Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 170 of 227
Ta mike tsaye tana kuka, Ummi ma kukan take tana jin kamar tace mata kar ta tafi sai dai ta san tafiyarta zai fi zamanta a gidan alheri, idan ma ta roke ta ta zauna gidan Ameer ya aureta Maleek zai yi ta kallonta da ciwon zuciya ne Waira ta fice daga dakin ta nufo dakinta, ga mamakinta sai ta samu Ameer a tsaye yana jiran shigowarta. Tana kallonsa sai ya sauke idonsa kasa kamar mai tsoronta, murya can kasa kasa ya ce
“Na kasa natsuwa da jinin da na gani a idonki, ciwo kika ji? Ko kuma wani abun ne?”
Bata amsa masa ta taka daga bakin kofar da take tsaye ta isa inda yake tana kallonsa.
“Ameer ka cire ni a zuciyarka, ka manta da an taba halittar wata mace kamar ni a duniyarka, ka goge duk wani hoto rayuwata da idonka suka dauka, ka karya alkalamin dake zana maka shirme akaina, ka yage littafin layin kaddarar dabam tawa dabam, babu ta inda muka dace da juna, ko da ma mun dace aure ba zai taba wanzuwa a tsakaninmu ba”
“It's because of abun da Maleek ya fada miki?”
“Aa saboda ciwon da kake sakawa Ummi, da kuma gabar da kake yi da dan'uwanka saboda ni, sanadinka Ummi ta canja min, ta zubar da hawaye a kaina, kuma take tsorona, idan ka shiga rayuwar mutum lalata kake yi Ameer”
Kamar ba shi ba, haka ta risina kasa yana kallonta.
“Zan canja Waira zan zama duk yadda kike son na zama, karki duba yadda soyayya ta maida wani sakare a gabanki ki yi amfani da wannan ki cutar da ni, ban taba so ba sai kanki saboda haka ban san zafinsa da haukarsa sai a yanzu, ban san haka yake maida mutum ba sai a yanzu”
“Yanzu kana iya jin yadda Nimra ta ji?”
Ya mike tsaye.
“Sunanta kawai idan kika kira, ji nake kamar hukunta ni kike yi, karki duba abun da na yi dan Allah Waira, abun da ya wuce mu bar shi a wuce”
“Shiyasa zan bar maka gidan, ba zaka sake ganina ba, and it means forever”
“Ba sai kin tafi ba, zan iya bar miki gidan na yi nisa da inda zaki gan ni, amman please ki zauna a nan din, karki tafi saboda ni, idan baki so ne ba laifi ba ne, zaki iya auren Maleek, ki musulunta ta hannuna ko da wannan sai na karu”
Ya kauce daga gabanta ya fice daga dakin yana jin zuciyarsa kamar zata rabe biyu, be taba jinsa a irin wannan yanayi ba, sai a yau shi kam da ma zai mutu ya hutu, yaushe soyayyar Waira ta kama shi amman sai azabtuwa yake da abun da be yi zato ba, yaushe ya zurfafa a kaunar ko dan be taba yi ba sai a yanzu, ko kuma saboda yana tarayyar kaunarta da wani ne? Ya sauko kasa yana jinsa kamar ba shi ba, kasar ma takawa kawai yake yana tafiya amman ji yake kamar ba duniya yake ba. Yana isa gurin motarsa ya jingina jikin motar ya kife kansa ya rasa abun da ke masa dadi a duniyar nan. Ya bude motar ya shiga yayi mata key baya yaja motar ya tsaya saitin da zai iya hango window Waira ya faka motar ya bude ya fito ta jingina yana kallonta, kallon windows dinta ma dadi yake masa, a haka zai ji sanyi ko da kuwa be shiga ya ganta ba. He spends hours yana kallon gurin yana jin kamar ta leko ta ce masa magana. Ta inda be yi zato ba ya ganta tsaye a bakin kofar falon tana saukowa ta nufo inda yake, da sauri ya mike tsaye daidai yana kallonta zuciyarsa sai halbawa take, da ace wani ne ya fada masa cewar zai hadu da yarinya kamar Waira ya haukace a sonta ba zai yarda, ko da kuwa za a buga kasa a kafa masa haka.
“Akwai abun da kike so ne?”
Ya tambaya yana jin kamar yaje a gushe ya rumgume ta. Ta tsaya daidai shi ta daga kai ta kalleshi.
“Kai ka wayar min da kai akan addinin musulumci, ka fada min abubuwa da yawa da ban tambaya ba, ka sanar da abubuwan da ban sani ba, na fahimci addinin saboda kai kuma na ji ina kaunarsa duk a ta dalilinka, ina son na musulunta, musulunci kadai abun da zan tafi da shi, da zan zo ban zo da komai ba, dan haka ba zan dauki komai ba, zan tafi daga ni sai abun da na koya... Ya ake shiga musuluncin ina son na shiga, na yi rayuwa mai tsafta kamar ku, ka karu da abun da ka koyar, kuma ka cika burinka kamar yadda ka roko...”
Ya hade yawu da karfi, farinciki da kishiyarsa suka ziyarce a lokaci daya.
[8/3, 9:46 PM] My S Line: 69
Daga kwance da Ummi take ta dago ta kalli Abiey daya shigo dakin sanye da tufafin bachi, abun ka da mace mai kula da miji sai ta yaye zanen da ta rufa da shi ta tashi zaune tana kallonsa har ya iso inda take ya zauna bakin gadon yana kallonta.
“Madam yau kuma a nan zaki kwana?”
Ta sauke kai kasa ba tare da tace masa komai ba.
“Tun da ciwon nan ya bayyana a garemu, sai duk kika canja, abubuwa da yawa wadanda ba halayyarki ba kika ara kika yafa, wadanda suke naki kuma kika zubar, lokacin da ya kamata ace kina cikin farinciki da jindadi, sai kika mayarda da su na bakinciki da damuwa, alhalin ni yanzu ban ga wani abun damuwa a tare da ke ba”
“Haka dai kake gani, amman har yanzu ban gama cika burina ba, balle na zaba zama cikin farinciki, ko kuma damuwa ta zabi rabuwa da ni”
“Toh me ya rage? Ina ce yanzu kina tare da Ameer, iyayen Deen sun san komai, bayan shi akwai wani abun da kika aikata kuma da kike jiran neman yafiyar wani?”
“Ranka ya dade yanzu ba yafiyar wani nake nema ba, hadin kan ƴaƴa nake da bukata, yadda za tafi na bar Ameer yana rashin jituwa da yan'uwansa ne damuwata, yadda kake nuna masa tsana da kiyayya ne matsala ta, ni na rike naka yayan da zuciya daya, na kaunace na nuna musu so, amman kai ka kasa nunawa Ameer nawa kwaya daya tal, har ya gama fahimtar baka sonshi, gashi duk wasu kalamai da zan yi amfani da su na sauya tunaninsa sun kare, kuzarina ya tafi, ina tausayin rayuwar Ameer idan bana raye”
Abiey ya sauke ajiyar zuciya yana kallonta.
“Na taba furta cewar bana son Ameer? Kamin yanzu ban fada miki ki yi iya yadda zaki yi Ameer ya zauna a hannunki ba, ni kuma zan goya miki baya, amman kika zabi abun da kika zaba? Zaman a gidan nan na taba hana shi shiga wani bangare na gidan ko kuma na taba cewa ya fice min daga gida? Zahra ki rika sara kina duba bakin gatari, kar son Ameer ya rufe miki ki kasa ganin gaskiya a inda take marararta”
“Idan har son wani zai rufe min ido na kasa ganin komai, to sonka ne farkon abun da ya fara cutar da ni, kuma ya cutar da Ameer, a duk lokacin da zan yi maganar Ameer ko na nemi ganinsa ina ganin kiyayyar haka a idonka, ka sha canja mu'alama da ni saboda kawai na nuna ina son ganin ďana, ka kasa daina kiyayya da wanda ya manta da ya taba wanzuwa a duniya, ka kasa nuna min soyayyar da kake takamar kana yi min tun kurciya har tsufa, saboda ka kasa tirsasa zuciyarka ka fi karfinta ta cusa mata son ďana jinina”
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.