Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 195 of 227

*** *** ***

“Me yasa kika dage sai kin raba ni da shi? Me na yi miki? Akan wane dalili zaki kawo shi inda za a raba mu?”

Nuwaira ta daga kai ta kalli matar dake ta masifa tana kuka.

“Wace ce ke?”

“Matarsa ce ni, idan kika raba ni da shi yaransa ki yi yaya da su?”

Ta nuna mata yaran biyu dake tsaye gefe daya dayan kuma yana hannunta.

“Tun da kika shigo rayuwarsa kika sauya komai, da na shaka masa liyi da mata, amman kina zuwa kika fara kawo min matsala yanzu kuma kika kokarin raba ni da shi, bayan kin nisanta ni da bana samun lokacinsa kamar da, ni ma musulma ce be kamata ki yi min haka ba, ba ki san tsawon lokaci da na dauka a tare da shi ba, duk yadda zan yi na rabaku na yi amman kin zama karfen kafa, ni ce nake miki siffarsa ina taba ki, amman haka be yi tasiri akanki ba, na fito miki a fili ba sau daya ba amman ba ki kyale min mijina ba”

“Ni ban miki komai ba...”

A take matar ta jefar da ďanta ta yi cikin Nuwaira ta shake wuyanta da karfi.

“Ki yi min, ki yi min, ki yi min”

Shi ne abun da take fada ya shake Nuwaira da dukannin karfinta, Nuwaira sai fisge-fisge take tana neman ceto numfashinta na kokarin daukewa. Daker ta iya fisgo kanta ta farka daga bachin sai ta tashi zaune da sauri tana hakki ta rike wuyanta. Maleek da har lokacin karatu yake ya haska fuskarta.

“Lafiya?”

“Wata mata na gani a mafarki ta makure ni sai fada take da ni, wai na kawo ta inda za a raba ku, matar da nake gani dakinka ce kuma ta ce ita matarka ce”

And now he's smile ya bar inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna.

“Matata kuma? How are you okay”

Nuwaira na shafa wuyanta ta ce.

“Baka mafarkin wata mata? Ni na fada maka ina ganin mace a dakinka da har da yayanta ma, ita ce ta fara sumar da ni a lokacin da na fara ganinta a dakinka har ka mareni lokacin da na tsorata na rike ka”

“Shiyasa kike tambayar ina da mata? Ba ni da mata ni ban taba cewa ina son kowa ba, balle kuma aure”

“Ni ma na yi mamakin da bata fitowa ta zauna a tare da mu, amman ban gane aljana ce ba sai yanzu, saboda ta fada min har kuna da yaya baka mafarkinta ko ganinta kai?”

“Sometimes amman ina daukar duk mafarki ne ba gaske ba, kuma da can nake yi daga baya na daina”

“Ta makoreni sosai”

Tana maganar tana kuka, da fitilar wayarsa yayi amfani ya haska wuyanta, sai ga shakin yatsu gurin ya mata ja alamar jini ya kwanta.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Subhanallahi”

Fada cike da mamaki, ayatul kursiyu ya karanta ya tofa mata a wuyan tare kula'uzai.

“Nuwaira dole ki dage da addu'a, kuma ki yi kokarin raba kanki da tsafin da yake cikin jikinki saboda, so that ki samu full kariya daga Allah, wata kila idan kika rabu da tsafin ba za su taba iya sarrafa ki ba, saboda karfin addu'a, and we have to leave this place by tomorrow hankali be kwanta ba, na kasa samu bachi...”

Ta gyada kai tana jin zafin wuyan nata har lokacin, sai dai kuma bata jin zata iya barin garin.
[8/10, 6:44 PM] 🦋-🦋: 76

AMEER POV.

Ta tunani da kuma fargaba ya fito bayan ya faka motarsa a harabar gidan Abiey. Yadda ya ga Abiey yana safa da marwa waya a kunnesa ya dan daga hankalinsa domin yanayin Abiey yana nuna ba lafiya ba, kuma shi be taba ganinsa a harabar gidan ba tun da ya saka kafarsa a gidan ma sai yau. Ameer yayi kamar ya wuce bangaren Ummi sai kuma ya ji be natsu da hakan ba, dole ya nufi gurin da Abiey yake tsaye ya saka hannayensa biyu aljihu ya soke kai kasa da fari ya yi zaton ko ciwon Ummi ne ya zafafa ya saka Abiey a wannan halin, sai dai sauraren wayar da Abiey yake abubuwan da ya ji yana furta ya nuna ba akan Ummi ba ne, a take gabansa ya soma faduwa. Tsayawa yayi a gurin har sai da Abiey ya gama wayar sannan ya matsa kusa da shi.

“Lafiya kuwa na ji kana fada”

“Ba dole na yi fada ba, imagine saboda a sama musu tsaro na saka police suka raka su tun daga nan, kuma bayan sun isa can aka kara musu wasu biyu, wai yanzu dayan yake fada min su sun juyo suna cikin Katsina Maleek kuma yana can garin ya dage sai ya shiga ciki su kuma ba za su iya shiga ba saboda haka suka dawo, ji min wata maganar banza ba za su iya shiga ba suka bar min yaro ya shiga shi? Kuma saboda ya raina min hankali sai fada min yake wai garin da mutanen garin suna da hatsari ba sa son baki, na fada masa idan wani abu ya sami ďana sai na yi shari'a da su, kuma su koma su taho min da ďana, shiyasa tun jiya ina ta kiran wayarsa bata shiga, Ummi ma tace ta kira shi ya fi a kirga wayar be shiga ba”

Ameer be san lokacin da kai hannu ya dafe kirjinsa ba, saboda bugun zuciyarsa da karu daman tun da ya farka yake jin ba lafiya ba, gashi kuma yanzu Abiey ya fada masa abun da zai hana shi bachi.

“Allah yasa ba wani abu ya same Waira ba”

“Waira ko Maleek?”

Abiey ya tambaya yana mamakin jin yadda ya bar dan'uwansa yake fargabar kar wani abu ya same wata.

“Dukansu Allah yasa suna cikin aminci”

“Ameen, karka fadawa Ummi wannan maganar domin kasan bata da lafiya be kamata ta ji wannan abun tashin hankalin a yanzu ba, karka kuskura nuna mata komai”

Da kai kawai Ameer ya iya amsawa Abiey ya juya ya nufi hanyar shiga part din Ummi, Abiey kuma ya nufi bangarensa yana kara kiran wata number. Sai da Ameer ya isa kofar falon Ummi ya kai hannunsa ya taba kofar sai ya kasa murdawa ya tura ya shiga, saboda jikinsa a mace yake, damuwar dake zuciyarsa kuma ta nuna a fuskarsa, Ummi zata iya tambayarsa be san yadda zai kare kansa ba. Fasa shiga falon yayi ya juya ya nufi motarsa kamin ya isa ya ciro wayarsa ya gwada kiran number Maleek amman bata shiga sai yankewa kiran yake. Kamar wanda ke shirin rasa rai haka ya bude motar ya shiga gabansa na tsananta faduwa zazzabi na neman rufe shi.

Daker da sudin goshi ya samu kuzarin murza key motar yayi reverse ya fita daga gidan, be yi nisa ba ya ji kamar ba zai iya tukin ba sai ya faka gefen titi ya kifa kansa a sitiyarin motar kalaman da Nuwaira ta fada masa kawai yake tunawa, yawan nanata cewar idan suka koma a garin kasheta za ayi ya tsaya masa a rai. Sai a yanzu yake jin ina ma shi ya raka ta ba Maleek ba? Me yasa da Abiey ya ce ya rakata ya musa masa be amsa ba..? Shigowar kiran Humairah ne ya saka shi dagowa da sauri ya kalli wayar with hoping Maleek ne ya kira ganin sunan Humairah ya saka shi rufe ido ya sauke ajiyar zuciya ya busar da iskar bakinsa.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.