Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 200 of 227
“Kamar na sanki”
Yayi maganar kamar ba shi yayi ba, domin be kalleta ba kuma be fasa game din ba. Dan juyowa ta yi ta kalleshi
“Maybe”
Sai a lokacin ya kalleta daman shi be iya munafurci ko shan mur ba, he's straight forward yana da wayayya da kowa even if ace yau kuka fara haduwa, balle kuma ita da jikinsa ke bata ya taba ganinta ko saninta.
“A ina?”
“I don't know, ko Maybe restaurant na yi siyar da abinci a can before”
Ya sake dubanta da kyau from head to toe be ga ta yi masa kama da wadda ke siyar da abinci ba.
“Wasa kike min?”
Ta yi dariya.
“Baka yarda ba?”
“Babu wanda zai yarda ai”
“Haka mutane suke cewa idan na fada, ban san me yasa ba”
“Yanayinki be bada haka ba”
“Abun ba daga yanayi ba ne, amman ba zan maka karya a farkon ganinka da ni ba”
Ya dan tabe baki feeling comfortable with her.
“Ba zan iya shaidar baki ba”
“Ni ba bakuwa ba ce, na taba zuwa gidan nan sai ko idan ka manta ko kuma baka nan”
“Na miki kama da wanda kika taba gani? And when kika taba zuwa gidan nan don't lie”
Bata san lokacin da murmushi ya subuce mata ba
“Da girma zan yi karya? Idan baka yarda ba ka tambayi Ummi, ita ta gayyatoni a gidan nan ma”
“How are you? Kin girma ki fadi karya ne? Karki cece ni da innocent face din nan, ni at first ma na dauka ko wata sabuwar budurwa Ameer ya kawo mana”
“Kai Ameer a yanzu ai be jin yaren kowa sai na Nuwaira, ni kuma yanzu I'm not ready na fada son wanda be shirya so na ba, ita kanta Nuwaira na fada masa ba zai same ta da sauki ba idan ma ya samu”
“Why? Ba ki masa fatan samunta kishi kike?”
“Why would I be jealous? No I'm not ni ba budurwarsa ba ce, just his cousin”
“Don't you have feelings for him?”
Wannan karon Mahmood har da kanne ido daya yake yana tambayarta sai ta yi murmushi ta girgiza kai.
“Da alama dai kai ne mararjin magana gida nan”
Ya mike tsaye yana murmushi.
“Na bar miki falon ma karki ce na cika ki da surutu”
Humairah dai ban da murmushi babu abun da take ta bishi da kallo har ya fice, sannan ta samu damar baza idonta a falon tana karewa komai na cikin falon kallo, tana jin motsin daukowar mutum ta yi saurin yin kasa da kanta.
“Sannu Humairah an barki babu ko ruwa, Wai shi nake sake kira ko zai daga”
Jin muryar Ummi ya saka ta dago ta dubeta Ummi da rama da ciwo ke kara bayyana a jikinta.
“Hello.. Ameer...”
“Ba Ameer ba ne, Ameer din yayi accident ga mu a hanyar zuwa asibiti yanzu”
“Ameer kuma?”
Ummi ta sauke wayar daga kunnenta ta duba line da ta kira sannan ta mayar da wayar.
“Ameer ko dai Maleek?”
“Toh ban san sunan shi ba mai wannan wayar dai, ya samu hatsari jaction din Hird da ake bada hannu”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Ameer yayi hatsari, Innalillahi Ameer”
Humairah da tun da Ummi take wayar hankalinta ya tashi ta nufo Ummi da sauri ta rike ta, sai kuma ta sake ta ta nufi kofar fita falon da sauri ko zata samu ganin Mahmood da ya fita ba jimawa. Bata ganshi ba ta dawo da sauri a daidai lokacin ne Namra ta sauko kamakon kukan da Ummi take tana tambayar me yake faruwa.
“Ameer yayi accident kar ďana ya mutu please janyo mota ki kai ni gurinsa yi sauri Namra, ďa”
“Waya fada miki wannan maganar Ummi kina cikin wannan hali?”
Ta rika Ummi tana kallon Humairah dake girgiza kai alamar ba ita ba ce.
“Ita ta kira waya sai aka dauka aka fada mata”
Namra ta saki Ummi ta nufi bangaren Abiey da gudu. Duk yadda Abiey ya so Ummi ta zauna a gida, shi da Mahmood su tafi asibiti bata yarda ba, ganin take kamar ma ya mutu ne gaba daya, ko kuma zai mutu idan bata kusa da shi. Abiey ya karbi wayarta ya sake kiran number Ameer din police din da suka yi jagorancin kai shi asibiti suka amsa wayar suka fada masa asibitin da suke. Ummi gaba daya hankalinta a tashe yake son kawai take ta ga Ameer a dole tare da ita suka je asibitin. Ko da suka isa asbitin har likitoci na masa dressing guraren da ya samu rauni, kirjinsa sai kafarsa sai kuma gefen kafadarsa. Sai dai ba abar Ummi ta ganshi ba sai da aka gama masa komai aka ware masa dakinsa sannan Ummi ta shiga tare da Namra da Humairah Mahmood da Abiey. Tana ganinsa ta isa gurinsa da sauri ta kama hannunsa ta rike tana ta kuka.
“Haba Ameer miye haka? Police sun fada mana gudu kake yi sosai ana daga maka hannu ka tsaya amman baka yi ba har ka bugu wasu motocin? So kake ka kashe kanka? Saboda me Ameer”
Cikin wani yanayi na rashin lafiya da azababen ciwon kai Ameer ya kalli Ummi yana murmushin karfin hali ya ce.
“Ba haka ba ne, jikina ne yayi nauyi burki kuma ya cige”
“Gudu yake sosai ni ma dazun har tsoro ya ba ni, baya duba kowa idan hankalinsa ko ransa ya bace”
Humairah ta fada tana share hawayenta ganin babu ko riga a jikinsa sai bandeji. Abiey ya ce.
“Rayuwa guda ce dai, kuma yanzu girma kake yi ya kamata ka rage wasu abubuwan ko dan mahaifiyarka da ka ga yadda ta tashi hankalinta a yanzu nan muma yadda hankalinmu ya tashi da baka aikata haka ba, Alhaji Bashir ma yanzu na kira na fada masa da sauki amman hankalinsa duk ya tashi, kana da mutane masu son rayuwarka ya kamata ka tausaya musu ka kula da kanka”
“Zan kiyaye gaba Abiey i promise”
Ya fada sannan ya kalli mahaifiyarsa da har lokacin hawaye take yayi murmushi.
“Ummi I'm fine kin gani, dan Allah ki daina kuka”
“Ka yi alkawari ba zaka sake irin wannan abun ba? Idan ma kashe kanka kake son yi ka bari sai na mutu, amman a yanzu babu abun da nake bukata sai rayuwarka”
“Hakan ba zai sake faruwa ba Ummi na miki alkawari”
Namra ta masa hannu ya amsa Mahmood ma yayi masa kamin ya amsa Mr Bashir ya shigo dakin hankali tashe baya ganin kowa sai Ameer Mommy tana bayansa ita kan sai hawaye take kasancewarta mace bata iya rike kuka ko damuwa. Abiey na gama fadawa Mr Bashir abun da police din suka fada masa ya zabura ya rufe Ameer da fada kamar zai doke shi har sai da Ummi ta shiga tsakiya ta tare Ameer.
“Ni ma na masa fada, ai that's enough”
“No it's not enough duk wani iskanci da yake ina jurewa ina dauka amman ban da wasa da rayuwa, idan kuma ka ce haka zaka yi to sai mu saka kafar wando daya da shi”
“Daddy I'm sorry it wasn't intentionally”
“Na dai fada maka”
Daddy ya fice a fusace, Abiey ma fita yayi domin ya san Ummi ba zata yarda ta bishi su tafi gida a yanzu ba. After like 5 minutes Doctor ya shigo ya bukaci kowa ya fita a bar Ameer shi kadai ya huta suka saka masa drip tare da magani sannan suka fice within seconds bachi yayi gaba da shi.
[8/12, 8:57 PM] 🦋-🦋: 78
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.