Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 77 of 227

“Nimra wooo what happened?”

Ta dago ta kalleshi tare da kai hannu ta taba fuskarsa.

“Ameer. Abiey, Ummi da Ya Maleek ba za su bari na aureka ba, ba za su bari mu zauna a tare ba, Ameer idan suka ba ni da kai mutuwa zan yi, ni kadai na san yadda nake ji a raina, Ameer guduwa zan yi, mu tafi wani gurin har sai iyayena sun sauka daga fushinsu, zan iya daukar komai amman ban da rabuwa da kai, ina sonka Ameer...”

Lokaci daya aka jefo masa digon tausayinta a ransa, yadda aka yi mata jina jina da jiki kuma har ta baro gidansu a irin wannan yanayin babu mayafi babu talkami hawayen da take zubar kawai sun isa su sosa masa zuciya.

“No Nimra ba zaki aikata haka ba”

“Ba zaman ban za zamu yi idan muka gudu ba Ameer aure zamu yi, mahaifina ba zai saurareni a yanzu ba, kalli yadda Ya Maleek yayi min da jiki”

Ta nuna masa jikinta, duk sai ya ji wani iri domin saboda shi komai ya faru, a kuma manufarsa ta daukar fansa ba dan yana sonta ko son aurenta da gaske ba. Ya saka hannunsa ya daga ta daga kasa ya zaunar da ita kan kujera ya rumgumeta.

“Ba zamu aikata hakan ba Nimra, ni ma da kika ga na gudu saboda Mahaifina ya kore ni da kansa ne, ke kuma mace ce hakan zai iya janyo miki matsala ba ga iyayenki kadai ba”

“Ameer ba ka ce kana kaunata ba? Zaka iya yin komai akaina?”

Yayi shiru kamar mai tunanin amsa mata, ba kansa yake ji ba, ita yake ji idan har ta aikata abun da zuciyarta ta raya mata zata jefa kanta a matsala ne kawai ne.

“Hakan ba yana nufin na sake jefaki a wata matsala a yanzu ba, Nimra I'm ever to fight for you now i can't let your family hurt you again, I'm serious this time”

“I think I'm losing my mind now, please don't let me down Ameer ina matukar kaunarka, dan Allah mu gudu idan mahaifina ya san na sake zuwa gurinka kashe ni zai yi”

Ta saki jikinsa ta mike tsaye jikinta na rawa. Sai yayi saurin mikewa shi ma ya rumgume ta.

“Shikenan zamu gudu, amman yanzu akwai wanda ya san kin zo nan?”

Ta girgiza masa kai alamar aa.

“Amman za su iya zuwa nema na a nan, Abiey zai iya kashe ni idan ya zo ya gan ni a nan”

Ya saketa ya nufi inda ya aje wayarsa ya dauka ya dauki key dinsa ya dauki wayarta ya rika hannunta ya fito da ita da sauri, a motarsa ya saka ta, sannan ya nufi motarta ya kashe ya dawo gurin motarsa ya shiga mazaunin direba ya tashi motar, ana bude masa gate ya fice da gudu, sai da yayi nisa sannan ya faka ya kwantar mata da kujerar motar yana kallon idonta dake rufe fuskarta har ta fara canja kammani. Tunanin inda za su je su boya ya fara yi kamin ya mike hannu ya rike hannunta shi dai ya san har ga Allah baya son ta a zuciyarsa sai dai kuma tausayinta ya cika masa zuciya a yanzu, domin ya fahimci ta gama haukacewa kansa.
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 32

*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

Jin ya faka ya saka ta bude idonta daya domin ďayan ya rike ya rufe a yanzu ya like, tana kallon gurin ta dube shi.

“Me mike yi a nan?”

“Dole zamu zauna mu yi tunani inda zamu tafi mana, kuma kin ga muna bukatar kudi mai yawa da zai wadace mu a iya zaman da zamu yi, and dole mu tsara komai kamin mu tafi, kin ga babu wanda ya san muna zuwa nan balle ya saka mana ido ko a fada cewar an ganki”

Ta fashe da kuka.

“Ban tana tunanin zan iya aikata haka ba Ameer dan Allah karka ci amanata, karka bar ni dan Allah”

Ya saka hannunsa ya rike fuskarta.

“Ni na janyo miki wannan abun Nimra, so i promise you ba zan kyale ki ki sake aikata kuskure ba, kuma ba zan kyale ki sha wahala ke kadai ba”

Ya sumbanci hannunta, tun da yake a rayuwarsa be taba jin tausayin wani mutum lokaci daya kamar yadda ya ji tausayinta a yanzu ba. Yarda da ta yi da shi ya saka ta amince da kalamansa har ya bude motar ya fita ya zagaya side dinta ya bude mota ta sauko sai yayi mata side hug domin bata iya tsayuwa da kyau kuma ba zai yiyu ya dauke ta a public guri kamar wannan ba, haka ya shiga da ita a gurin ya nufi gurin da suka saba zama ya zaunar da ita sannan ya koma ya dauko wayarsa da tata wayar ya dawo ya zauna, yana kallonta sai ta miko hannunta ta rika hannunta. Humairah dake gefe tana kula da wasu wata abokiyar aikinta ta tabo ta ta nuna mata shigowarsu domin kowa a gurin ya san Humaira ce kadai take kula da su idan sun zo gurin. Sai da ta gama da wandanda suke serving sannan ta nufo gurin da Ameer yake zaune tana rare wakar da ta tanadar musu. Kusan a yanzu ya haddace wakar dan haka tana fara rerawa sai ya tayata suka kare wakar a tare.

“Idan ka biye ta kan saurayi, sai ya kai ka ya baro, samarin yanzu yan shan minti ne, yar'uwa ki yi hankali 🎶 Duniya budurwar wawa yarinya ki yi hattara... 🎶 iyeee yaraye nanaye Humaira.... 🎶”

“Na haddace wannan wakar sai wace kuma?”

Ya tambaya a tsawa yana kallonta sai ta daga kafadunta tana kallonsa ita ma.

“Wakata ce kawai”

“Nice song”

“Thank You”

Ganin kamar tana kokarin raina masa da wayo ya saka ya daki teburin gabansa da karfi, har sai da ta zabura.

“Don't you ever singing that song again”

Ta hade yawu tana sauke ajiyar zuciya domin ta lura ba da wasa yake ba.

“Me za a kawo muku?”

“Ba ma bukata go back to your work”

Ta juya ta fice daga gurin tana ta mamakin dukan data gani a jikin budurwarsa yau, fada suka yi yayi mata wannan dukan ko kuma dai wani ne yayi mata, idan har wani yayi mata zata fi kowa jindadin musamman ace iyayenta ne sun san halin da take ciki, domin dai alakar dake tsakanin yarinyar da Ameer ya isheta sai ka ce a kanta suke zaune.

“Dear shiga ki wanke fuskarki a restroom i will make a phone call na yi mana booking flight”

Ta daga masa kai ta fara kokarin mikewa tsaye ta kasa sai Ameer yayi kiran Humairah da hannu, ta zo gurin daman idonta yana kansu, ya nuna mata Nimra.

“Taimaka mata ta shiga bandaki”

Humaira ta kalli Nimra tsab sai kuma ta kalleshi da alamar tuhuma, da ido yayi mata alama da lafiya? Bata ce komai ba ta rikata Nimra ta mike tsaye suka nufi hanyar shiga bandakin. Sai da suka wuce sannan Ameer ya ďauki wayar Nimra dake aje a gabansa saman teburin da suke zaune ya bude security wayar, domin ya dade ta sanin password din ya shiga calls dinta ya duba number da yake kyautata zaton ta mahaifiyarta saboda an yi saving dinta da My Lovely Ummie and saka heart emoji da rose flower, number ya kwashe ya saka a wayarsa da danna kira. Sai da ya kira kira har sau uku ba a daga ba ya sake gwadawa ana biyar aka yi picking.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.