Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 215 of 227

“Tun yaushe kake nan?”

“Tun jiya, na yi missing dinki ne sosai Ummi ina son ganinki”

Murmushi ya bayyana a fuskarta.

“Kullum sai na yi maganar ka, ina yawan fada ma Abiey ya kula min da kai ko bayan raina”

Ya kwanto ya rungume yana magana kamar rada

“Ba zaki mutu yanzu ba Ummi sai kin ga yayanmu da jikokina ma”

Ta yi murmushi.

“Haka Abiey da Maleek suke fada, nima zan so haka idan Allah ya ara mana time, sai dai ban ga wani kokari da kuke akan haka ba”

“Muna yi Ummi, na ma zo miki da albishir amman ba zan fada ba sai gobe ya kamata ki koma ki kwanta yanzu”

“Na yi bachin enough kuma na farka na ga abun da nake ta muradin gani a kusa da ni da na”

Tana maganar tana kara rike shi da dayan hannunta...

“Ban samu enough time na kula da kai yadda ya kamata ba, shiyasa kullum ina tunanin ko a wane hali kake yanzu? Gashi ciwo ya kwantar da ni na fadawa Abiey na fi son mutuwa a gida cikin family na amman ya ki saurarena”

“Haba Ummi kar wannan ya dame ki you have done enough, and yanzu time dina ne da zan iya idan ma kina jin ba ki yi enough ba idan kika samu lafiya sai ki yi”

“Allah ya nufa”

“Fada min albishir din minene?”

“Albishir din da zan miki zan fada miki cewar ina son na yi aure soon very soon”

Ummi ta kalleshi da sauri da mamaki da kuma jindadi marar misaltuwa.

“Da gaske Ameer?”

“Da gaske Ummi ai ban taba miki karya ba, kuma ba zan fara a yanzu ba”

“Oh ya Allah na, yaushe wace mai sa'arce haka?”

Ya shafa kansa yana murmushi.

“So Ummi kina tunanin idan wata ta same ni a yanzu ita mai sa'arce?”

“Sosai kai fa dan Abiey ne, dan Mr Bashir dan Deen kuma dan mamansa Zahra”

Still murmushin yake yana tuna makamancin wannan furucin da Humairah ta taba yi masa.

“Na san surukata ba zata wuce Nuwaira ba”

“No Ummi ba ita ba ce, Nuwaira tana da wanda take so, and idan muna son mutane dole ne mu so farincikinsu”

“Wa take so? Fada kuka yi please don't break her heart”

“I didn't ita ta yi breaking heart dina, ko ba ita ba ba zan sake breaking heart din wasu ba balle kuma ita da take karkashin ikon uwata”

“What happen?”

“Babu kawai dai na fahimci bata ra'ayi kin san shi so wani abu ne da yake gina kansa a zuciyar bawa, tana so zan iya fadar haka domin muna da kyakkyawar fahimta da ita, sai dai ba irin so na aureba kamar yadda ta fada, kuma na fahimce ta na mata uzuri”

Ummi ta ji wani iri a zuciyarta tausayinta danta ya kamata, sai dai kuma ya san bata isa ta saka Nuwaira son Ameer a dole ba kamar yadda bata isa ta cire wanda ke zuciyarta ba, ko ba a fada mata ba ta san ba zai wuce Maleek ba, domin Ummi ta ga irin kukan da ta sha lokacin da ta san da Maleek za a tafi, and duk gaisawar da zata yi da Ummi idan ta tambaye Ummi yaushe zata dawo sai ta ce Ya Maleek yaushe zaka dawo, shi kansa Maleek din tana lura da irin yadda yanayinsa yake canjawa idan yana video call da ita a gaban Ummi.

“Ameer dan Allah kar wannan ya saka ka a damuwa, komai nufi ne na Allah kuma so da yawa mukan so abu ya zama ba alheri ba ne a garemu, wani lokacin kuma sai mu ki abu ya zama alheri a garemu”

“Yeah shiyasa na daga mata kafa ai, a yanzu dai ina nan ina ta addu'a Allah ya yaye min duk wani abu da nake ji a zuciyata akan son Nuwaira”

“Ni ma zan taya ka da addu'a, amman kuma a cikin wannan halin kake zancen yin aure wa zaka aura?”

“Ban gama yanke hukunci ba, domin a yanzu bana jin sonta a raina kamar yadda nake jin Nuwaira, bana son na aureta na cutar da ita, wata kila kuma zan iya koya har na fara, ina jin zan iya zama da ita na bata kulawar da ya kamata amman ba zan ji sonta kamar Nuwaira ba, sai dai idan har ta tabbata abun da Hajiya ta fada min cewar ita din tana sona sosai kuma a haka take kokarin ganin na samu abun da nake so, ni kuma ba zan bari zuciyarta ta karaya ba”

“Humairah ce?”

“Ita ce Ummi, Hajiya ta nuna min tana son na aureta tun kamin Nuwaira ta amsa cewar bata so na, Daddy ma shi kuma saboda alakar dake tsakaninki da su ta yi karfi, i hope idan har abun da nake hasashe ya kasance zaki yarda da ita”

“Ameer ni ai ko yar tsana zaka kawo min matukar kana kaunarta ni ma ina sonta, amman karka cilastawa kanka sonta karka tirsasa kanka sonta ka bari son ya shiga zuciyarka da kansa”

Ya amsa mata da kai. Kwatantawa yayi da lokacin sallah sannan ya fita daga dakin, duk yadda Ummi ta so ya je gidan Dr Zainab ya zauna sai ya ki, shi dai ya fi ra'ayin ya zauna gidan mahaifinsa, ya fita daga asibitin texi ya dauka zuwa cath sai dai kamin ya isa gari ya fara haske kasancewar tafiya ce mai tazara daga inda gidan yake zuwa asibitin da Ummi take kwance.

Two Weeks Ameer yayi tare da Ummi within days din nan babu ranar da baya waya da Humairah, da safe kamin ta tafi school zata yi waya da shi da dare ma idan zai kwanta sai ya kira ta, duk wani attention da take bukata yana bata not because of yana son ya so ta sai dan yana da bukatar duk wani abu da zai dauke masa hankali daga Nuwaira for now kwanciyar hankali yake bukata kamin yayi tunanin abun da ya kamata yayi next. Two days da zuwan Abiey tare da Namra da Mahmood har ma da Maleek dukansu a gidan Dr Zainab suka sauka domin gida ne a gurinsu ko a lokacin da take aiki balle kuma yanzu da yayanta ne suke aiki nan bayan ita ta yi retired. After two days da zuwansu ya shirya ya koma gida Nigeria. Sanin yadda Humairah take daukin ganinsa da yadda ta kwallafa rai na cewar sai ta tafi airport ta tarbe shi ya saka tun kamin ya isa ya fadawa direban gidansu lokacin da zai je ya dauke ta ya kaita airport din bayan ya sanar da ita lokacin da za su sauka. Dan haka ta shirya da wuri ba shiri kawai ta yi ba har da shirya masa abincin da ta san zai iya ci ta gyara dakinsa kamar wata mai aure da mijinta zai dawo. Misalin karfe daya jirginsu ya sauka Lagos, daga Lagos ya shiga wani jirgin zuwa Abuja. Tun kamin ya karasa fitowa Airport din ya hangota a gurin da aka tanada domin aje motoci, tana tsaye jikin motar tana ta rabon ido, murmushi ne ya kawata fuskarsa sai a yanzu yake jin marmarinta har ganin yayi kamar ta kara kyau saboda yar ramar da ta yi. Tana hangoshi ta doso inda yake da saurinta shi ma ya kara hanzari ya iso inda take sai ta yi tsaye tana kallonsa da wani irin dauki da murmushi a kumatunta.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.