsa har sai da ta daina hangoshi sannan ta juya ta koma cikin. Ba shi da wani gurin zuwa da ya wuce gidansu, daman idan bashi a office yana a gida ko kuma yana tare da abokansa, sai dai a yau jin yake baya kaunar kwana a gidan. Saboda haka ya nufi gidansa, fakawarsa ke da wuya a harabar gidan kiran Daddy ya shigo wayarsa, sai da yayi kamar ba zai daga ba sai kuma wata zuciyar ta hana shi kin amsa kiran Daddy.
“Hello”
“Kana ina?”
With serious voice Daddy yake tambayarsa.
“Ina gidana”
“Gidanka? Yaushe ka fara zama a gidanka?”
“Na kan zo sometimes da rana, yau kuma ina jin zan kwana a nan ne”
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.