Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 3 of 227

Ya dauko wani box ya bude ya saka sarewar sannan ya cire tufafin jikinsa ya jefawa wata na'urar dake rike kaya ta saka su a gurin da aka tanada domin zuba kaya masu datti, even though daga tufafinsa har jikinsa babu inda yake da datti domin tsananin tsabtar Ameer baya yarda ko kura ta raba kusa da shi balle kuma dauda. Bedroom dinsa ya dawo ya shiga bathroom wani kalar kamshi mai dadi ne ya fara tashi a lokacin da ya soma murza shower gel din da yake wanka da shi, a tsanake ya gama ya fito ya sake komawa Boutique dinsa dake cikin dakin, ya shafa mai a jikinsa sannan turare ya raka masa baya, ya dauko kananan kaya ya saka, ya fito daga dakin yana wani irin kamshi kai ka rantse daga cikin ruwan turare ya fito.

Kofar da zata sadashi da bangaren mahaifinsa ya nufa, tun kam ya isa kamshin turarensa ya sanar da Momy da Daddynsa cewar gashi nan isowa. Dukan kanensa suna zaune a dinning din suna cin abinci tare da iyayensa, da sauri Zeezee ta rufe gashin kanta, gudun kar ganin gashinta ya hana shi cin abinci domin tsananin tsabtar da yake da ita ta saka masa kyama da tsandar abubuwa da dama ciki kuwa har da gashin mace.

Kujerarsa yaja ya zauna ya kalli mahaifinsa dake kallonsa da irin duba na mai laifi. Fadada fuskarsa da murmushi shi ne abun da ya fara yi sannan ya dauki plate ya soma zubawa kansa abinci.

“Miyasa ka kori ma'aikatanka?”

Ya dan tsaya daga zuba abincin da yake, ya kalli Daddy.

“I told them kar wanda ya sake shigo min office da kazanta, shi dayan be ji ba na lura rigarsa ta jiya ce ya maimaita kuma be wanke ta ba, dayan kuma karni yake Daddyn kasan yadda nake jin warin mutane, bana son kazanta ko kadan kuma bana son na ji mutum ba kamshi”

Daddy ya girgiza kai cikin damuwa.

“Amman Ameer wannan be kai ace ka sallame su daga aiki ba? Kuma bayan sallamar ka ce ba za a ba su salary su na wannan watan ba, secondly an fada min jiya ka kade wani mutum da mota”

“Shi ma wasa yake da brayuwarsa, overtaking yayi, ya ba ni haushi sosai shiyasa na yi masa haka next time ai zai san muhimmancin rayuwarsa”

“Wannan duk ba hujja ba ce Ameer, rayuwar mutum tana da muhimmanci”

Cewar Momy tana kallon ďa ďaya tilo Namiji kuma farincikin mijinta.

“Zan kiyaye next time, amman dai hakan ba yana nufin wani banza ya taka ni na kyale shi ba, kuna da damuwa da mutanen da be kamata mu damu da su ba”

Ya tsayar da cin abincin da yake ya sake duba mahaifinsa.

“But Daddy I'm sorry”

Da sauri Mr Bashir ya girgiza masa kai domin ko kadan baya son bacin ran ďan nasa Ameer.

“No No No don't, Daddy loves you so much”

Ameer yayi murmushi ya cigaba da cin abincinsa.

“Daman ai kai baka laifi a gurin Daddy da dai mu ne”

Cewar Teema sai duk suka saka dariya har Daddy, Ameer ya kai fork dinsa ya dauko namanta ya cinye sai ta fara kukan shagwaba, dariya yayi ya mike tsaye tare da daukar kofin lemun dake gaban Daddynsa.

“Momy thank you for the lunch yayi dadi sosai”

“Baka ci komai ba ai ka tashi, ina zaka je?”

“Abokaina ke jirana akwai inda zamu je yanzu nan”

“Take care”

Daddy ya fada masa yana kallonsa, domin ya san ba karamin aikinsa ba ne a kira shi a sanar da shi Ameer yayi wani laifin ko kuma yayi fada da wani ko ya karya wata dokar kasa.

“I will Daddy ba zan janyo maka magana ba”

Daddy yayi murmushi, sallama Ameer yayi musu sannan ya fice daga bangaren.

___________________

Ga wani sabon zubi,
Sabuwar shimfida mai zafi
A sabuwar Shekara.
ku daura Belt dinku domin wannan tafiyar ba mai sauki ba ce.
Haka kuma ba free book ba ne, paid book ne a 300.

Few pages ne muke da su na free, sauran duk na kudi ne.

One page ne kullum da yarda Allah, sai dai bana posting Monday da Friday, saboda wani uzurin, haka kuma idan ban samu yi a ranakun posting ba zan sanar kuma zan ranka page din In Shaa Allah.

Yadda na fara lafiya Allah ya amince min na karasa shi cikin aminci da farinciki, Ameen.

Ina fatar zaku karbe shi hannu hudu ba ma biyu ba. 🥰

If you want to Subscribe pay 300 to

2451879008
Hadiza Abubakar
Zenith Bank

And sent the evidence of payment to 08036126660

Yan Nijar zaku biya ta wannan line +22790165991

Za ku iya samun WANI GARI a Arewabooks @KhadeejaCandy domin pages din can za su dara na nan yawa.

Lastly idan kin san zaki biya domin ki fitar dan Girman Allah da ya hallice ki karki siya, idan kuma kika fitar min hakika kin cutar da ni kuma idan ina da hakki Allah zai saka min domin ba zan yafe ba.

Happy reading 🫶🏻
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*

_Na Khadeeja Candy_

2️⃣

Sai da ta gama rawar sannan ta shiga cikin gidansu ta zarce bandakin da aka hada manyan itace gurin ginashi, ta saka tokar murhu ta goge jikinta tare da bakin gawayi, sai da ta tabbatar jikinta ya yi tass sannan ta dauki ruwan dake cikin kaskon kasa ta zuba tun daga saman gashin kanta har zuwa kafarta, ta saka talkamin danko ta fito bandaki tana daure da gayen ayaba ta shiga dakinta. Wata brown gown ta dauko doguwar rigar da zata tsaya iya guiwar kafafuwanta ta bayyana farare kuma tsala tsala cinyoyinta. A hankali ta yaryarda gashin kanta ya kwanta bayanta, sannan ta fito waje ta nufi wani itacen fulawa ta tsinke fulawar ta laka a kanta.
Daga gurin ta fara ajujuwa tana dariya har ta isa gurin da ruwan saman da aka yi mai kama da bakin kwarya ya kwanta sai ta leka kanta tana kallon kyakkyawar fuskarta, da yadda furen fulawar ya kawata jikaken gashin kanta. Babu madubin duba fuska a kaf fadin garin, idan mace ko namiji suka yi kwalliya ko suka zo ganin fuskokinsu suna zuwa ne a gurin da ruwa ya wanta irin wanda yake aje a guri daya baya motsi su kalli kansu, wasu kuma suna zuba ruwan ne a wani muhalli na dabam su bar shi a ciki a matsayin madubinsu sai kuma ma su amfani da tsafi su ga fuskarsu. Ta cikin ruwan ta yi arba da Eid yana kallonta fuskarsa da murmushi, a take ta juyowa tana murmushi ta kalli saitin inda yake tsaye, babu shi a zahiri domin ya bata a idonta da duk idon dan'adam mai gani, sai dai tana iya ganinsa a cikin ruwan yana kallonta, kyalkyalewa ta yi da dariya mai matukar dadin sauraro da burgewa ta tsallaka ruwan ta mike hanya tana tafiya sai ya mika hannunsa ya kama nata ya tsayar da ita daga tafiyar da yake, wannan karon ta ganshi ido da ido domin ya so ta ganshi din ne, ba a yau ya saba yi mata haka ba, ya boye mata kansa ta yadda sai ya ga dama zata ganshi, ita ma tana daf ta iya duk wani abu da ake da tsafi da zarar ta cika shekara 20, an bata kambun sarautar da aka aje mata tun gabanin haihuwarta.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.