Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 57 of 227

“Haba ya za'ayi yarinyar da muke son ta sake jiki mu fahimce ta ta fada mana danginta a maidata cikinsu zamu barta gurin Hanne ta zauna gashi ko lafiya bata da”

“Ummi ji ihun da take mana idan an kunna Plasma, ga kazanta kuma bata saba cin irin abincin mu ba, kuma Wallahi bata da hankali, ni dai gaskiya ba zan iya zama guri daya da ita ba”

Namra ta fada, ita dai yar'uwarta Nimra kanta a kasa yake domin bata son hada ido da Abiey musamman a yanzu da ya zama ita ce silar faruwar komai.

“Zan ta iya zama a dakinta, for now asibiti zan kai ta a duba lafiyarta”

“Har da kwakwalwarta a duba Ummi kar wata rana ta kashe mu muna bachi Wallahi, Nimra kin ja mana masifa Wallahi”

Abiey yayi saurin tarewa yarsa domin ya san tana cikin damuwar rashin magana da yake mata yanzu kuma suna son kara mata wani.

“Haka Allah ya kaddara stop blaming her”

Nimra ta dan dago a hankali ta kalli Abiey tana jin sanyi a ranta. Maleek dake rumgume da hannayensa yana kallonsu ya ce

“Tana Garden tana kuka”

Ummi ta kalleshi da sauri.

“Waya kaita waje?”

Ya daga mafadarsa alamar be sani ba, sannan ya karasa saukowa ya nufi hanyar da zata sada shi da bangaren mahaifinsa.

“Ni na ce Hanne ta kaita waje”

“Haba Namra”

“Madam idan yaranki basa son abu don't force them please, ba ina nufin a waulakanta yarinyar nan ba, no zai fi kyau a barta ta zauna a BQ saboda su samu sukuni”

“Dan Allah ka barta ta zauna a nan, ina son yarinyar jin ta nake kamar yata ina son na taimaki rayuwarta, tana cire min kewar abubuwa da yawa, ko ba komai ina bukatar wanda zai zauna da ni idan Namra ta fita yar'uwarta ta fita Mahmood ba shi nan ni kadai ake bari a gidan nan”

Magana ce karama amman sai da ta saka Ummi hawaye domin ita kadai ta san abun da take ji a zuciyarta, Abiey kuma ya gane yarenta, hawayenta kuma suka sosa zuciyarsa hakan ya saka shi zolayarta.

“Abokiyar zama kike so kenan?”

Ta share hawayenta tana hararashi.

“Tab ka ma isa to ka fara din ka ga yadda zan yi da kai”

Sai duk suka saka dariya, ita kuma ya fice daga falon ta nufi Garden, kuka ta samu Waira na yi sosai sai ta mika mata hannu tana mata alama da ta taso, Waira ta girgiza mata kai ta lake kafada. Ta yi mata alamar mari a hannu ta kuma yi alamar dangwarar da Hanne ta yi mata.

“Waya dake ke ki kuma?”

Ta tambaye ta da hannu sai ta nuna cikin gidan, Ummi ta kama hannunta ta jata da karfi ta taso a dolenta suka koma falon.

“Waya mareta?”

Shi ne abun da Ummi ta fara tambaya a lokacin da ta shiga falon, Nimra ta aje wayar dake hannunta.

“Babu wanda ya mareta, waya am mareta?”

“Ita ta fada min”

“Ba wanda ya mareta”

Waira ta taba Ummi ta nuna mata Hanne ta yi mata alama da dangwara ta sake nunata tana tabbatarwa da Ummi ita din ce.

“Hanne ne ta yi miki kika dangwareta?”

“Ni..... Ya ilahi”

Hanne ta nuna kanta tana tambayar Ummi kamin ta karaso gurin Waira ta nuna kanta.

“Ni na dangwareki”

Waira kamar ta san abun da ake fada sai ta daga kanta sama alamar eh, kamin ta juya ta nunawa Ummi Nimra ta yi mata alama da abinci ta kuma yi kakarin amai.

“Ni kuma me na yi?”

“Miyasa kika bata abincin da ta ci ta yi amai”

Ummi ta fada domin ita ta gane abun da Waira take nufi, sai Nimra ta saka dariya ta kama kunneta ta hade hannayenta tana bawa Waira hakuri.

“To yi hakuri, lallai Ummi kin iya maganar kurame”

Ummi ta yi murmushi sannan ta kalli Hanne ta ce.

“Ke ma ki bata hakuri kuma kar hannunki ya sake kawai a jikinta”

Ita ma ta yi yadda Nimra ta yi tana dariya, Ummi ta shiga da ita dakin da aka ajeta ta taya ta cire kayanta domin aman ya taba wani bangare na rigar ta dauko tawul ta daura mata, ta shiga bandaki ta hada mata ruwan wanka ta saka a bandakin ta janyo mata kofa ta fice daga dakin ba tare da ta rufe kofar ba ta shiga dakin Maleek. Abun ka da wanda be son wanka haka Waira ta fara jan kofar bandakin tana son budewa ta fito abu ya gagara daker ta samu ta lankwasa kofar abun ya bude sannan ya fito ganin kofa bude ta fice daga dakin daga ita sai tawul din da take daure ta fara talawa tana dan leke lake a hankali jin motsi a bayanta ya saka ta juyo ta nufi dakin Maleek dake gaban nata, shi ma kofarsa a bude take ta nufi dakin ne ba dan ta san cewa na Maleek ba ne sai dan motsin da ta ji a ciki tana son gani idan Ummi ce a ciki. Lekawa ta fara yi sai ta hango Ummi duke gurin gadon Maleek tana gyara masa, domin ita kadai ya yarda ta gyara masa gadonsa shi ma dan tana kokarin kiyaye abubuwan da baya so na, ba kamar kanensa da idan za su shiga dakin wani lokacin har jan baki sai sun shafa ba, idan ma bata gyara masa ba ya kan gyara abunsa time to time ya fin natsuwa da ya gyara fiye da wani ya gyara masa ma. Ba Ummi kadai Waira ta gani ba har da wata farar mace wacce ta fi Ummi tsawo sosai gashin kanta a yamutse ga manyan idanuwa kamar kwai, farcenta har ya kusan tsawon yatsan Waira, bata da kafafuwa sai doguwar bakar rigar da ke ja mata a kasa bakinta na fitar da hayaki tana goye da yaro sai jijjiga shi take tana hararar Ummi. Da sauri Waira ta nuna inda matar take tsaye ta yi kara Ummi ta kalleta da sauri ta juya a firgice ta kalli inda Waira take nunawa bata ga komai ba sai ta fito dakin da gudu, matar na ganin Waira ta ganta sai ta fitar mata da hakora ta firrrr kamar kamar tsuntsuwa ta dire ta Window dakin dake bude, Waira ta kwala kara ta yi baya da sauri Ummi na kokarin rikota sai ga jini ya fara fitowa a idonta..

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”

Ummi ta rika ta da sauri ta rumgume tana ihu.

“Hanne Namra Nimra waye a kusa”

Namra dake dakinta ta riga iso gurin tana ganin jini a idon Waira taja waya ita ma ta fara nata ihun.

“Innalillahi mun shiga uku”

Fitowar Mahmood a dakinsa dake bachi ta yi daidai da haurowar Nimra da Hanne. Karbarta yayi a hannun Ummi tana kiran sunanta.

“Waira... Waira...”

Ta kalleshi daman hankalinta be gushe ba, tsorata kawai ta yi sai kuma hawayen jinin dake fitar mata a ido.

“Mi ya same?”

Ummi ta fada masa iya abun da ya faru da kuma abun da take tunanin ko Waira ta ga wani abun ne, Mahmood ya sake ta, ya shiga dakin yana dubawa da dan tsoro ko zai ga wani abu be ga komai ba.

“Dan Allah Hanne da Nimra a saka mata kaya zan je na shirya na kaita asibiti yanzu nan”

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.