Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 63 of 227

“What's her name again”

Jabir ya tambaya yana kallon idonta dake yawo a kasa. Sai Mahmood ya amsa masa.

“Waira”

“Waira.... What's that mean?”

Ya maimaita sunan tare da tambayar ma'anarsa, Mahmood ya daga kafadunsa.

“Just, but Ummi tace tana tunanin Nuwaira su kuma suke kiransa da Waira kawai”

“Oh okay har yanzu bata jin hausa?”

“Tana ji, and she can speak some, as well as English ana mata Evening lesson and tana zuwa makaranta”

Mahmood ya juya ya kalleta.

“Waira ki cewa Jabir barka da zuwa”

Sai ta dago ta kalli mutumen da Mahmood ya nuna mata, ta maida kanta kasa ba tare da ce masa komai ba.

“Yana ďaya daga cikin dalilin da ya saka na tsani yarinyar nan, sai ta rika abu kamar munafuka, ko kuma bata yarda da mutane ba Mtscheeeeee”

Waira ta kalli Namra wacce ta yi maganar ta sake maida kanta kasa. Mahmood yayi murmushi.

“Bata ga damar magana ba”

“Tau saboda ta ga baki ne ko? Kasan bata taba ganinmu ba sai yau”

Yesmin ta fada tana mika hannu ta karbi ruwan da Hanne take mika mata. Umar ya mike tsaye rike da wayarsa.

“Bari na fara ba cikina hakkinsa tukunna”

Namra suka saka masa dariya daman duk wanda ya san Umar ya san baya wasa da cikinsa ko kadan idan kuma zai ci ba kadan yake ci ba, wannan ya saka ya banbanta da yan'uwansa domin shi yana da jiki sosai kana ganinsa ka ga ďan lukuti ba kamar sauran yan'uwansa dake da kirar zaratan jarumai ba. Kusan lokaci daya Namra da cousin's dinta suka haura sama zuwa dakinta suna hira, Jabir kuma ya tashi tare da Mahmood sai ya rage falon babu kowa sai Waira dake zauna a cushion, da kuma Umar dake bawa cikinsa babban aiki, sai da yayi rabin plate sannan ya juyo ya kalli Waira dake zaune tana taba sarkar zoben dake wuyanta.

“Hey young lady zaki iya sama min wani lemun a fridge bana shan lemu mai kwakwa”

Ta dago sai dai bata juyo ta kalleshi, ta san da ita yake domin babu kowa a falon sai ita, Hanne ta fice tun bayan data mikawa Yesmin ruwa, sai dai hakan be saka ta motsa daga inda take ba balle ta yi alamar dauko masa abun da ya bukata.

“Bata san inda yake ba”

Ya sake juyowa jin wata kalar hausar bambarakwai.

“Ita wa?”

Sai a lokacin ta juya ta kalleshi ta idanuwanta masu matukar kyau da daukar hankali, sai ta nuna kanta.

“Waira... Bata sani ba”

Murmushi yayi mai kama da dariya ya juya ya cigaba da cin abincinsa. Ita kuma ya juyo da kanta tana cigaba da wasa da sarkarta, kusan ita da shi duk baki ne a gidan wata kila ma shi ya fita sakewa ya shiga yayi abun da yake so ita bata yi ba, har yanzu bata taba abu idan ba a Ummi ko wani ya bata umarnin yin haka ba, ta kayyadewa kanta abubuwan da take iya ci ko sha, wannan ya saka idan ka ganta kofar kitchen to Ummi ta kirata ta bata abun da ta sabawa kanta da ci ne, ko kuma ta shiga ta gada ma kanta kamar yadda Ummi ta nuna mata idan bata nan zata iya hadawa kanta tea ko zuba ruwa ta sha, ko kuma ta bude warmer ta zuba dankali ko dafaffen kwai domin bata cin soyayya, sai fruit da zallar madara, ko nama da aka dafa da gishi kawai ba tare da an sanka magi ko yaji ba, sai kuma cake da biscuits ko cookies da ake yi da kayan zaki wannan kan duk tana iya ci ko ta sha. Bayan shi bata da wani abinci da take ci. Wannan ya saka bata katsalanta a harkokin gidan duk kuwa da irin yadda Ummi take son ta saki jikinta da su ba komai ta san muhallinsa a gidan ba, kuma bata taba kokarin cilastawa kanta sani ba, domin komai yi mata ake idan Ummi bata yi mata ba, Mahmood ko Nimra zata su mata balle kuma Hanne da Ummi tace ta rika yi mata komai a gidan, Namra da Maleek kadai mutanen da bata taba shan inuwarsu a gidan ba, idan zata zillo ta fadi babu mai tareta a cikin, Namra dai saboda jin kai da ganin level dinsu ba ďaya ba, Maleek kuma saboda kyamar matan da yake, duk kuwa da kasancewar ya canja sosai ba kamar da yake baya iya zama a gurin da mata suke zaune ba, ko cin abinci tare da kanensa, a yanzu kam ya kan ci ko zama tare da su har ma ya dan tsoma baki idan suna magana amman ban da Waira, komai zata yi ko tace ba zai saka baki ba, duk yadda Ummi zata yi zancen wani abu daya shafeta ba zai ce komai ba, komai take ba zai yi magana ba sai dai ya kalleta.

Ita ma kuma bata taba kokarin son yi masa magana ba, tana kokarim kiyaye iyakarta da shi tun a lokacin da ta fahimci yadda rayuwarsa take, ko a kitchen ta shiga idan ta ga shi ne a ciki fitowa take sai yayi abun da zai yi ya gama sannan ta shiga, Ummi ta sha mata fadan hakan har ta fara gajiya, domin so take shi kanshi Maleek ya dawo kamar kowa, wannan ya saka tun tana cilastawa kanta da yayanta da shi kansa zaman a cikin yana takura har ta fara sabawa yana sakewa, domin kullum addu'a take shi ma kuma be fasa ba, azkar din safiya da yamma basa wuce tun a wacan lokacin da yayi mata alkawari. Haka ma idan zai kwanta zai yi addu'a tare da alwala sannan ya kwanta. Duk wani mataki na neman kariya da kuma mafita na halin da yake ciki Ummi ta bi, kuma tana kan bi, addu'ar da Abiey yace zai saka ayi masa bava fasa ba, an roka masa sauki har gaban Ɗakin Allah, tare da kyautata zaton addu'ar ta fara karbuwa domin kaso 50 na rayuwar da yake a baya ta barshi a yanzu, kyanar matan da yake ya ragu yanzu ba kamar da ba, sai dai har yanzu baya jin wani hauki ko ko burgewa a game da mace, har yanzu bata iya hada jikinsa da mace ko da kuwa Ummi ce balle kuma wata macen dabam da be taba kawowa kansa zai iya son wata mace balle har ta kai ga ya aureta ba, balle kuma ace wata mu'amala ta shiga tsakaninsu idan ma ya tuna da wannan sai ya ji baya bukatar auren gaba daya, ba dan kuma ba shi da lafiya ba, sai dai halittarsa data kasance haka.

Sai da Umar ya gama cin abinci tsab sannan ya tashi ya shiga kitchen ya dauko kalar lemun da yake yana gyatsa ya zuba a cup ya sha sannan ya nufi upstairs. Ana kiran Sallah La'asar suka sauko gaba dayansu a tare, wato Umar da dan'uwansa Jabir sai Maleek dake warware hannun rigarsa Mahmood na gefensa, har suka sauko kowanensu da kalar kamshin turaren da yake, suka fice daga falon Waira bata dago ta kallesu ba, ta mike tsaye ta nufi upstars tana takawa a hankali har ta haye sama ta nufi dakin Ummi ta kwankwasa kamar yadda Ummi ta koya mata ta ja ta tsaya har sai Ummi ta bata umarni shiga sannan ta kai hannunta ta murda kofar ta shiga, suna hada ido da Ummi sai ta nufi Ummi da sauri ta zauna kusa da ita saboda ganin Ummi na kuka.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.